< Ibraniyawa 11 >

1 Bangaskiya ita ce kasance tabbacin abin da muke bege a kai da kuma tabbatar da abin da ba mu gani ba.
Biswas to hoile, amikhan ki asha kore, juntu nadikhe, hoilebi hosa ase aru pabo koi kene jane.
2 Abin da aka yabi kakanni na dā a kai ke nan.
Taikhan laga biswas nimite he amikhan laga baba khan ke Isor pora thik ase koi dise.
3 Ta wurin bangaskiya ne muka fahimci cewa an halicci duniya bisa ga umarnin Allah, saboda an halicce abin da ake gani daga abin da ba a gani. (aiōn g165)
Biswas pora he etu pura shristi to Isor laga hukum pora bonai dise koi kene amikhan jane, etu nimite ki saman dikhi ase eitu khan nadikha laga saman pora bona nohoi. (aiōn g165)
4 Ta wurin bangaskiya Habila ya miƙa wa Allah hadayar da ta fi wadda Kayinu ya miƙa. Ta wurin bangaskiya aka yabe shi cewa shi mai adalci ne, sa’ad da Allah ya yi magana mai kyau game da bayarwarsa. Ta wurin bangaskiya kuma har yanzu yana magana, ko da yake ya riga ya mutu.
Biswas pora Abel he Cain pora bhi bhal daan Isor ke dise, etu pora taike dharmik bonai dise, aru Isor pora tai laga daan dikhi kene bhal kotha koise, aru biswas pora he aji tak Abel kotha kore, tai mori jaise hoile bhi.
5 Ta wurin bangaskiya ne aka ɗauki Enok daga wannan rayuwa, ta haka bai ɗanɗana mutuwa ba; ba a kuwa same shi ba, domin Allah ya ɗauke shi. Gama kafin a ɗauke shi, an yabe shi a kan ya gamshi Allah.
Biswas pora he Enoch ke Isor logot sorgote uthaikene loi jaise aru tai mora ke dikha nai. “Taike puwa nai kele koile Isor pora taike loi jaise.” Taike loi naja age te, tai Isor ke khushi korise koi kene gawahi dise.
6 In ba tare da bangaskiya ba kuwa, ba ya yiwuwa a gamshi Allah, domin duk mai zuwa wurin Allah dole yă gaskata cewa yana nan, kuma shi ne yakan sāka wa waɗanda suke nemansa da gaske.
Etiya biswas nathakile Isor ke khushi kori bole na paribo. Kelemane kun Isor usorte ahe Tai jinda ase koi kene biswas kori bole lage aru kun manu Taike bisare taikhan ke inam dibo.
7 Ta wurin bangaskiya Nuhu, sa’ad da aka yi masa gargaɗi a kan abubuwan da ba a gani ba tukuna, a cikin tsoro mai tsarki ya sassaƙa jirgi don ceton iyalinsa. Ta wurin bangaskiyarsa ya hukunta duniya ya kuma zama magājin adalcin da ake samu ta wurin bangaskiya.
Biswas pora Noah ke, ki nadikhe etu laga kotha khan janibole dise, Isor ke bhoi kori kene thaka nimite, tai laga ghor manu khan ke bachai lobole nimite pani laga jahaaj bona bole dise. Etu kori kene, tai prithibi ke ninda korise aru dharmikta laga uttoradhikari hoise, biswas pora.
8 Ta wurin bangaskiya ne Ibrahim, sa’ad da aka kira shi ya fita zuwa wata ƙasar da zai karɓi gādo daga baya, ya kuwa yi biyayya ya tafi, ko da yake bai san inda za shi ba.
Biswas pora Abraham, jitia Isor pora taike matise, kotha mani kene tai pabole thaka jagate jaise. Tai ulaikene jaise, kun jagate jabo lage etu bhi najani kene jaise.
