< Ibraniyawa 3 >
1 Saboda haka,’yan’uwa tsarkaka, waɗanda suke da rabo a kiran nan na sama, ku kafa tunaninku a kan Yesu, manzo da kuma babban firist wanda muke shaidawa.
Wherefore, holy brethren, partakers of a heavenly calling, consider the apostle and high-priest of our profession, Jesus;
2 Ya yi aminci ga wanda ya naɗa shi, kamar yadda Musa ya yi aminci ga dukan gidan Allah.
who was faithful to him that appointed him, as also was Moses in all his house.
3 An ga Yesu ya cancanci girma fiye da Musa, kamar yadda mai ginin gida ya fi gidan daraja.
For he hath been counted worthy of more glory than Moses, inasmuch as greater than the house is he who built it.
4 Gama kowane gida yana da wanda ya gina shi, amma maginin dukan abu Allah ne.
For every house is builded by some one; but he who built all things is God.
5 Musa ya yi aminci a matsayin bawa cikin dukan gidan Allah, yana ba da shaida a kan abubuwan da za a faɗa nan gaba.
And Moses indeed was faithful in all his house as a servant, that he might testify of those things which were to be spoken;
6 Amma Kiristi mai aminci ne kamar ɗa a gidan Allah. Mu kuwa gidansa ne, in muka tsaya gabanmu gadi da kuma begen da muke taƙama a kai.
but Christ as a son over his house; whose house are we, if we hold fast the confidence and joyousness of our hope.
7 Kamar dai yadda Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Yau, in kuka ji muryarsa,
Wherefore, as the Holy Spirit saith: “To-day, if ye hear his voice,
8 kada ku taurare zukatanku, yadda kuka yi a tawayen nan, a lokacin gwaji a hamada,
harden not your hearts, as in the provocation, in the day of the temptation in the wilderness,
9 inda kakanninku suka gwada ni, suka kuma gwada ni, ko da yake a cikin shekaru arba’in sun ga abin da na yi.
where your fathers tempted me by proving me, and saw my works forty years.
10 Shi ya sa na yi fushi da wancan zamani, na kuma ce, ‘Kullum zukatansu a karkace suke, ba su kuma san hanyoyina ba.’
Wherefore I was offended with that generation, and said, They always err in their heart, but they knew not my ways;
11 Saboda haka na yi rantsuwa a cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”
so I swore in my wrath, They shall not enter into my rest.”
12 Ku lura fa,’yan’uwa, cewa kada waninku yă kasance da zuciya mai zunubi marar bangaskiya da takan juye daga bin Allah mai rai.
Take heed, brethren, lest there be in any one of you an evil heart of unbelief, in departing from the living God.
13 Sai dai ku ƙarfafa juna kullum, muddin akwai lokacin da ana ce da shi Yau, don kada waninku yă zama mai taurin zuciya ta wurin ruɗun zunubi.
But exhort one another daily, as long as it is called To-day, that none of you may be hardened through the deceitfulness of sin.
14 Mu masu tarayya ne da Kiristi idan mun riƙe bangaskiyarmu da ƙarfi daga farko har zuwa ƙarshe.
For we have become partakers of Christ, if we hold fast our first confidence firm to the end.
15 Kamar yadda aka faɗa cewa, “Yau, in kuka ji muryarsa, kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a tawayen nan.”
When it is said, “To-day, if ye hear his voice, harden not your hearts, as in the provocation,”
16 Su wane ne suka ji suka kuma yi tawaye? Ba su ne duk waɗanda Musa ya bi da su daga Masar ba?
who then, when they had heard, provoked? Was it not all who came out of Egypt by means of Moses?
17 Da su wane ne kuwa ya yi fushi har shekaru arba’in? Ba da waɗanda suka yi zunubi, waɗanda suka mutu a hamada ba?
And with whom was he offended forty years? Was it not with those who sinned, whose carcasses fell in the wilderness?
18 Kuma ga su wane ne Allah ya rantse cewa ba za su taɓa shiga hutunsa ba, in ba ga marasa biyayyan nan ba?
And to whom did he swear that they should not enter into his rest, except to those who were disobedient?
19 Saboda haka mun ga cewa ba su iya shiga ba, saboda rashin bangaskiyarsu ne.
So then we see that they could not enter in because of unbelief.