< Ibraniyawa 12 >

1 Saboda haka, da yake muna kewaye da irin wannan taron shaidu mai girma, sai mu yar da duk abin da yake hana mu da kuma zunubin da yake saurin daure mu, mu kuma yi tseren da aka sa a gabanmu da nacewa.
Therefore let us also, who have all these witnesses surrounding us like clouds, cast from us all encumbrances, and sin, which is always prepared for us; and let us run with patience the race that is appointed for us.
2 Bari mu kafa idanunmu a kan Yesu, tushe da kuma kammalar bangaskiyarmu, wanda ya jure kunyar gicciye da aka yi masa, domin ya san cewa daga baya zai yi farin ciki ya yi haka. Yanzu kuma yana zaune a hannun dama na kursiyin Allah.
And let us look on Jesus, who hath become the commencement and the completion of our faith; who, on account of the joy there was for him, endured the cross, and surrendered himself to opprobrium; and is seated on the right hand of the throne of God.
3 Ku lura da wannan wanda ya jure da irin hamayyan nan daga masu zunubi, don kada ku gaji, har ku fid da zuciya.
Behold, therefore, how much he suffered from sinners, from them who are adversaries of their own soul, that ye may not be discouraged, nor your soul become remiss.
4 Cikin famanku da zunubi, ba ku yi tsayayya har ga zub da jininku ba tukuna.
Ye have not yet come unto blood, in the contest against sin.
5 Kun kuma manta da kalmar ƙarfafawan nan da tana ce da ku’ya’ya, “Ɗana kada ka rena horon Ubangiji, kada kuma ka fid da zuciya sa’ad da ya kwaɓe ka,
And ye have forgotten the monition, which saith to you, as to children, My son, disregard not the chastening of the Lord; nor let thy soul faint, when thou art rebuked by him.
6 domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, yakan kuma hori duk wanda yakan karɓa a matsayin ɗa.”
For, whom the Lord loveth, he chasteneth; and he scourgeth those sons, for whom he hath kind regards.
7 Ku jimre shan wahala a matsayin horo; Allah yana yi da ku kamar’ya’ya. Gama wane ɗa ne mahaifinsa ba ya horonsa?
Therefore endure ye the chastisement; because God is dealing with you as with sons. For what son is there, whom his father chasteneth not?
8 In ba a hore ku ba (kowa kuwa yakan sami horo), to, ku shegu ne ba’ya’yan gida ba.
But if ye are without that chastisement, with which every one is chastened, ye are become strangers and not sons.
9 Ban da haka ma, dukanmu mun kasance da ubannin jiki waɗanda suka hore mu muka kuma yi musu ladabi. Ashe, bai kamata mu yi wa Uban ruhohinmu biyayya mu kuwa rayu ba!
And if our fathers of the flesh chastened us, and we revered them, how much more ought we to be submissive to our spiritual fathers, and live?
10 Ubanninmu sun hore mu na ɗan lokaci yadda suka ga ya fi kyau; amma Allah yakan hore mu don amfaninmu, domin mu sami rabo cikin tsarkinsa.
For they chastened us for a short time, according to their pleasure; but God, for our advantage, that we may become partakers of his holiness.
11 Babu horon da yake da daɗi a lokacin da ake yinsa, sai dai zafi. Amma daga baya waɗanda suka horu ta haka sukan sami kwanciyar rai wadda aikin adalci yake bayarwa.
Now all chastisement, in the time of it, is not accounted a matter of joy, but of grief: yet, afterwards, it yieldeth the fruits of peace and righteousness to them who are exercised by it.
12 Saboda haka, sai ku ƙarfafa raunanan hannuwanku da gwiwoyinku marasa ƙarfi!
Wherefore, strengthen ye your relaxed hands, and your tottering knees:
13 “Ku shirya hanyoyi marasa gargaɗa saboda ƙafafunku,” don kada guragu su daɗa gurguntawa, sai dai su warke.
and make straight paths for your feet, that the limb which is lame may not be wrenched, but may be healed.
14 Ku yi iyakacin ƙoƙari ku yi zaman lafiya da kowa, ku kuma zama masu tsarki; gama in ban da tsarki ba babu wanda zai ga Ubangiji.
Follow after peace with every man; and after holiness, without which a man will not see our Lord.
15 Ku lura fa kada wani yă kāsa samun alherin Allah, kada kuma wani tushen ɗacin rai yă tsira har yă kawo rikici, yă kuma ƙazantar da mutane da yawa.
