< Ibraniyawa 11 >
1 Bangaskiya ita ce kasance tabbacin abin da muke bege a kai da kuma tabbatar da abin da ba mu gani ba.
А віра — то підста́ва споді́ваного, доказ неба́ченого.
2 Abin da aka yabi kakanni na dā a kai ke nan.
Бо нею засвідчені ста́рші були́.
3 Ta wurin bangaskiya ne muka fahimci cewa an halicci duniya bisa ga umarnin Allah, saboda an halicce abin da ake gani daga abin da ba a gani. (aiōn )
Вірою ми розуміємо, що віки́ Словом Божим збудовані, так що з невидимого сталось видиме. (aiōn )
4 Ta wurin bangaskiya Habila ya miƙa wa Allah hadayar da ta fi wadda Kayinu ya miƙa. Ta wurin bangaskiya aka yabe shi cewa shi mai adalci ne, sa’ad da Allah ya yi magana mai kyau game da bayarwarsa. Ta wurin bangaskiya kuma har yanzu yana magana, ko da yake ya riga ya mutu.
Вірою Авель приніс Богові жертву кращу, як Ка́їн; нею засвідчений був, що він праведний, як Бог сві́дчив про да́ри його; нею, і вмерши, він ще промовляє.
5 Ta wurin bangaskiya ne aka ɗauki Enok daga wannan rayuwa, ta haka bai ɗanɗana mutuwa ba; ba a kuwa same shi ba, domin Allah ya ɗauke shi. Gama kafin a ɗauke shi, an yabe shi a kan ya gamshi Allah.
Вірою Ено́х був перене́сений на небо, щоб не бачити смерти; і його не знайшли, бо Бог переніс його. Бо раніш, як його перенесено, він був засвідчений, що „Богові він догоди́в“.
6 In ba tare da bangaskiya ba kuwa, ba ya yiwuwa a gamshi Allah, domin duk mai zuwa wurin Allah dole yă gaskata cewa yana nan, kuma shi ne yakan sāka wa waɗanda suke nemansa da gaske.
Догоди́ти ж без віри не можна. І той, хто до Бога приходить, мусить вірувати, що Він є, а тим, хто шукає Його, Він дає нагороду.
7 Ta wurin bangaskiya Nuhu, sa’ad da aka yi masa gargaɗi a kan abubuwan da ba a gani ba tukuna, a cikin tsoro mai tsarki ya sassaƙa jirgi don ceton iyalinsa. Ta wurin bangaskiyarsa ya hukunta duniya ya kuma zama magājin adalcin da ake samu ta wurin bangaskiya.
Вірою Ной, як дістав об'я́влення про те, чого́ ще не бачив, побоявшись, зробив ковчега, щоб дім свій спасти́; нею світ засудив він, і став спадкоє́мцем праведности, що з віри вона.
8 Ta wurin bangaskiya ne Ibrahim, sa’ad da aka kira shi ya fita zuwa wata ƙasar da zai karɓi gādo daga baya, ya kuwa yi biyayya ya tafi, ko da yake bai san inda za shi ba.
Вірою Авраа́м, покликаний на місце, яке мав прийняти в спа́дщину, послухався та й пішов, не відаючи, куди йде.
9 Ta wurin bangaskiya ya yi zama a ƙasar da aka yi masa alkawari kamar baƙo a baƙuwar ƙasa; ya zauna a tentuna, haka ma Ishaku da Yaƙub, waɗanda su ma magādan alkawarin nan ne tare da shi.
Вірою він перебува́в на Землі Обі́цяній, як на чужій, і проживав у наме́тах з Іса́ком та Яковом, співспадкоє́мцями тієї ж обі́тниці,
10 Gama yana zuba ido ga birnin nan mai tushe, wanda mai zānen gininsa da kuma mai gininsa Allah ne.
бо чекав він міста, що має підва́лини, що Бог його будівни́чий та творе́ць.
11 Ta wurin bangaskiya Ibrahim, ko da yake shekarunsa sun wuce, Saratu kanta kuma bakararriya ce ya iya zama mahaifi domin ya amince cewa shi wanda ya yi alkawarin mai aminci ne.
Вірою й Са́ра сама дістала силу прийняти насіння, і породила понад час свого віку, бо вірним вважала Того, Хто обі́тницю дав.
12 Saboda haka, daga mutum ɗaya, wanda dā shi ma da matacce kusan ɗaya ne, zuriya masu yawa suka fito kamar taurari a sararin sama da kuma kamar yashin da ba a iya ƙirgawa a bakin teku.
