< Ibraniyawa 12 >

1 Saboda haka, da yake muna kewaye da irin wannan taron shaidu mai girma, sai mu yar da duk abin da yake hana mu da kuma zunubin da yake saurin daure mu, mu kuma yi tseren da aka sa a gabanmu da nacewa.
לכן גם אנחנו אשר ענן עדים רב כזה סבב אתנו נשליכה ממנו כל טרח והחטא המקיף עלינו ונרוצה בתוחלת את המרוצה הערוכה לפנינו׃
2 Bari mu kafa idanunmu a kan Yesu, tushe da kuma kammalar bangaskiyarmu, wanda ya jure kunyar gicciye da aka yi masa, domin ya san cewa daga baya zai yi farin ciki ya yi haka. Yanzu kuma yana zaune a hannun dama na kursiyin Allah.
ונביטה אל ישוע ראש האמונה ומשלימה אשר בעד השמחה השמורה לו סבל את הצלב ויבז החרפה וישב לימין כסא האלהים׃
3 Ku lura da wannan wanda ya jure da irin hamayyan nan daga masu zunubi, don kada ku gaji, har ku fid da zuciya.
התבוננו אליו אשר נשא כלמת חטאים גדולה כזאת למען לא תיעפו ולא תיגעו בנפשותיכם׃
4 Cikin famanku da zunubi, ba ku yi tsayayya har ga zub da jininku ba tukuna.
עדין לא עמדתם עד לדם במלחמתכם עם החטא׃
5 Kun kuma manta da kalmar ƙarfafawan nan da tana ce da ku’ya’ya, “Ɗana kada ka rena horon Ubangiji, kada kuma ka fid da zuciya sa’ad da ya kwaɓe ka,
ותשכחו דבר הנחומים המדבר אליכם כמו אל בנים לאמר מוסר יהוה בני אל תמאס ואל תקץ בתוכחתו׃
6 domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, yakan kuma hori duk wanda yakan karɓa a matsayin ɗa.”
כי את אשר יאהב יהוה יוכיח יכאב את בן ירצה׃
7 Ku jimre shan wahala a matsayin horo; Allah yana yi da ku kamar’ya’ya. Gama wane ɗa ne mahaifinsa ba ya horonsa?
אם סבלים אתם מוסר דעו כי כאב עם בניו כן מתנהג אלהים עמכם כי איה הבן אשר אביו לא ייסרנו׃
8 In ba a hore ku ba (kowa kuwa yakan sami horo), to, ku shegu ne ba’ya’yan gida ba.
אך אם תהיו באין מוסר אשר היה מנת כלם אז ממזרים אתם ולא בנים׃
9 Ban da haka ma, dukanmu mun kasance da ubannin jiki waɗanda suka hore mu muka kuma yi musu ladabi. Ashe, bai kamata mu yi wa Uban ruhohinmu biyayya mu kuwa rayu ba!
ועוד אם אבות בשרנו היו מיסרים אתנו ונירא מהם אף כי נכנע לפני אבי הרוחות ונחיה׃
10 Ubanninmu sun hore mu na ɗan lokaci yadda suka ga ya fi kyau; amma Allah yakan hore mu don amfaninmu, domin mu sami rabo cikin tsarkinsa.
כי המה יסרונו כטוב בעיניהם לימים מעטים אבל זה להועיל למען יהיה לנו חלק בקדשתו׃
11 Babu horon da yake da daɗi a lokacin da ake yinsa, sai dai zafi. Amma daga baya waɗanda suka horu ta haka sukan sami kwanciyar rai wadda aikin adalci yake bayarwa.
וכל מוסר בעת עברו עלינו איננו שמחה בעינינו כי אם יגון אולם באחריתו יתן פרי שלום לצדקה למלמדים בו׃
12 Saboda haka, sai ku ƙarfafa raunanan hannuwanku da gwiwoyinku marasa ƙarfi!
על כן חזקו ידים רפות וברכים כשלות׃
13 “Ku shirya hanyoyi marasa gargaɗa saboda ƙafafunku,” don kada guragu su daɗa gurguntawa, sai dai su warke.
ומעגל רגליכם פלסו למען לא תטה הצלעה מן הדרך כי אם תרפא׃
14 Ku yi iyakacin ƙoƙari ku yi zaman lafiya da kowa, ku kuma zama masu tsarki; gama in ban da tsarki ba babu wanda zai ga Ubangiji.
רדפו את השלום עם כל אדם ואת הקדשה אשר בלעדיה לא יראה איש את האדון׃
15 Ku lura fa kada wani yă kāsa samun alherin Allah, kada kuma wani tushen ɗacin rai yă tsira har yă kawo rikici, yă kuma ƙazantar da mutane da yawa.
