< Ibraniyawa 3 >
1 Saboda haka,’yan’uwa tsarkaka, waɗanda suke da rabo a kiran nan na sama, ku kafa tunaninku a kan Yesu, manzo da kuma babban firist wanda muke shaidawa.
Therefore, holy brothers, you share in a heavenly calling. Think about Jesus, the apostle and high priest of our confession.
2 Ya yi aminci ga wanda ya naɗa shi, kamar yadda Musa ya yi aminci ga dukan gidan Allah.
He was faithful to God, who appointed him, just as Moses was also faithful in God's house.
3 An ga Yesu ya cancanci girma fiye da Musa, kamar yadda mai ginin gida ya fi gidan daraja.
For Jesus has been considered worthy of greater glory than Moses, because the one who builds a house has more honor than the house itself.
4 Gama kowane gida yana da wanda ya gina shi, amma maginin dukan abu Allah ne.
For every house is built by someone, but the one who built everything is God.
5 Musa ya yi aminci a matsayin bawa cikin dukan gidan Allah, yana ba da shaida a kan abubuwan da za a faɗa nan gaba.
For Moses was faithful as a servant in God's entire house, bearing witness about the things that were to be spoken of in the future.
6 Amma Kiristi mai aminci ne kamar ɗa a gidan Allah. Mu kuwa gidansa ne, in muka tsaya gabanmu gadi da kuma begen da muke taƙama a kai.
But Christ is faithful as a Son who is in charge of God's house. We are his house if we hold fast to our courage and the hope of which we boast.
7 Kamar dai yadda Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Yau, in kuka ji muryarsa,
Therefore, it is just as the Holy Spirit says: “Today, if you hear his voice
8 kada ku taurare zukatanku, yadda kuka yi a tawayen nan, a lokacin gwaji a hamada,
do not harden your hearts as in the rebellion, in the time of testing in the wilderness.
9 inda kakanninku suka gwada ni, suka kuma gwada ni, ko da yake a cikin shekaru arba’in sun ga abin da na yi.
This was when your ancestors rebelled by testing me, and when, during forty years, they saw my deeds.
10 Shi ya sa na yi fushi da wancan zamani, na kuma ce, ‘Kullum zukatansu a karkace suke, ba su kuma san hanyoyina ba.’
Therefore I was displeased with that generation. I said, 'They have always gone astray in their hearts. They have not known my ways.'
11 Saboda haka na yi rantsuwa a cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”
It is just as I swore in my anger: 'They will never enter my rest.'”
12 Ku lura fa,’yan’uwa, cewa kada waninku yă kasance da zuciya mai zunubi marar bangaskiya da takan juye daga bin Allah mai rai.
Be careful, brothers, so that among you there will not be anyone with an evil heart of unbelief, a heart that turns away from the living God.
13 Sai dai ku ƙarfafa juna kullum, muddin akwai lokacin da ana ce da shi Yau, don kada waninku yă zama mai taurin zuciya ta wurin ruɗun zunubi.
Instead, encourage one another daily, as long as it is called “today,” so that no one among you will be hardened by the deceitfulness of sin.
14 Mu masu tarayya ne da Kiristi idan mun riƙe bangaskiyarmu da ƙarfi daga farko har zuwa ƙarshe.
For we have become partners of Christ if we firmly hold to our confidence in him from the beginning to the end.
15 Kamar yadda aka faɗa cewa, “Yau, in kuka ji muryarsa, kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a tawayen nan.”
About this it has been said, “Today, if you hear his voice, do not harden your hearts, as in the rebellion.”
16 Su wane ne suka ji suka kuma yi tawaye? Ba su ne duk waɗanda Musa ya bi da su daga Masar ba?
Who was it who heard God and rebelled? Was it not all those who came out of Egypt through Moses?
17 Da su wane ne kuwa ya yi fushi har shekaru arba’in? Ba da waɗanda suka yi zunubi, waɗanda suka mutu a hamada ba?
With whom was he angry for forty years? Was it not with those who sinned, whose dead bodies fell in the wilderness?
18 Kuma ga su wane ne Allah ya rantse cewa ba za su taɓa shiga hutunsa ba, in ba ga marasa biyayyan nan ba?
To whom did he swear that they would not enter his rest, if it was not to those who disobeyed him?
19 Saboda haka mun ga cewa ba su iya shiga ba, saboda rashin bangaskiyarsu ne.
We see that they were not able to enter his rest because of unbelief.