< Ibraniyawa 13 >

1 Ku ci gaba da ƙaunar juna kamar’yan’uwa.
Semoga kasih kita terhadap satu sama lain sebagai saudara dan saudari terus berlanjut!
2 Kada ku manta da yin alheri ga baƙi, gama ta yin haka ne waɗansu suka yi wa mala’iku hidima, ba da saninsu ba.
Jangan lupa juga untuk menunjukkan kasih kepada orang asing, karena dengan melakukan itu sebagian kita sudah menyambut malaikat tanpa menyadarinya.
3 Ku riƙa tunawa da waɗanda suke a kurkuku kamar tare kuke a kurkuku, da kuma waɗanda ake gwada musu azaba, kamar ku ake yi wa.
Ingatlah mereka yang dikurung di penjara seolah-olah kalian juga sedang dipenjara bersama mereka. Ingatlah mereka yang dianiaya seolah-olah kalian juga secara fisik menderita bersama mereka.
4 Aure yă zama abin girmamawa ga kowa, a kuma kiyaye gadon aure da tsabta, gama Allah zai hukunta masu zina da kuma dukan masu fasikanci.
Setiap orang harus menghormati pernikahan. Suami dan istri harus setia satu sama lain. Allah akan menghakimi mereka yang melakukan perzinahan.
5 Ku kiyaye kanku daga yawan son kuɗi, ku kuma gamsu da abin da kuke da shi, gama Allah ya ce, “Ba zan taɓa bar ka ba; ba zan taɓa yashe ka ba.”
Jangan cinta kepada uang; puaslah dengan apa yang kalian miliki. Allah sendiri sudah berkata, “Aku tidak akan pernah mengecewakanmu; Aku tidak akan pernah menyerah atasmu.”
6 Saboda haka muna iya fitowa gabagadi, mu ce, “Ubangiji ne mai taimakona; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai iya yi mini?”
Itulah sebabnya kita dapat dengan yakin berkata, “Tuhanlah yang membantu saya, jadi saya tidak akan takut. Apa yang bisa dilakukan seseorang kepadaku?”
7 Ku tuna da shugabanninku, waɗanda suka faɗa muku maganar Allah. Ku dubi irin rayuwar da suka yi ku kuma yi koyi da bangaskiyarsu.
Ingatlah pemimpin kalian yang menjelaskan firman Allah kepada kalian. Lihat kembali hasil hidup mereka, dan tiru kepercayaan mereka pada Allah.
8 Yesu Kiristi ba ya sākewa, shi ne a jiya, shi ne a yau, shi ne kuma har abada. (aiōn g165)
Yesus Kristus tetap sama kemarin, hari ini, dan selamanya. (aiōn g165)
9 Kada a ɗauke muku hankali da sababbin koyarwa dabam-dabam. Yana da kyau zukatanmu su ƙarfafa ta wurin alheri, ba ta wurin abinci waɗanda ba su da amfani ga waɗanda suke cinsu.
Jangan terganggu oleh berbagai jenis ajaran yang aneh. Adalah baik bagi pikiran untuk diyakinkan oleh kasih karunia, bukan oleh hukum Taurat tentang apa yang kita makan. Mereka yang mengikuti hukum Taurat tidak mendapatkan apa-apa.
10 Muna da bagade inda firistocin da suka yi hidima a tabanakul ba su da izini su ci.
Kami memiliki mezbah yang tidak berhak dimakan oleh para imam Kemah Tuhan.
11 Babban firist yakan ɗauki jinin dabbobi yă shiga cikin Wuri Mafi Tsarki a matsayin hadaya ta zunubi, amma jikunan dabbobin akan ƙone su a bayan sansani.
Bangkai binatang yang darahnya dibawa oleh Imam Besar ke Ruang Maha Kudus sebagai kurban penghapus dosa, dibakar di luar perkemahan.
12 Haka ma Yesu ya sha wahala a bayan gari don yă tsarkake mutane ta wurin jininsa.
Dengan cara yang sama Yesus juga mati di luar gerbang kota agar Dia dapat menguduskan umat Allah melalui darahnya sendiri.
13 Saboda haka, sai mu fita mu je wajensa a bayan sansani, muna ɗaukar kunyar da ya sha.
Jadi marilah kita pergi kepada-Nya, di luar perkemahan, mengalami dan berbagi dalam rasa malu-Nya.
