< Ibraniyawa 2 >

1 Dole mu ƙara mai da hankali sosai ga abubuwan da muka ji, don kada mu kauce.
Therefore we ought to give the more earnest heed to the things that were heard, lest haply we drift away [from them].
2 Gama in saƙon da aka faɗi ta bakin mala’iku ya zama tabbatacce, kuma kowane ƙeta umarni da rashin biyayya suka karɓi sakamakonsu da ya dace,
For if the word spoken through angels proved stedfast, and every transgression and disobedience received a just recompense of reward;
3 yaya za mu tsira in muka ƙyale irin wannan babban ceto? Wannan ceto, wanda Ubangiji ne ya fara sanar, aka kuma tabbatar mana ta bakin waɗanda suka ji shi.
how shall we escape, if we neglect so great salvation? which having at the first been spoken through the Lord, was confirmed unto us by them that heard;
4 Allah shi ma ya shaida ta wurin alamu, abubuwan banmamaki da mu’ujizai iri-iri, da kuma baye-bayen Ruhu Mai Tsarki da aka rarraba bisa ga nufinsa.
God also bearing witness with them, both by signs and wonders, and by manifold powers, and by gifts of the Holy Ghost, according to his own will.
5 Ba ga mala’iku ba ne ya sa su yi mulkin duniya mai zuwa, wanda muke magana a kai ba.
For not unto angels did he subject the world to come, whereof we speak.
6 Amma akwai wani wurin da wani ya shaida cewa, “Mene ne mutum, da kake tuna da shi, ɗan mutum da kake kula da shi?
But one hath somewhere testified, saying, What is man, that thou art mindful of him? Or the son of man, that thou visitest him?
7 Ka sa shi ƙasa kaɗan da darajar mala’iku; ka naɗa shi da ɗaukaka da girma,
Thou madest him a little lower than the angels; Thou crownedst him with glory and honour, And didst set him over the works of thy hands:
8 ka kuma sa kome a ƙarƙashin ƙafafunsa.” Ta wurin sa kome a ƙarƙashinsa, Allah bai bar wani abu da bai sa a ƙarƙashinsa ba. Duk da haka a yanzu ba mu ga kowane abu a ƙarƙashinsa ba.
Thou didst put all things in subjection under his feet. For in that he subjected all things unto him, he left nothing that is not subject to him. But now we see not yet all things subjected to him.
9 Sai dai muna ganin Yesu, wanda aka mai da shi ƙasa kaɗan da darajar mala’iku, yanzu kuwa an naɗa shi da ɗaukaka da girma domin yă sha wahalar mutuwa, domin ta wurin alherin Allah yă ɗanɗana mutuwa saboda kowa.
But we behold him who hath been made a little lower than the angels, [even] Jesus, because of the suffering of death crowned with glory and honour, that by the grace of God he should taste death for every [man].
10 Ta wurin kawo’ya’ya masu yawa zuwa ga ɗaukaka, ya dace cewa Allah, wanda dominsa da kuma ta wurinsa ne kome yake kasancewa, ya sa tushen cetonsu yă zama cikakke ta wurin shan wahala.
For it became him, for whom are all things, and through whom are all things, in bringing many sons unto glory, to make the author of their salvation perfect through sufferings.
11 Da shi wanda yake tsarkake mutane da kuma su waɗanda ake tsarkakewa duk’yan iyali ɗaya ne. Saboda haka Yesu ba ya kunyan kiransu’yan’uwansa.
For both he that sanctifieth and they that are sanctified are all of one: for which cause he is not ashamed to call them brethren,
12 Ya ce, “Zan sanar da sunanka ga’yan’uwana; a gaban jama’a zan rera yabonka.”
saying, I will declare thy name unto my brethren, In the midst of the congregation will I sing thy praise.
13 Har wa yau ya ce, “Zan dogara gare shi.” Ya kuma ce, “Ga ni, da’ya’yan da Allah ya ba ni.”
And again, I will put my trust in him. And again, Behold, I and the children which God hath given me.
14 Da yake’ya’yan suna da nama da jini, shi ma sai ya ɗauki kamanninsu na mutum domin ta wurin mutuwarsa yă hallaka wanda yake riƙe da ikon mutuwa, wato, Iblis
Since then the children are sharers in flesh and blood, he also himself in like manner partook of the same; that through death he might bring to nought him that had the power of death, that is, the devil;
15 ya kuma’yantar da waɗanda dukan rayuwarsu tsoron mutuwa ya riƙe su cikin bauta.
and might deliver all them who through fear of death were all their lifetime subject to bondage.
16 Gama tabbatacce ba mala’iku ne ya taimaka ba, sai dai zuriyar Ibrahim.
For verily not of angels doth he take hold, but he taketh hold of the seed of Abraham.
17 Saboda wannan dole a mai da shi kamar’yan’uwansa ta kowace hanya, domin yă zama babban firist mai aminci da mai jinƙai cikin hidima ga Allah, yă kuma miƙa hadayar sulhu saboda zunuban mutane.
Wherefore it behoved him in all things to be made like unto his brethren, that he might be a merciful and faithful high priest in things pertaining to God, to make propitiation for the sins of the people.
18 Domin shi kansa ya sha wahala sa’ad da aka gwada shi, yana iya taimakon waɗanda ake yi wa gwaji.
For in that he himself hath suffered being tempted, he is able to succour them that are tempted.

< Ibraniyawa 2 >