And be careful, lest any be found among you destitute of the grace of God; or lest some root of bitterness shoot forth germs, and trouble you; and thereby many be defiled:
16 Ku lura kada wani yă zama mai fasikanci, ko marar tsoron Allah kamar Isuwa, wanda saboda ƙwaryar abinci ɗaya tak ya sayar da gādonsa na ɗan fari.
or lest any one be found among you a fornicator; or a heedless one like Esau, who for one mess of food, sold his primogeniture.
17 Daga baya, kamar yadda kuka sani, sa’ad da ya nemi yă gāji wannan albarka, aka ƙi shi. Bai sami zarafin tuba ba, ko da yake ya nemi albarkan nan da hawaye.
For ye know that, afterwards when he wished to inherit the blessing, he was rejected; for he found not a place for repentance, although he sought it with tears.
18 Ba ku zo ga Dutsen Sinai wanda ana iya taɓawa ba, ko ga wuta mai ci sosai, ko ga duhu baƙi ƙirin, ko
For ye have not come to the fire that burned, and the tangible mount; nor to the darkness and obscurity and tempest;
19 ko busar ƙaho, ko ga irin wata murya mai magana da kalmomin da masu jinta suka yi roƙo kada su ƙara ji,
nor to the sound of the trumpet, and the voice of words, which they who heard, entreated that it might no more be spoken to them;
20 domin ba su iya jimrewa da abin da aka umarta cewa, “Ko da ma dabba ce ta taɓa dutsen, dole a jajjefe ta da duwatsu.”
for they could not endure what was commanded. And even a beast, if it approached the mountain, was to be stoned.
21 Ganin wannan abu da matuƙar bantsoro yake, har Musa ya ce, “Ina rawar jiki don tsoro.”
And so terrible was the sight, that Moses said, I fear and tremble.
22 Sai dai kun zo ne ga Dutsen Sihiyona, ga Urushalima ta sama, birnin Allah mai rai. Kun zo ga dubu dubban mala’ikun da suke cikin taron farin ciki,
But ye have come to Mount Zion, and to the city of the living God, the Jerusalem that is in heaven; and to the assemblies of myriads of angels;
23 kun zo ga ikkilisiyar ɗan fari, waɗanda sunayensu suna a rubuce a sama. Kun zo ga Allah, alƙalin dukan mutane, kun kuma zo ga ruhohin mutane masu adalci da aka mai da su cikakku.
and to the church of the first-born, who are enrolled in heaven and to God the judge of all; and to the spirits of the just, who are perfected;
24 Kun zo ga Yesu, mai yin sulhu na sabon alkawari, da kuma ga jinin da aka yayyafa wanda yake magana mafi kyau fiye da jinin Habila.
and to Jesus, the Mediator of the new covenant; and to the sprinkling, of his blood, which speaketh better than that of Abel.
25 Ku lura fa kada ku ƙi wanda yake magana. Gama in su ba su tsira sa’ad da suka ƙi wanda ya gargaɗe su a wannan duniya ba, to, ƙaƙa mu za mu tsira, in mun ƙi jin wannan da yake yi mana gargaɗi daga Sama?
Beware, therefore, lest ye refuse to hear him who speaketh with you. For if they escaped not, who refused to hear him who spake with them on the earth, how much more shall we not, if we refuse to hear him who speaketh with us from heaven?
26 A lokacin nan muryarsa ta jijjiga duniya, amma yanzu ya yi alkawari cewa, “Har wa yau sau ɗaya tak zan ƙara jijjiga ba duniya kaɗai ba, amma har ma da sammai.”
Whose voice then shook the earth; but now he hath promised, and said, yet again once more, I will shake not the earth only, but also heaven.
27 Wannan magana “sau ɗayan nan” sun nuna, kawar da abin da za a iya jijjigawa, wato, ƙirƙiro abubuwa, saboda abubuwan da ba a iya jijjigawa, su kasance.
And this his expression, Once more, indicateth the mutation of the things that are shaken, because they are fabricated; that the things which will not be shaken, may remain.
28 Saboda haka, da yake muna karɓar mulkin da ba ya jijjiguwa, sai mu yi godiya, ta haka kuwa mu yi wa Allah sujada yadda ya kamata, tare da bangirma da kuma tsoro,
Since, therefore, we have received a kingdom that is unshaken, let us grasp the grace whereby we may serve and please God, with reverence and fear.
29 gama “Allahnmu wuta ne mai cinyewa.”
For our God is a consuming fire.

< Ibraniyawa 12 >