והזהרו פן יש בכם איש מתאחר מחסד אלהים פן יוגיעכם שרש פרה לענה ויטמאו בו רבים׃
16 Ku lura kada wani yă zama mai fasikanci, ko marar tsoron Allah kamar Isuwa, wanda saboda ƙwaryar abinci ɗaya tak ya sayar da gādonsa na ɗan fari.
פן ימצא בכם זנה או חלל כעשו אשר בנזיד אחד מכר את בכורתו׃
17 Daga baya, kamar yadda kuka sani, sa’ad da ya nemi yă gāji wannan albarka, aka ƙi shi. Bai sami zarafin tuba ba, ko da yake ya nemi albarkan nan da hawaye.
הלא ידעתם כי גם נמאס אחרי כן כאשר רצה לרשת את הברכה כי לא מצא מקום לתשובה אף בקש אותה בדמעות׃
18 Ba ku zo ga Dutsen Sinai wanda ana iya taɓawa ba, ko ga wuta mai ci sosai, ko ga duhu baƙi ƙirin, ko
כי לא באתם אל הר נמשש ובער באש ולא אל ענן וערפל וסערה׃
19 ko busar ƙaho, ko ga irin wata murya mai magana da kalmomin da masu jinta suka yi roƙo kada su ƙara ji,
ולא לקול שופר ולקול הדברים אשר שמעיו בקשו שלא יוסיף לדבר עמהם עוד׃
20 domin ba su iya jimrewa da abin da aka umarta cewa, “Ko da ma dabba ce ta taɓa dutsen, dole a jajjefe ta da duwatsu.”
כי לא יכלו לשאת את אשר צוו ואם בהמה תגע בהר סקל תקסל או ירה תירה בחצים׃
21 Ganin wannan abu da matuƙar bantsoro yake, har Musa ya ce, “Ina rawar jiki don tsoro.”
והמראה היה נורא עד מאד ויאמר משה יגרתי וחרדתי׃
22 Sai dai kun zo ne ga Dutsen Sihiyona, ga Urushalima ta sama, birnin Allah mai rai. Kun zo ga dubu dubban mala’ikun da suke cikin taron farin ciki,
כי אם באתם אל הר ציון ואל עיר אלהים חיים אל ירושלים שבשמים׃
23 kun zo ga ikkilisiyar ɗan fari, waɗanda sunayensu suna a rubuce a sama. Kun zo ga Allah, alƙalin dukan mutane, kun kuma zo ga ruhohin mutane masu adalci da aka mai da su cikakku.
ואל עצרת רבבות המלאכים ועדת הבכורים הכתובים בשמים ואל אלהים שפט הכל ואל רוחות הצדיקים הנשלמים׃
24 Kun zo ga Yesu, mai yin sulhu na sabon alkawari, da kuma ga jinin da aka yayyafa wanda yake magana mafi kyau fiye da jinin Habila.
ואל ישוע סרסר הברית החדשה ואל דם ההזאה המיטיב דבר מדם הבל׃
25 Ku lura fa kada ku ƙi wanda yake magana. Gama in su ba su tsira sa’ad da suka ƙi wanda ya gargaɗe su a wannan duniya ba, to, ƙaƙa mu za mu tsira, in mun ƙi jin wannan da yake yi mana gargaɗi daga Sama?
לכן ראו פן תמאנו לשמע אל המדבר כי הן לא נמלטו המאנים לשמע אל המדבר עמהם בארץ אף אנחנו אם נמאן לשמע בקול המדבר מן השמים׃
26 A lokacin nan muryarsa ta jijjiga duniya, amma yanzu ya yi alkawari cewa, “Har wa yau sau ɗaya tak zan ƙara jijjiga ba duniya kaɗai ba, amma har ma da sammai.”
אשר קולו הרעיש אז את הארץ ועתה זה הבטיח לאמר עוד אחת ואני מרעיש לא לבד את הארץ כי גם את השמים׃
27 Wannan magana “sau ɗayan nan” sun nuna, kawar da abin da za a iya jijjigawa, wato, ƙirƙiro abubuwa, saboda abubuwan da ba a iya jijjigawa, su kasance.
וזו עוד אחת שאמר משמיע חליפת הנרעשים אשר הם עשוים למען יעמד אשר איננו נרעש׃
28 Saboda haka, da yake muna karɓar mulkin da ba ya jijjiguwa, sai mu yi godiya, ta haka kuwa mu yi wa Allah sujada yadda ya kamata, tare da bangirma da kuma tsoro,
לכן אנחנו המקבלים מלכות אשר לא תמוט נבאה נא בתודה ונעבד בה את האלהים לרצון לו בצניעות וביראה׃
29 gama “Allahnmu wuta ne mai cinyewa.”
כי אלהינו אש אכלה הוא׃

< Ibraniyawa 12 >