Тому́ й від одно́го, та ще змертвілого, народилось так багато, як зо́рі небесні й пісок незчисле́нний край моря.
13 Duk mutanen nan suna cikin bangaskiya sa’ad da suka mutu. Ba su kuwa karɓi abubuwan da aka yi alkawari ba; sun dai hango su suka kuma marabce su daga nesa. Suka kuma amince cewa su baƙi ne, bare kuma a duniya.
Усі вони повмирали за вірою, не оде́ржавши обі́тниць, але зда́лека бачили їх, і повітали, і ві́рували в них, та визнавали, що „вони на землі чужани́ці й прихо́дьки“.
14 Mutane masu faɗin irin abubuwan nan sun nuna cewa suna neman ƙasar da take tasu.
Бо ті, що говорять таке, виявляють, що шукають ба́тьківщини.
15 Da a ce suna tunanin ƙasar da suka bari a baya, da sun riga sun sami damar komawa.
І коли б вони пам'ятали ту, що вийшли з неї, то мали б час повернутись.
16 A maimako, suna marmarin wata ƙasa mafi kyau, ta sama. Saboda haka Allah ba ya kunya a kira shi Allahnsu, domin ya riga ya shirya musu birni.
Та бажають вони тепер кращої, цебто небесної, тому́ й Бог не соро́миться їх, щоб звати Себе їхнім Богом, бо Він приготува́в їм місто.
17 Ta wurin bangaskiya Ibrahim, sa’ad da Allah ya gwada shi, sai ya miƙa Ishaku hadaya. Shi da ya karɓi alkawaran ya yi shirin miƙa makaɗaicin ɗansa,
Вірою Авраа́м, випробо́вуваний, привів на жертву Ісака, і, мавши обі́тницю, приніс одноро́дженого,
18 ko da yake Allah ya ce masa, “Ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.”
що йому було сказано: „В Ісакові буде насіння тобі“.
19 Ibrahim ya yi tunani cewa Allah yana iya tā da matattu, a misalce kuwa, ya sāke karɓan Ishaku daga matattu.
Бо він розумі́в, що Бог має силу й воскресити з мертвих, тому й одержав його на проо́браз.
20 Ta wurin bangaskiya ne Ishaku ya albarkaci Yaƙub da Isuwa game da nan gabansu.
Вірою в майбу́тнє поблагословив Іса́к Якова та Іса́ва.
21 Ta wurin bangaskiya ne Yaƙub, sa’ad da yake bakin mutuwa, ya albarkaci kowane ɗan Yusuf, ya kuma yi sujada yayinda yake jingine a kan sandansa.
Вірою Яків, умираючи, поблагословив кожного сина Йо́сипового, і „схилився на верх свого́ жезла.“
22 Ta wurin bangaskiya ne Yusuf, sa’ad da kwanakinsa suka yi kusan ƙarewa, ya yi magana game da fitowar Isra’ilawa daga Masar ya kuma ba da umarni game da ƙasusuwansa.
Вірою Йо́сип, умираючи, згадав про ви́хід синів Ізра́їлевих та про кості свої запові́в.
23 Ta wurin bangaskiya ne iyayen Musa suka ɓoye shi har wata uku bayan haihuwarsa, domin sun ga cewa shi ba kamar sauran yara ba ne, ba su kuwa ji tsoron umarnin sarki ba.
Вірою Мойсе́й, як родився, перехо́вувався батьками своїми три місяці, бо вони бачили, що гарне дитя, і не злякались нака́зу царе́вого.
24 Ta wurin bangaskiya ne Musa, sa’ad da ya yi girma, ya ƙi a kira shi ɗan diyar Fir’auna.
Вірою Мойсе́й, коли виріс, відрікся зватися сином дочки́ фарао́нової.
25 Ya zaɓa yă sha wahala tare da mutanen Allah, maimakon yă ji daɗin sha’awace-sha’awacen zunubi na ɗan lokaci.
Він хотів краще страждати з наро́дом Божим, аніж мати доча́сну гріховну потіху.
26 Ya ɗauki wulaƙancin da yake sha saboda Kiristi ya fi dukiyar Masar daraja, domin ya sa ido ga ladansa.
Він наругу Христову вважав за більше багатство, ніж ска́рби єгипетські, бо він озирався на Божу нагороду.
