< Ibraniyawa 12 >
1 Saboda haka, da yake muna kewaye da irin wannan taron shaidu mai girma, sai mu yar da duk abin da yake hana mu da kuma zunubin da yake saurin daure mu, mu kuma yi tseren da aka sa a gabanmu da nacewa.
Therefore, surrounded as we are by such a vast cloud of witnesses, let us fling aside every encumbrance and the sin that so readily entangles our feet. And let us run with patient endurance the race that lies before us,
2 Bari mu kafa idanunmu a kan Yesu, tushe da kuma kammalar bangaskiyarmu, wanda ya jure kunyar gicciye da aka yi masa, domin ya san cewa daga baya zai yi farin ciki ya yi haka. Yanzu kuma yana zaune a hannun dama na kursiyin Allah.
simply fixing our gaze upon Jesus, our Prince Leader in the faith, who will also award us the prize. He, for the sake of the joy which lay before Him, patiently endured the cross, looking with contempt upon its shame, and afterwards seated Himself-- where He still sits--at the right hand of the throne of God.
3 Ku lura da wannan wanda ya jure da irin hamayyan nan daga masu zunubi, don kada ku gaji, har ku fid da zuciya.
Therefore, if you would escape becoming weary and faint-hearted, compare your own sufferings with those of Him who endured such hostility directed against Him by sinners.
4 Cikin famanku da zunubi, ba ku yi tsayayya har ga zub da jininku ba tukuna.
In your struggle against sin you have not yet resisted so as to endanger your lives;
5 Kun kuma manta da kalmar ƙarfafawan nan da tana ce da ku’ya’ya, “Ɗana kada ka rena horon Ubangiji, kada kuma ka fid da zuciya sa’ad da ya kwaɓe ka,
and you have quite forgotten the encouraging words which are addressed to you as sons, and which say, "My son, do not think lightly of the Lord's discipline, and do not faint when He corrects you;
6 domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, yakan kuma hori duk wanda yakan karɓa a matsayin ɗa.”
for those whom the Lord loves He disciplines: and He scourges every son whom He acknowledges."
7 Ku jimre shan wahala a matsayin horo; Allah yana yi da ku kamar’ya’ya. Gama wane ɗa ne mahaifinsa ba ya horonsa?
The sufferings that you are enduring are for your discipline. God is dealing with you as sons; for what son is there whom his father does not discipline?
8 In ba a hore ku ba (kowa kuwa yakan sami horo), to, ku shegu ne ba’ya’yan gida ba.
And if you are left without discipline, of which every true son has had a share, that shows that you are bastards, and not true sons.
9 Ban da haka ma, dukanmu mun kasance da ubannin jiki waɗanda suka hore mu muka kuma yi musu ladabi. Ashe, bai kamata mu yi wa Uban ruhohinmu biyayya mu kuwa rayu ba!
Besides this, our earthly fathers used to discipline us and we treated them with respect, and shall we not be still more submissive to the Father of our spirits, and live?
10 Ubanninmu sun hore mu na ɗan lokaci yadda suka ga ya fi kyau; amma Allah yakan hore mu don amfaninmu, domin mu sami rabo cikin tsarkinsa.
It is true that they disciplined us for a few years according as they thought fit; but He does it for our certain good, in order that we may become sharers in His own holy character.
11 Babu horon da yake da daɗi a lokacin da ake yinsa, sai dai zafi. Amma daga baya waɗanda suka horu ta haka sukan sami kwanciyar rai wadda aikin adalci yake bayarwa.
Now, at the time, discipline seems to be a matter not for joy, but for grief; yet it afterwards yields to those who have passed through its training a result full of peace--namely, righteousness.
12 Saboda haka, sai ku ƙarfafa raunanan hannuwanku da gwiwoyinku marasa ƙarfi!
Therefore strengthen the drooping hands and paralysed knees,
13 “Ku shirya hanyoyi marasa gargaɗa saboda ƙafafunku,” don kada guragu su daɗa gurguntawa, sai dai su warke.
and make straight paths for your feet, so that what is lame may not be put entirely out of joint
14 Ku yi iyakacin ƙoƙari ku yi zaman lafiya da kowa, ku kuma zama masu tsarki; gama in ban da tsarki ba babu wanda zai ga Ubangiji.
but may rather be restored. Persistently strive for peace with all men, and for that growth in holiness apart from which no one will see the Lord.
15 Ku lura fa kada wani yă kāsa samun alherin Allah, kada kuma wani tushen ɗacin rai yă tsira har yă kawo rikici, yă kuma ƙazantar da mutane da yawa.