14 Gama a nan ba mu da dawwammamen birni, sai dai muna zuba ido a kan birnin nan mai zuwa.
Karena kita tidak memiliki kota permanen untuk ditinggali di bumi ini, kita sedang mencari rumah yang akan datang.
15 Saboda haka, ta wurin Yesu, bari mu ci gaba da miƙa hadaya ta yabo ga Allah, yabon leɓuna da yake shaidar sunansa.
Jadi biarlah kita melalui Yesus selalu mempersembahkan kurban pujian kepada Allah — ini berarti berbicara dengan baik tentang Allah, menyatakan karakter-Nya.
16 Kada kuma ku manta yin aikin nagari da kuma taimakon waɗansu, gama da irin waɗannan hadayu ne Allah yake jin daɗi.
Dan jangan lupa untuk melakukan perbuatan yang baik, dan untuk berbagi dengan orang lain apa yang kalian miliki, sebab Allah senang saat kalian melakukan pengorbanan seperti itu.
17 Ku yi wa shugabanninku biyayya ku kuma miƙa kanku ga ikonsu. Suna lura da ku kuma za su ba da lissafi a gaban Allah. Saboda haka kada ku sa su yi fushi saboda aikinsu, ku sa su yi farin ciki. In ba haka ba za su iya taimakonku ba ko kaɗan.
Ikuti para pemimpin kalian, dan lakukan perintah mereka, sebab mereka berjaga-jaga atas kalian dan harus bertanggung jawab untuk itu. Bertindaklah sedemikian rupa sehingga mereka mengerjakan tugas mereka dengan sukacita — dan bukan dengan kesedihan, karena hal itu tidak akan membantu kalian!
18 Ku yi mana addu’a. Mun tabbata cewa muna da lamiri mai kyau, kuma muna da marmari mu yi rayuwa ta bangirma a ta kowace hanya.
Tetaplah berdoa untuk kami. Kami yakin kami sudah bertindak dengan hati nurani yang baik, selalu ingin melakukan perbuatan yang baik dan benar dalam setiap situasi.
19 Ni musamman, ina roƙonku ku yi addu’a, don a komo da ni a gare ku ba da daɗewa ba.
Saya sangat ingin kalian berdoa dengan sungguh-sungguh agar saya bisa segera bertemu denganmu kembali.
20 Bari Allah na salama, wanda ta wurin jinin madawwamin alkawari ya tā da Ubangijinmu Yesu daga matattu, wannan Makiyayin tumaki mai girma, (aiōnios g166)
Sekarang semoga Allah Sang Damai yang menghidupkan kembali Tuhan kita Yesus, gembala domba yang agung, dari antara orang mati, dengan darah perjanjian kekal — (aiōnios g166)
21 yă kintsa ku da kowane abu mai kyau domin aikata nufinsa, bari kuma yă aikata abin da zai gamshe shi cikinmu, ta wurin Yesu Kiristi, a gare shi ɗaukaka ta tabbata har abada. Amin. (aiōn g165)
semoga Dia memberikan kepada kalian semua segala yang baik sehingga kalian dapat melakukan kehendak-Nya. Semoga Dia bekerja di dalam kita, melakukan segala sesuatu yang menyenangkan Dia, melalui Yesus Kristus — kemuliaan bagi-Nya selama-lamanya. Amin. (aiōn g165)
22 ’Yan’uwa, ina roƙonku ku yi haƙuri da wannan gargaɗi, don ba wata doguwar wasiƙa ce na rubuta muku ba.
Saya ingin mendorong kalian, saudara dan saudari, untuk memperhatikan apa yang sudah saya tulis kepada kalian dalam surat pendek ini.
23 Ina so ku san cewa an saki ɗan’uwanmu Timoti. In ya iso da wuri, zan zo tare da shi in gan ku.
Kalian harus tahu bahwa Timotius sudah dibebaskan. Jika dia bisa segera sampai di sini, saya akan ikut dengannya untuk menemui kalian.
24 Ku gai da dukan shugabanninku da kuma dukan mutanen Allah. Waɗanda suke Italiya suna gaishe ku.
Salam saya untuk semua pemimpin kalian, dan untuk semua orang percaya di sana. Orang-orang percaya di sini di Italia mengirimkan salam mereka.
25 Alheri yă kasance da ku duka.
Semoga kasih karunia Allah menyertai kalian semua. Amin.

< Ibraniyawa 13 >