9 Ta wurin bangaskiya ya yi zama a ƙasar da aka yi masa alkawari kamar baƙo a baƙuwar ƙasa; ya zauna a tentuna, haka ma Ishaku da Yaƙub, waɗanda su ma magādan alkawarin nan ne tare da shi.
Biswas pora tai Isor pora kosom diya laga jagate jai kene dusra desh laga manu nisena thakise. Ta te tai tombu ghor te Isaac aru Jacob, kun tai logot Isor pora diya uttoradhikari paise, taikhan ke loi kene thakise.
10 Gama yana zuba ido ga birnin nan mai tushe, wanda mai zānen gininsa da kuma mai gininsa Allah ne.
Kelemane tai ekta bhal pora bhetimul dikena bona laga sheher ke sai thakise, aru etu Isor pora bona ase.
11 Ta wurin bangaskiya Ibrahim, ko da yake shekarunsa sun wuce, Saratu kanta kuma bakararriya ce ya iya zama mahaifi domin ya amince cewa shi wanda ya yi alkawarin mai aminci ne.
Biswas pora, Sarah buri hoi jaile bhi, bacha bukhi bole parise, kelemane Isor pora ki kosom dise tai etu uporte biswas korise.
12 Saboda haka, daga mutum ɗaya, wanda dā shi ma da matacce kusan ɗaya ne, zuriya masu yawa suka fito kamar taurari a sararin sama da kuma kamar yashin da ba a iya ƙirgawa a bakin teku.
Etu nimite, ekjon manu pora- juntu Abraham ase, mori bole he thakise- akas te ginti kori bole napara tara nisena tai laga khandan khan jonom hoise, aru taikhan to samundar kinar te balu thaka nisena ginti kori bole napara laga hoi jaise.
13 Duk mutanen nan suna cikin bangaskiya sa’ad da suka mutu. Ba su kuwa karɓi abubuwan da aka yi alkawari ba; sun dai hango su suka kuma marabce su daga nesa. Suka kuma amince cewa su baƙi ne, bare kuma a duniya.
Taikhan sob kosom napa age te biswas te mori jaise, kintu bisi dur te taikhan pora eitu khan sob dikhise aru khusi paise. Aru taikhan nijor pora taikhan to dusra desh te thaki ase aru prithibi te nijor manu pora dur hoi kene ase koise.
14 Mutane masu faɗin irin abubuwan nan sun nuna cewa suna neman ƙasar da take tasu.
Kelemane kun manu khan eneka kotha kore, taikhan nijor laga ghor bona bole bisari ase.
15 Da a ce suna tunanin ƙasar da suka bari a baya, da sun riga sun sami damar komawa.
Jodi taikhan kun to desh pora ulaikene jaise etu bhabi thakise koile, taikhan ta te aru bhi wapas ghurabole paribo thakise.
16 A maimako, suna marmarin wata ƙasa mafi kyau, ta sama. Saboda haka Allah ba ya kunya a kira shi Allahnsu, domin ya riga ya shirya musu birni.
Kintu, taikhan etu pora bhi bhal desh nimite itcha korise, etu hoile, sorgote thaka ula. Etu nimite Isor to taikhan laga Isor ase kobole sorom nakore, kelemane Tai pora taikhan nimite ekta sheher bonai kene rakhise.
17 Ta wurin bangaskiya Ibrahim, sa’ad da Allah ya gwada shi, sai ya miƙa Ishaku hadaya. Shi da ya karɓi alkawaran ya yi shirin miƙa makaɗaicin ɗansa,
Biswas pora he Abraham, jitia Isor pora taike porikha korise, Isaac ke bolidan dibole taiyar hoise. Tai bhi Isor pora asirbad paise aru tai laga ekjon bacha thaka ke bhi bolidan kori bole itcha thakise.
18 ko da yake Allah ya ce masa, “Ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.”
Isor pora taike eneka koisele, “Isaac laga naam pora he tumi laga khandan laga naam matibo.”
