< Ibraniyawa 3 >
1 Saboda haka,’yan’uwa tsarkaka, waɗanda suke da rabo a kiran nan na sama, ku kafa tunaninku a kan Yesu, manzo da kuma babban firist wanda muke shaidawa.
Because of which, holy brothers, companions of a heavenly calling, consider the Apostle and High Priest of our affirmation, Jesus Christ,
2 Ya yi aminci ga wanda ya naɗa shi, kamar yadda Musa ya yi aminci ga dukan gidan Allah.
who was faithful to him who appointed him, as also was Moses in all his house.
3 An ga Yesu ya cancanci girma fiye da Musa, kamar yadda mai ginin gida ya fi gidan daraja.
For this man was considered worthy of more glory than Moses, by so much as he who built it has more esteem than the house.
4 Gama kowane gida yana da wanda ya gina shi, amma maginin dukan abu Allah ne.
For every house is built by some man, but he who built all things is God.
5 Musa ya yi aminci a matsayin bawa cikin dukan gidan Allah, yana ba da shaida a kan abubuwan da za a faɗa nan gaba.
And Moses was indeed faithful in all his house as a servant, for a testimony of the things that were going to be spoken,
6 Amma Kiristi mai aminci ne kamar ɗa a gidan Allah. Mu kuwa gidansa ne, in muka tsaya gabanmu gadi da kuma begen da muke taƙama a kai.
but Christ as a Son over his house, whose house we are, if only we keep in possession our confidence and pride of hope, firm until the end.
7 Kamar dai yadda Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Yau, in kuka ji muryarsa,
Therefore, as the Holy Spirit says, Today if ye hear his voice,
8 kada ku taurare zukatanku, yadda kuka yi a tawayen nan, a lokacin gwaji a hamada,
do not harden your hearts as in the rebellion, according to the day of the trial in the wilderness,
9 inda kakanninku suka gwada ni, suka kuma gwada ni, ko da yake a cikin shekaru arba’in sun ga abin da na yi.
where your fathers challenged me, tested me, and saw my works forty years.
10 Shi ya sa na yi fushi da wancan zamani, na kuma ce, ‘Kullum zukatansu a karkace suke, ba su kuma san hanyoyina ba.’
Therefore I was angry with that generation, and said, They are always led astray in their heart, and they did not know my ways.
11 Saboda haka na yi rantsuwa a cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”
So I swore in my wrath, They will not enter into my rest.
12 Ku lura fa,’yan’uwa, cewa kada waninku yă kasance da zuciya mai zunubi marar bangaskiya da takan juye daga bin Allah mai rai.
Watch, brothers, lest there will be in any of you an evil heart of unbelief in withdrawing from the living God.
13 Sai dai ku ƙarfafa juna kullum, muddin akwai lokacin da ana ce da shi Yau, don kada waninku yă zama mai taurin zuciya ta wurin ruɗun zunubi.
But exhort each other during each day, while it is called Today, lest any of you may be hardened by the deceitfulness of sin.
14 Mu masu tarayya ne da Kiristi idan mun riƙe bangaskiyarmu da ƙarfi daga farko har zuwa ƙarshe.
For we have become companions of the Christ, if only we keep in possession the primacy of the essence, steadfast until the end,
15 Kamar yadda aka faɗa cewa, “Yau, in kuka ji muryarsa, kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a tawayen nan.”
while it is said, Today if ye will hear his voice, do not harden your hearts as in the rebellion.
16 Su wane ne suka ji suka kuma yi tawaye? Ba su ne duk waɗanda Musa ya bi da su daga Masar ba?
For some who heard rebelled, but not all those who came out of Egypt by Moses.
17 Da su wane ne kuwa ya yi fushi har shekaru arba’in? Ba da waɗanda suka yi zunubi, waɗanda suka mutu a hamada ba?
But with whom was he angry forty years? Was it not with those who sinned, whose carcasses fell in the wilderness?
18 Kuma ga su wane ne Allah ya rantse cewa ba za su taɓa shiga hutunsa ba, in ba ga marasa biyayyan nan ba?
And to whom did he swear were not going to enter into his rest, if not to those who were disobedient?
19 Saboda haka mun ga cewa ba su iya shiga ba, saboda rashin bangaskiyarsu ne.
And we see that they were not able to enter in because of unbelief.