< Ibraniyawa 12 >

1 Saboda haka, da yake muna kewaye da irin wannan taron shaidu mai girma, sai mu yar da duk abin da yake hana mu da kuma zunubin da yake saurin daure mu, mu kuma yi tseren da aka sa a gabanmu da nacewa.
Therefore we also, having so great a cloud of witnesses surrounding us, having put off every weight and cleverly entangling sin, let us run by perseverance the contest being set before us.
2 Bari mu kafa idanunmu a kan Yesu, tushe da kuma kammalar bangaskiyarmu, wanda ya jure kunyar gicciye da aka yi masa, domin ya san cewa daga baya zai yi farin ciki ya yi haka. Yanzu kuma yana zaune a hannun dama na kursiyin Allah.
Looking to Jesus the pathfinder and perfecter of the faith, who, against the joy set before him, endured a cross, having despised the shame, and has sat down at the right hand of the throne of God.
3 Ku lura da wannan wanda ya jure da irin hamayyan nan daga masu zunubi, don kada ku gaji, har ku fid da zuciya.
For consider the man who endured such hostility against him by sinners, so that ye may not be weary in your souls, being disheartened.
4 Cikin famanku da zunubi, ba ku yi tsayayya har ga zub da jininku ba tukuna.
Ye have not yet resisted as far as blood, struggling against sin.
5 Kun kuma manta da kalmar ƙarfafawan nan da tana ce da ku’ya’ya, “Ɗana kada ka rena horon Ubangiji, kada kuma ka fid da zuciya sa’ad da ya kwaɓe ka,
And have ye forgotten the exhortation that reasons with you as with sons, My son, do not disparage the chastening of the Lord, nor become disheartened when punished by him?
6 domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, yakan kuma hori duk wanda yakan karɓa a matsayin ɗa.”
For whom the Lord loves he chastens. And he whips every son whom he receives.
7 Ku jimre shan wahala a matsayin horo; Allah yana yi da ku kamar’ya’ya. Gama wane ɗa ne mahaifinsa ba ya horonsa?
Because of chastening ye endure; God is treating you as with sons, for what son is there whom a father does not chasten?
8 In ba a hore ku ba (kowa kuwa yakan sami horo), to, ku shegu ne ba’ya’yan gida ba.
And if ye are without chastening, of which all have become participants, then ye are bastards, and not sons.
9 Ban da haka ma, dukanmu mun kasance da ubannin jiki waɗanda suka hore mu muka kuma yi musu ladabi. Ashe, bai kamata mu yi wa Uban ruhohinmu biyayya mu kuwa rayu ba!
Besides, we indeed have had chastisers-the fathers of our flesh-and we were turned around. Shall we not much more be subordinate to the Father of the spirits, and we will live?
10 Ubanninmu sun hore mu na ɗan lokaci yadda suka ga ya fi kyau; amma Allah yakan hore mu don amfaninmu, domin mu sami rabo cikin tsarkinsa.
For those men indeed for a few days chastened us according to that which seemed good to them, but he for that which is advantageous, in order to be partakers of his holiness.
11 Babu horon da yake da daɗi a lokacin da ake yinsa, sai dai zafi. Amma daga baya waɗanda suka horu ta haka sukan sami kwanciyar rai wadda aikin adalci yake bayarwa.
But of course no chastening for the present seems to be of joy but of sorrow, yet afterward it yields peaceable fruit of righteousness to those who have been trained by it.
12 Saboda haka, sai ku ƙarfafa raunanan hannuwanku da gwiwoyinku marasa ƙarfi!
Therefore lift up the drooping hands, and the feeble knees,
13 “Ku shirya hanyoyi marasa gargaɗa saboda ƙafafunku,” don kada guragu su daɗa gurguntawa, sai dai su warke.
and make straight paths for your feet, so that what is lame may not be turned away, but may be healed instead.
14 Ku yi iyakacin ƙoƙari ku yi zaman lafiya da kowa, ku kuma zama masu tsarki; gama in ban da tsarki ba babu wanda zai ga Ubangiji.
Pursue peace with all men, and the sanctification without which no man will see the Lord.
15 Ku lura fa kada wani yă kāsa samun alherin Allah, kada kuma wani tushen ɗacin rai yă tsira har yă kawo rikici, yă kuma ƙazantar da mutane da yawa.
