< Ibraniyawa 2 >
1 Dole mu ƙara mai da hankali sosai ga abubuwan da muka ji, don kada mu kauce.
(On this account, we ought to attend the more earnestly to the things which were heard; lest at any time we should left them slip.
2 Gama in saƙon da aka faɗi ta bakin mala’iku ya zama tabbatacce, kuma kowane ƙeta umarni da rashin biyayya suka karɓi sakamakonsu da ya dace,
For if the word spoken by angels was firm, and every transgression and disobedience received a just retribution;
3 yaya za mu tsira in muka ƙyale irin wannan babban ceto? Wannan ceto, wanda Ubangiji ne ya fara sanar, aka kuma tabbatar mana ta bakin waɗanda suka ji shi.
how shall we escape if we neglect so great salvation? which, beginning to be spoken by the Lord, was confirmed to us by them who heard him;
4 Allah shi ma ya shaida ta wurin alamu, abubuwan banmamaki da mu’ujizai iri-iri, da kuma baye-bayen Ruhu Mai Tsarki da aka rarraba bisa ga nufinsa.
God, also, bearing witness, both by signs and wonders, and divers miracles, and distributions of the Holy Spirit, according to his own pleasure.)
5 Ba ga mala’iku ba ne ya sa su yi mulkin duniya mai zuwa, wanda muke magana a kai ba.
Moreover, he has not subjected to the angels the world to come, of which we are speaking.
6 Amma akwai wani wurin da wani ya shaida cewa, “Mene ne mutum, da kake tuna da shi, ɗan mutum da kake kula da shi?
But one in a certain place has testified, saying, "What is man that thou art mindful of him--or the son of man, that thou dost regard him?
7 Ka sa shi ƙasa kaɗan da darajar mala’iku; ka naɗa shi da ɗaukaka da girma,
Thou hast made him a little lower than the angels; thou hast crowned him with glory and honor,
8 ka kuma sa kome a ƙarƙashin ƙafafunsa.” Ta wurin sa kome a ƙarƙashinsa, Allah bai bar wani abu da bai sa a ƙarƙashinsa ba. Duk da haka a yanzu ba mu ga kowane abu a ƙarƙashinsa ba.
thou hast put all things under his feet." Now, by putting all things in subjection to him, he left nothing that is not subject to him; but now, we do not yet see all things subjected to him;
9 Sai dai muna ganin Yesu, wanda aka mai da shi ƙasa kaɗan da darajar mala’iku, yanzu kuwa an naɗa shi da ɗaukaka da girma domin yă sha wahalar mutuwa, domin ta wurin alherin Allah yă ɗanɗana mutuwa saboda kowa.
but we see Jesus, who was made a little lower than the angels, that he, by the favor of God, might taste death for all; for the suffering of death, crowned with glory and honor!
10 Ta wurin kawo’ya’ya masu yawa zuwa ga ɗaukaka, ya dace cewa Allah, wanda dominsa da kuma ta wurinsa ne kome yake kasancewa, ya sa tushen cetonsu yă zama cikakke ta wurin shan wahala.
For it became him, for whom are all things, and by whom are all things, to make him, who leads many sons to glory--even the Captain of their Salvation--perfect through sufferings.
11 Da shi wanda yake tsarkake mutane da kuma su waɗanda ake tsarkakewa duk’yan iyali ɗaya ne. Saboda haka Yesu ba ya kunyan kiransu’yan’uwansa.
For both he who sanctifies, and they who are sanctified, are all of one Father; for which cause he is not ashamed to call them brethren;
12 Ya ce, “Zan sanar da sunanka ga’yan’uwana; a gaban jama’a zan rera yabonka.”
saying, "I will announce thy name to my brethren: in the midst of the congregation I will sing praises to thee."
13 Har wa yau ya ce, “Zan dogara gare shi.” Ya kuma ce, “Ga ni, da’ya’yan da Allah ya ba ni.”
And, again, "I will put my trust in him." And again, "Behold I, and the children whom God has given me."
14 Da yake’ya’yan suna da nama da jini, shi ma sai ya ɗauki kamanninsu na mutum domin ta wurin mutuwarsa yă hallaka wanda yake riƙe da ikon mutuwa, wato, Iblis
Since, then, the children partook of flesh and blood; he, also, in like manner, partook of these; that, through death, he might vanquish him who had the power of death, that is, the devil;
15 ya kuma’yantar da waɗanda dukan rayuwarsu tsoron mutuwa ya riƙe su cikin bauta.
and deliver them, who, through fear of death, were all their lifetime subject to bondage.
16 Gama tabbatacce ba mala’iku ne ya taimaka ba, sai dai zuriyar Ibrahim.
For, indeed, he has not at all assumed the nature of angels; but he has assumed the seed of Abraham.
17 Saboda wannan dole a mai da shi kamar’yan’uwansa ta kowace hanya, domin yă zama babban firist mai aminci da mai jinƙai cikin hidima ga Allah, yă kuma miƙa hadayar sulhu saboda zunuban mutane.
Hence, it was necessary for him to be made like his brethren in all things; that he might be a merciful and faithful High Priest, in matters pertaining to God, in order to expiate the sins of the people;
18 Domin shi kansa ya sha wahala sa’ad da aka gwada shi, yana iya taimakon waɗanda ake yi wa gwaji.
for, by what he suffered himself, when tried; he is able to succor them who are tried.