Be carefully on your guard lest there be any one who falls back from the grace of God; lest any root bearing bitter fruit spring up and cause trouble among you, and through it the whole brotherhood be defiled;
16 Ku lura kada wani yă zama mai fasikanci, ko marar tsoron Allah kamar Isuwa, wanda saboda ƙwaryar abinci ɗaya tak ya sayar da gādonsa na ɗan fari.
lest there be a fornicator, or an ungodly person like Esau, who, in return for a single meal, parted with the birthright which belonged to him.
17 Daga baya, kamar yadda kuka sani, sa’ad da ya nemi yă gāji wannan albarka, aka ƙi shi. Bai sami zarafin tuba ba, ko da yake ya nemi albarkan nan da hawaye.
For you know that even afterwards, when he wished to secure the blessing, he was rejected; for he found no opportunity for undoing what he had done, though he sought the blessing earnestly with tears.
18 Ba ku zo ga Dutsen Sinai wanda ana iya taɓawa ba, ko ga wuta mai ci sosai, ko ga duhu baƙi ƙirin, ko
For you have not come to a material object all ablaze with fire, and to gloom and darkness and storm and trumpet-blast and the sound of words--
19 ko busar ƙaho, ko ga irin wata murya mai magana da kalmomin da masu jinta suka yi roƙo kada su ƙara ji,
a sound of such a kind that those who heard it entreated that no more should be added.
20 domin ba su iya jimrewa da abin da aka umarta cewa, “Ko da ma dabba ce ta taɓa dutsen, dole a jajjefe ta da duwatsu.”
For they could not endure the order which had been given, "Even a wild beast, if it touches the mountain, shall be stoned to death;"
21 Ganin wannan abu da matuƙar bantsoro yake, har Musa ya ce, “Ina rawar jiki don tsoro.”
and so terrible was the scene that Moses said, "I tremble with fear."
22 Sai dai kun zo ne ga Dutsen Sihiyona, ga Urushalima ta sama, birnin Allah mai rai. Kun zo ga dubu dubban mala’ikun da suke cikin taron farin ciki,
On the contrary you have come to Mount Zion, and to the city of the ever-living God, the heavenly Jerusalem, to countless hosts of angels,
23 kun zo ga ikkilisiyar ɗan fari, waɗanda sunayensu suna a rubuce a sama. Kun zo ga Allah, alƙalin dukan mutane, kun kuma zo ga ruhohin mutane masu adalci da aka mai da su cikakku.
to the great festal gathering and Church of the first-born, whose names are recorded in Heaven, and to a Judge who is God of all, and to the spirits of righteous men made perfect,
24 Kun zo ga Yesu, mai yin sulhu na sabon alkawari, da kuma ga jinin da aka yayyafa wanda yake magana mafi kyau fiye da jinin Habila.
and to Jesus the negotiator of a new Covenant, and to the sprinkled blood which speaks in more gracious tones than that of Abel.
25 Ku lura fa kada ku ƙi wanda yake magana. Gama in su ba su tsira sa’ad da suka ƙi wanda ya gargaɗe su a wannan duniya ba, to, ƙaƙa mu za mu tsira, in mun ƙi jin wannan da yake yi mana gargaɗi daga Sama?
Be careful not to refuse to listen to Him who is speaking to you. For if they of old did not escape unpunished when they refused to listen to him who spoke on earth, much less shall we escape who turn a deaf ear to Him who now speaks from Heaven.
26 A lokacin nan muryarsa ta jijjiga duniya, amma yanzu ya yi alkawari cewa, “Har wa yau sau ɗaya tak zan ƙara jijjiga ba duniya kaɗai ba, amma har ma da sammai.”
His voice then shook the earth, but now we have His promise, "Yet again I will, once for all, cause not only the earth to tremble, but Heaven also."
27 Wannan magana “sau ɗayan nan” sun nuna, kawar da abin da za a iya jijjigawa, wato, ƙirƙiro abubuwa, saboda abubuwan da ba a iya jijjigawa, su kasance.
Here the words "Yet again, once for all" denote the removal of the things which can be shaken--created things--in order that the things which cannot be shaken may remain.
28 Saboda haka, da yake muna karɓar mulkin da ba ya jijjiguwa, sai mu yi godiya, ta haka kuwa mu yi wa Allah sujada yadda ya kamata, tare da bangirma da kuma tsoro,
Therefore, receiving, as we now do, a kingdom which cannot be shaken, let us cherish thankfulness so that we may ever offer to God an acceptable service, with godly reverence and awe.
29 gama “Allahnmu wuta ne mai cinyewa.”
For our God is also a consuming fire.