Looking carefully lest any man fall short, away from the grace of God, lest any root of bitterness sprouting up would cause trouble, and by this many may be defiled,
16 Ku lura kada wani yă zama mai fasikanci, ko marar tsoron Allah kamar Isuwa, wanda saboda ƙwaryar abinci ɗaya tak ya sayar da gādonsa na ɗan fari.
lest a fornicator or profane man like Esau, who, in place of one meal sold his birthright.
17 Daga baya, kamar yadda kuka sani, sa’ad da ya nemi yă gāji wannan albarka, aka ƙi shi. Bai sami zarafin tuba ba, ko da yake ya nemi albarkan nan da hawaye.
For ye also know that wanting afterward to inherit the blessing, he was rejected, for he found no place of repentance, though having sought it with tears.
18 Ba ku zo ga Dutsen Sinai wanda ana iya taɓawa ba, ko ga wuta mai ci sosai, ko ga duhu baƙi ƙirin, ko
For ye have not come to a mountain being felt, and which burned with fire, and to darkness, and gloom, and a tempest,
19 ko busar ƙaho, ko ga irin wata murya mai magana da kalmomin da masu jinta suka yi roƙo kada su ƙara ji,
and a sound of a trumpet, and a voice of words, of which those who heard begged that a word not be added to them.
20 domin ba su iya jimrewa da abin da aka umarta cewa, “Ko da ma dabba ce ta taɓa dutsen, dole a jajjefe ta da duwatsu.”
For they did not bear that which was commanded, if even a beast should touch the mountain, it shall be stoned.
21 Ganin wannan abu da matuƙar bantsoro yake, har Musa ya ce, “Ina rawar jiki don tsoro.”
And so fearful was that which was made visible, that Moses said, I am terrified and trembling.
22 Sai dai kun zo ne ga Dutsen Sihiyona, ga Urushalima ta sama, birnin Allah mai rai. Kun zo ga dubu dubban mala’ikun da suke cikin taron farin ciki,
But ye have come to mount Zion, and to the city of a living God, a heavenly Jerusalem, and to myriads of agents,
23 kun zo ga ikkilisiyar ɗan fari, waɗanda sunayensu suna a rubuce a sama. Kun zo ga Allah, alƙalin dukan mutane, kun kuma zo ga ruhohin mutane masu adalci da aka mai da su cikakku.
to a festal gathering and assembly of firstborn sons who were enrolled in the heavens, and to God, a Judge of all, and to spirits of righteous men who were made fully perfect,
24 Kun zo ga Yesu, mai yin sulhu na sabon alkawari, da kuma ga jinin da aka yayyafa wanda yake magana mafi kyau fiye da jinin Habila.
and to Jesus a mediator of a new covenant, and to blood of sprinkling that speaks better than Abel.
25 Ku lura fa kada ku ƙi wanda yake magana. Gama in su ba su tsira sa’ad da suka ƙi wanda ya gargaɗe su a wannan duniya ba, to, ƙaƙa mu za mu tsira, in mun ƙi jin wannan da yake yi mana gargaɗi daga Sama?
Watch, that ye not refuse him who speaks. For if those men did not escape, having refused him who spoke a divine message on earth, much more we, those who turn away from him from the heavens,
26 A lokacin nan muryarsa ta jijjiga duniya, amma yanzu ya yi alkawari cewa, “Har wa yau sau ɗaya tak zan ƙara jijjiga ba duniya kaɗai ba, amma har ma da sammai.”
whose voice then shook the earth. But now he has promised, saying, Yet once, I shake not only the earth, but also the heaven.
27 Wannan magana “sau ɗayan nan” sun nuna, kawar da abin da za a iya jijjigawa, wato, ƙirƙiro abubuwa, saboda abubuwan da ba a iya jijjigawa, su kasance.
And the, Yet once, signifies the removal of the things being shaken-as of things that were made-so that the things not being shaken may remain.
28 Saboda haka, da yake muna karɓar mulkin da ba ya jijjiguwa, sai mu yi godiya, ta haka kuwa mu yi wa Allah sujada yadda ya kamata, tare da bangirma da kuma tsoro,
Therefore, receiving an immovable kingdom, we may have grace, through which we may serve God acceptably with reverence and awe.
29 gama “Allahnmu wuta ne mai cinyewa.”
For our God is also a consuming fire.

< Ibraniyawa 12 >