< Ibraniyawa 12 >
1 Saboda haka, da yake muna kewaye da irin wannan taron shaidu mai girma, sai mu yar da duk abin da yake hana mu da kuma zunubin da yake saurin daure mu, mu kuma yi tseren da aka sa a gabanmu da nacewa.
Derfor lader også os, efterdi vi have så stor en Sky af Vidner omkring os, aflægge enhver Byrde og Synden, som lettelig hilder os, og med Udholdenhed gennemløbe den foran os liggende Bane,
2 Bari mu kafa idanunmu a kan Yesu, tushe da kuma kammalar bangaskiyarmu, wanda ya jure kunyar gicciye da aka yi masa, domin ya san cewa daga baya zai yi farin ciki ya yi haka. Yanzu kuma yana zaune a hannun dama na kursiyin Allah.
idet vi se hen til Troens Begynder og Fuldender, Jesus, som for den foran ham liggende Glædes Skyld udholdt et Kors, idet han ringeagtede Skændselen, og som har taget Sæde på højre Side af Guds Trone.
3 Ku lura da wannan wanda ya jure da irin hamayyan nan daga masu zunubi, don kada ku gaji, har ku fid da zuciya.
Ja, tænker på ham, som har udholdt en sådan Modsigelse imod sig af Syndere, for at I ikke skulle blive trætte og forsagte i eders Sjæle,
4 Cikin famanku da zunubi, ba ku yi tsayayya har ga zub da jininku ba tukuna.
Endnu have I ikke stået imod indtil Blodet i eders Kamp imod Synden,
5 Kun kuma manta da kalmar ƙarfafawan nan da tana ce da ku’ya’ya, “Ɗana kada ka rena horon Ubangiji, kada kuma ka fid da zuciya sa’ad da ya kwaɓe ka,
og I have glemt Formaningen, der jo dog taler til eder som til Sønner: "Min Søn! agt ikke Herrens Tugtelse ringe, vær heller ikke forsagt, når du revses af ham;
6 domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, yakan kuma hori duk wanda yakan karɓa a matsayin ɗa.”
thi hvem Herren elsker, den tugter han, og han slår hårdelig hver Søn, som han tager sig af."
7 Ku jimre shan wahala a matsayin horo; Allah yana yi da ku kamar’ya’ya. Gama wane ɗa ne mahaifinsa ba ya horonsa?
Holder ud og lader eder tugte; Gud handler med eder som med Sønner; thi hvem er den Søn, som Faderen ikke tugter?
8 In ba a hore ku ba (kowa kuwa yakan sami horo), to, ku shegu ne ba’ya’yan gida ba.
Men dersom I ere uden Tugtelse, hvori alle have fået Del, da ere I jo uægte og ikke Sønner.
9 Ban da haka ma, dukanmu mun kasance da ubannin jiki waɗanda suka hore mu muka kuma yi musu ladabi. Ashe, bai kamata mu yi wa Uban ruhohinmu biyayya mu kuwa rayu ba!
Fremdeles, vore kødelige Fædre havde vi til Optugtere, og vi følte Ærefrygt; skulde vi da ikke meget mere underordne os under Åndernes Fader og leve?
10 Ubanninmu sun hore mu na ɗan lokaci yadda suka ga ya fi kyau; amma Allah yakan hore mu don amfaninmu, domin mu sami rabo cikin tsarkinsa.
thi hine tugtede os for nogle få Dage efter deres Tykke, men han gør det til vort Gavn, for at vi skulle få Del i hans Hellighed.
11 Babu horon da yake da daɗi a lokacin da ake yinsa, sai dai zafi. Amma daga baya waɗanda suka horu ta haka sukan sami kwanciyar rai wadda aikin adalci yake bayarwa.
Al Tugtelse synes vel, imedens den er nærværende, ikke at være til Glæde, men til Bedrøvelse; men siden giver den til Gengæld dem, som derved ere øvede, en Fredens Frugt i Retfærdighed.
12 Saboda haka, sai ku ƙarfafa raunanan hannuwanku da gwiwoyinku marasa ƙarfi!
Derfor, retter de slappede Hænder og de lammede Knæ,
13 “Ku shirya hanyoyi marasa gargaɗa saboda ƙafafunku,” don kada guragu su daɗa gurguntawa, sai dai su warke.
og træder lige Spor med eders Fødder, for at ikke det lamme skal vrides af Led, men snarere helbredes.
14 Ku yi iyakacin ƙoƙari ku yi zaman lafiya da kowa, ku kuma zama masu tsarki; gama in ban da tsarki ba babu wanda zai ga Ubangiji.