27 Ta wurin bangaskiya ya bar Masar, ba tare da jin tsoron fushin sarki ba; ya kuwa jure domin ya ga wannan wanda ba a iya gani.
Вірою він покинув Єгипет, не злякавшися гніву царе́вого, бо він був непохитний, як той, хто Невиди́мого бачить.
28 Ta wurin bangaskiya ya kiyaye Bikin Ƙetarewa ya kuma yayyafa jini, domin kada mai hallakar’ya’yan fari yă taɓa’ya’yan fari na Isra’ila.
Вірою справив він Пасху й покро́плення крови, щоб їх не торкнувся той, хто погубив первороджених.
29 Ta wurin bangaskiya ne mutane suka bi ta cikin Jan Teku, sai ka ce a kan busasshiyar ƙasa; amma da Masarawa suka yi ƙoƙari su yi haka, sai aka nutsar da su.
Вірою вони перейшли Червоне море, немов суходо́лом, на що спокусившись єги́птяни, потопились.
30 Ta wurin bangaskiya ne katangar Yeriko ta rushe, bayan mutane suka yi ta kewaye ta har kwana bakwai.
Вірою впали єрихо́нські му́ри по семиденнім обхо́дженні їх.
31 Ta wurin bangaskiya ne ba a kashe Rahab karuwan nan, ta tare da marasa biyayya ba don ta marabci’yan leƙan asiri.
Вірою блудни́ця Раха́в не згинула з невірними, коли з миром прийняла́ виві́дувачів.
32 Me kuma zan faɗa? Ba ni da lokacin da zan ba da labari a kan Gideyon, Barak, Samson, Yefta, Dawuda, Sama’ila, da kuma annabawa,
І що ще скажу́? Бо не стане ча́су мені, щоб оповіда́ти про Гедео́на, Вара́ка, Самсо́на, Ефта́я, Дави́да й Самуї́ла та про пророків,
33 waɗanda ta wurin bangaskiya ne suka ci nasara a kan mulkoki, suka aikata adalci, suka kuma sami abin da aka yi alkawari; waɗanda suka rurrufe bakunan zakoki,
що вірою ца́рства побива́ли, правду чинили, оде́ржували обі́тниці, пащі левам загороджували,
34 suka kashe harshen wuta, suka kuma tsere wa kaifin takobi; waɗanda aka mai da rashin ƙarfinsu ya zama ƙarfi; waɗanda suka yi jaruntaka wajen yaƙi suka kuma fatattaki mayaƙan waɗansu ƙasashe.
силу огне́нну гасили, утікали від ві́стря меча, зміцнялись від слабости, хоробрі були́ на війні, оберта́ли в розтіч полки́ чужоземців;
35 Mata suka karɓi ƙaunatattunsu da aka sāke tasar daga matattu. Aka azabtar da yawancin mutanen nan, amma suka ƙi a sake su, domin sun tabbata za su sami lada mafi kyau sa’ad da aka tā da matattu.
жінки діставали поме́рлих своїх із воскресі́ння; а інші бували скатовані, не прийнявши визво́лення, щоб отримати краще воскресі́ння;
36 Waɗansu suka sha ba’a da bulala, har da dauri da sarƙa, da kuma jefa su cikin kurkuku.
а інші дізнали наруги та рани, а також кайда́ни й в'язниці.
37 Aka jajjefe su da duwatsu; aka raba su biyu da zarto; aka kashe su da takobi. Suka yi ta yawo saye da fatun tumaki da na awaki, suka yi zaman rashi, suka sha tsanani da kuma wulaƙanci
Камінням побиті бува́ли, допитувані, перепи́лювані, умирали, зару́бані мече́м, тинялися в овечих та ко́зячих шкурах, збідовані, засумовані, витерпілі.
38 duniya ba tă ma cancanci su zauna a cikinta ba. Suka yi ta yawo a cikin hamada da a kan duwatsu, da cikin kogwanni da kuma cikin ramummuka.
Ті, що світ не вартий був їх, тинялися по пустинях та го́рах, і по печерах та прова́ллях зе́мних.
39 Waɗannan duka an yabe su saboda bangaskiyarsu, duk da haka babu waninsu da ya sami abin da aka yi alkawari.
І всі вони, одержавши засвідчення вірою, обі́тниці не прийняли́,
40 Allah ya shirya mana wani abu mafi kyau. Kuma bai so su kai ga maƙasudin bangaskiyarsu ba sai tare da mu.
бо Бог передбачив щось краще про нас, — щоб вони не без нас досконалість оде́ржали.