< Ibraniyawa 3 >
1 Saboda haka,’yan’uwa tsarkaka, waɗanda suke da rabo a kiran nan na sama, ku kafa tunaninku a kan Yesu, manzo da kuma babban firist wanda muke shaidawa.
Wherefore, holy brethren, partakers of the heavenly calling, attentively consider Jesus, the Apostle and High Priest whom we have confessed;
2 Ya yi aminci ga wanda ya naɗa shi, kamar yadda Musa ya yi aminci ga dukan gidan Allah.
who, as well as Moses, is faithful to him that appointed him over all his house.
3 An ga Yesu ya cancanci girma fiye da Musa, kamar yadda mai ginin gida ya fi gidan daraja.
Indeed, he has been accounted worthy of glory, as far superior to Moses, as that of the builder is superior to the house.
4 Gama kowane gida yana da wanda ya gina shi, amma maginin dukan abu Allah ne.
Now every house is built by some one; but he, the builder of all things, is God.
5 Musa ya yi aminci a matsayin bawa cikin dukan gidan Allah, yana ba da shaida a kan abubuwan da za a faɗa nan gaba.
And Moses, indeed, as a servant, was faithful in all his house, for a testimony of the things that were to be spoken by him;
6 Amma Kiristi mai aminci ne kamar ɗa a gidan Allah. Mu kuwa gidansa ne, in muka tsaya gabanmu gadi da kuma begen da muke taƙama a kai.
but Christ, as a Son, over his own house--whose house we are, if we hold fast our confidence, and the rejoicing of our hope, unshaken to the end.
7 Kamar dai yadda Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Yau, in kuka ji muryarsa,
Wherefore, as the Holy Spirit says, "To-day, if you will hear his voice,
8 kada ku taurare zukatanku, yadda kuka yi a tawayen nan, a lokacin gwaji a hamada,
harden not your hearts, as in the bitter provocation, in the day of temptation in the wilderness;
9 inda kakanninku suka gwada ni, suka kuma gwada ni, ko da yake a cikin shekaru arba’in sun ga abin da na yi.
where your fathers tempted me, and proved me, yet saw my works for forty years.
10 Shi ya sa na yi fushi da wancan zamani, na kuma ce, ‘Kullum zukatansu a karkace suke, ba su kuma san hanyoyina ba.’
Wherefore, I was displeased with that generation, and said, They always err in heart, and they have not known my ways.
11 Saboda haka na yi rantsuwa a cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”
So, I swore, in my wrath, They shall not enter into my rest."
12 Ku lura fa,’yan’uwa, cewa kada waninku yă kasance da zuciya mai zunubi marar bangaskiya da takan juye daga bin Allah mai rai.
Brethren, take heed, lest there be in any of you an evil heart of unbelief, by departing from the living God.
13 Sai dai ku ƙarfafa juna kullum, muddin akwai lokacin da ana ce da shi Yau, don kada waninku yă zama mai taurin zuciya ta wurin ruɗun zunubi.
But, lest any of you be hardened, through the deceitfulness of sin, exhort one another every day, while it is called To-day:
14 Mu masu tarayya ne da Kiristi idan mun riƙe bangaskiyarmu da ƙarfi daga farko har zuwa ƙarshe.
(for we are all partakers of Christ, if, indeed, we hold fast this first confidence firm to the end; )
15 Kamar yadda aka faɗa cewa, “Yau, in kuka ji muryarsa, kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a tawayen nan.”
with this saying, "To-day, if you will hear his voice, harden not your hearts, as in the bitter provocation."
16 Su wane ne suka ji suka kuma yi tawaye? Ba su ne duk waɗanda Musa ya bi da su daga Masar ba?
For some, when they heard, did bitterly provoke; yet, not all that came out of Egypt by Moses.
17 Da su wane ne kuwa ya yi fushi har shekaru arba’in? Ba da waɗanda suka yi zunubi, waɗanda suka mutu a hamada ba?
Was it not with them who sinned, whose carcasses fell in the wilderness?
18 Kuma ga su wane ne Allah ya rantse cewa ba za su taɓa shiga hutunsa ba, in ba ga marasa biyayyan nan ba?
And to whom did he swear, that they should not enter into his rest, but to them who did not believe?
19 Saboda haka mun ga cewa ba su iya shiga ba, saboda rashin bangaskiyarsu ne.
So, we see that they could not enter in because of unbelief.