Stræber efter Fred med alle og efter Helliggørelsen, uden hvilken ingen skal se Herren;
15 Ku lura fa kada wani yă kāsa samun alherin Allah, kada kuma wani tushen ɗacin rai yă tsira har yă kawo rikici, yă kuma ƙazantar da mutane da yawa.
og ser til, at ikke nogen går Glip af Guds Nåde, at ikke nogen bitter Rod skyder op og gør Skade, og de mange smittes ved den;
16 Ku lura kada wani yă zama mai fasikanci, ko marar tsoron Allah kamar Isuwa, wanda saboda ƙwaryar abinci ɗaya tak ya sayar da gādonsa na ɗan fari.
at ikke nogen er en utugtig eller en vanhellig som Esau, der for een Ret Mad solgte sin Førstefødselsret.
17 Daga baya, kamar yadda kuka sani, sa’ad da ya nemi yă gāji wannan albarka, aka ƙi shi. Bai sami zarafin tuba ba, ko da yake ya nemi albarkan nan da hawaye.
Thi I vide, at han også siden, da han ønskede at arve Velsignelsen, blev forkastet (thi han fandt ikke Rum for Omvendelse), omendskønt han begærede den med Tårer.
18 Ba ku zo ga Dutsen Sinai wanda ana iya taɓawa ba, ko ga wuta mai ci sosai, ko ga duhu baƙi ƙirin, ko
I ere jo ikke komne til en håndgribelig og brændende Ild og til Mulm og Mørke og Uvejr,
19 ko busar ƙaho, ko ga irin wata murya mai magana da kalmomin da masu jinta suka yi roƙo kada su ƙara ji,
og ikke til Basunens Klang og til en talende Røst, hvorom de, der hørte den, bade, at der ikke mere måtte tales til dem.
20 domin ba su iya jimrewa da abin da aka umarta cewa, “Ko da ma dabba ce ta taɓa dutsen, dole a jajjefe ta da duwatsu.”
Thi de kunde ikke bære det, som blev påbudt: "Endog om et Dyr rører ved Bjerget, skal det stenes".
21 Ganin wannan abu da matuƙar bantsoro yake, har Musa ya ce, “Ina rawar jiki don tsoro.”
Og - så frygteligt var Synet - Moses sagde: "Jeg er forfærdet og bæver."
22 Sai dai kun zo ne ga Dutsen Sihiyona, ga Urushalima ta sama, birnin Allah mai rai. Kun zo ga dubu dubban mala’ikun da suke cikin taron farin ciki,
Men I ere komne til Zions Bjerg og til den levende Guds Stad, til det himmelske Jerusalem og til Englenes Titusinder i Højtidsskare
23 kun zo ga ikkilisiyar ɗan fari, waɗanda sunayensu suna a rubuce a sama. Kun zo ga Allah, alƙalin dukan mutane, kun kuma zo ga ruhohin mutane masu adalci da aka mai da su cikakku.
og til de førstefødtes Menighed, som ere indskrevne i Himlene, og til en Dommer, som er alles Gud, og til de fuldkommede retfærdiges Ånder
24 Kun zo ga Yesu, mai yin sulhu na sabon alkawari, da kuma ga jinin da aka yayyafa wanda yake magana mafi kyau fiye da jinin Habila.
og til den nye Pagts Mellemmand, Jesus, og til Bestænkelsens Blod, som taler bedre end Abel.
25 Ku lura fa kada ku ƙi wanda yake magana. Gama in su ba su tsira sa’ad da suka ƙi wanda ya gargaɗe su a wannan duniya ba, to, ƙaƙa mu za mu tsira, in mun ƙi jin wannan da yake yi mana gargaɗi daga Sama?
Ser til, at I ikke bede eder fri for den, som taler. Thi når de, som bade sig fri for ham, der talte sit Guddomsord på Jorden, ikke undslap, da skulle vi det meget mindre, når vi vende os bort fra ham, der taler fra Himlene,
26 A lokacin nan muryarsa ta jijjiga duniya, amma yanzu ya yi alkawari cewa, “Har wa yau sau ɗaya tak zan ƙara jijjiga ba duniya kaɗai ba, amma har ma da sammai.”
han, hvis Røst dengang rystede Jorden, men som nu har forjættet og sagt: "Endnu een Gang vil jeg ryste, ikke alene Jorden, men også Himmelen."
27 Wannan magana “sau ɗayan nan” sun nuna, kawar da abin da za a iya jijjigawa, wato, ƙirƙiro abubuwa, saboda abubuwan da ba a iya jijjigawa, su kasance.
Men dette "endnu een Gang" giver til Kende, at de Ting, der rystes, skulle omskiftes, efterdi de ere skabte, for at de Ting, der ikke rystes, skulle blive.
28 Saboda haka, da yake muna karɓar mulkin da ba ya jijjiguwa, sai mu yi godiya, ta haka kuwa mu yi wa Allah sujada yadda ya kamata, tare da bangirma da kuma tsoro,
Derfor, efterdi vi modtage et Rige, som ikke kan rystes, så lader os være taknemmelige og derved tjene Gud til hans Velbehag, med Ængstelse og Frygt.
29 gama “Allahnmu wuta ne mai cinyewa.”
Thi vor Gud er en fortærende Ild.