< Ibraniyawa 2 >
1 Dole mu ƙara mai da hankali sosai ga abubuwan da muka ji, don kada mu kauce.
For this cause, it behoveth us, with unwonted firmness, to be holding fast unto the things that have been heard, lest, at any time, we drift away.
2 Gama in saƙon da aka faɗi ta bakin mala’iku ya zama tabbatacce, kuma kowane ƙeta umarni da rashin biyayya suka karɓi sakamakonsu da ya dace,
For, if the word through messengers spoken became firm, and, every transgression and disobedience received a just recompense,
3 yaya za mu tsira in muka ƙyale irin wannan babban ceto? Wannan ceto, wanda Ubangiji ne ya fara sanar, aka kuma tabbatar mana ta bakin waɗanda suka ji shi.
how shall, we, escape, if, so great a salvation as this, we have neglected, —which, indeed, having received, a beginning, of being spoken through the Lord, by them who heard, unto us was confirmed,
4 Allah shi ma ya shaida ta wurin alamu, abubuwan banmamaki da mu’ujizai iri-iri, da kuma baye-bayen Ruhu Mai Tsarki da aka rarraba bisa ga nufinsa.
God, jointly witnessing also, both with signs and wonders and manifold mighty works, and with distributions of Holy Spirit, according to his own will?
5 Ba ga mala’iku ba ne ya sa su yi mulkin duniya mai zuwa, wanda muke magana a kai ba.
For, not unto messengers, hath he subjected the coming habitable earth of which we are speaking;
6 Amma akwai wani wurin da wani ya shaida cewa, “Mene ne mutum, da kake tuna da shi, ɗan mutum da kake kula da shi?
But one somewhere hath borne witness, saying—What is man, that thou shouldst make mention of him? Or the son of man, that thou shouldst put him in charge?
7 Ka sa shi ƙasa kaɗan da darajar mala’iku; ka naɗa shi da ɗaukaka da girma,
Thou hast made him less, some little, than messengers, With glory and honour, hast thou crowned him, —[And hast set him over the works of thy hands];
8 ka kuma sa kome a ƙarƙashin ƙafafunsa.” Ta wurin sa kome a ƙarƙashinsa, Allah bai bar wani abu da bai sa a ƙarƙashinsa ba. Duk da haka a yanzu ba mu ga kowane abu a ƙarƙashinsa ba.
All things, hast thou subjected beneath his feet. For, in subjecting, [to him] the all things, nothing, left he, to him unsubjected; But now, not yet, do we see, to him, the all things subjected; —
9 Sai dai muna ganin Yesu, wanda aka mai da shi ƙasa kaɗan da darajar mala’iku, yanzu kuwa an naɗa shi da ɗaukaka da girma domin yă sha wahalar mutuwa, domin ta wurin alherin Allah yă ɗanɗana mutuwa saboda kowa.
But, Jesus, made some little less than messengers, we do behold: by reason of the suffering of death, crowned with glory and honour, to the end that, by favour of God, in behalf of every one, he might taste of death.
10 Ta wurin kawo’ya’ya masu yawa zuwa ga ɗaukaka, ya dace cewa Allah, wanda dominsa da kuma ta wurinsa ne kome yake kasancewa, ya sa tushen cetonsu yă zama cikakke ta wurin shan wahala.
For it was becoming in him—For the sake of whom are the all things, and by means of whom are the all things, —when, many sons, unto glory, he would lead, The Princely Leader of their salvation, through sufferings, to make perfect.
11 Da shi wanda yake tsarkake mutane da kuma su waɗanda ake tsarkakewa duk’yan iyali ɗaya ne. Saboda haka Yesu ba ya kunyan kiransu’yan’uwansa.
For, both he that maketh holy, and they who are being made holy, are, all, of One; For which cause, he is not ashamed to be calling them, brethren,
12 Ya ce, “Zan sanar da sunanka ga’yan’uwana; a gaban jama’a zan rera yabonka.”
saying—I will declare thy name unto my brethren, in the midst of an assembly, will I sing praise unto thee;
13 Har wa yau ya ce, “Zan dogara gare shi.” Ya kuma ce, “Ga ni, da’ya’yan da Allah ya ba ni.”
and again—I, will be confident upon him; and again—Lo! I, and the children which, unto me, God, hath given.
14 Da yake’ya’yan suna da nama da jini, shi ma sai ya ɗauki kamanninsu na mutum domin ta wurin mutuwarsa yă hallaka wanda yake riƙe da ikon mutuwa, wato, Iblis
Seeing therefore the children have received a fellowship of blood and flesh, he also, in like manner, took partnership in the same, —in order that, through death, —he might paralyse him that held the dominion of death, that is, the Adversary, —
15 ya kuma’yantar da waɗanda dukan rayuwarsu tsoron mutuwa ya riƙe su cikin bauta.
And might release these—as many as, by fear of death, were all their lifetime liable, to bondage.
16 Gama tabbatacce ba mala’iku ne ya taimaka ba, sai dai zuriyar Ibrahim.
For, not surely of messengers, is he laying hold, but, of Abraham’s seed, he is laying hold.
17 Saboda wannan dole a mai da shi kamar’yan’uwansa ta kowace hanya, domin yă zama babban firist mai aminci da mai jinƙai cikin hidima ga Allah, yă kuma miƙa hadayar sulhu saboda zunuban mutane.
Whence he was obliged, in every way, unto the brethren, to be made like, that he might become a merciful and faithful high-priest, in the things pertaining unto God, —for the making of propitiation for the sins of the people.
18 Domin shi kansa ya sha wahala sa’ad da aka gwada shi, yana iya taimakon waɗanda ake yi wa gwaji.
For, in that, he, suffered when tested, he is able, unto them who are being tested, to give succour.