19 Ibrahim ya yi tunani cewa Allah yana iya tā da matattu, a misalce kuwa, ya sāke karɓan Ishaku daga matattu.
Abraham jani thakise Isor pora Isaac ke mora pora jinda kori bole paribo, aru bhabona nisena, tai Isaac ke etu jaga pora wapas pai loise.
20 Ta wurin bangaskiya ne Ishaku ya albarkaci Yaƙub da Isuwa game da nan gabansu.
Biswas pora he, ki ahibole ase etu nimite, Isaac pora Jacob aru Esau ke asirbad dise.
21 Ta wurin bangaskiya ne Yaƙub, sa’ad da yake bakin mutuwa, ya albarkaci kowane ɗan Yusuf, ya kuma yi sujada yayinda yake jingine a kan sandansa.
Biswas pora, jitia Jacob mori bole thakise, tai laga lathi uporte khara kori kene mohima korise, aru tai laga sob bacha khan ke tai asirbad dise.
22 Ta wurin bangaskiya ne Yusuf, sa’ad da kwanakinsa suka yi kusan ƙarewa, ya yi magana game da fitowar Isra’ilawa daga Masar ya kuma ba da umarni game da ƙasusuwansa.
Biswas pora Joseph, jitia tai mori bole thakise, tai laga chokra khan ke tai mora pichete Egypt pora tai laga hardi khan loi kene Israel te rakhibole nimite koise.
23 Ta wurin bangaskiya ne iyayen Musa suka ɓoye shi har wata uku bayan haihuwarsa, domin sun ga cewa shi ba kamar sauran yara ba ne, ba su kuwa ji tsoron umarnin sarki ba.
Biswas pora Moses, jitia jonom loise le, tai laga baba ama pora tin mohina tak taike lukai kene rakhise, kelemane tai sabole bisi sundur thakise, aru raja pora ki hukum dise etu nimite taikhan bhoi kora nai.
24 Ta wurin bangaskiya ne Musa, sa’ad da ya yi girma, ya ƙi a kira shi ɗan diyar Fir’auna.
Biswas pora Moses, jitia tai dangor hoi jaise, tai nijorke Pharoah laga chukri laga chokra kobole nimite mana korise.
25 Ya zaɓa yă sha wahala tare da mutanen Allah, maimakon yă ji daɗin sha’awace-sha’awacen zunubi na ɗan lokaci.
Kintu, tai nijorke Isor manu khan karone dukh pabole nimite basi loise, mangso laga itcha sob chari kene Isor ke sewa korise.
26 Ya ɗauki wulaƙancin da yake sha saboda Kiristi ya fi dukiyar Masar daraja, domin ya sa ido ga ladansa.
Tai koise Jisu Khrista laga dhun to Egypt laga dhun pora bhi bisi dangor ase. Kelemane tai suku to tai inam pabole thaka ke sai thakise.
27 Ta wurin bangaskiya ya bar Masar, ba tare da jin tsoron fushin sarki ba; ya kuwa jure domin ya ga wannan wanda ba a iya gani.
Biswas pora Moses Egypt chari kene jaise. Tai raja laga ghusa ke eku hisab kora nai, tai dukh pa-a homoi te, nadikha ekjon ke saithaka nisena bhabona kori kene dhorjo kori loise.
28 Ta wurin bangaskiya ya kiyaye Bikin Ƙetarewa ya kuma yayyafa jini, domin kada mai hallakar’ya’yan fari yă taɓa’ya’yan fari na Isra’ila.
Biswas pora tai Israel manu khan ke Nistar aru khun hali diya din manaise, etu pora prothom jonom kora bacha khan ke morai diya laga atma ahi kene namorabo nimite.
29 Ta wurin bangaskiya ne mutane suka bi ta cikin Jan Teku, sai ka ce a kan busasshiyar ƙasa; amma da Masarawa suka yi ƙoƙari su yi haka, sai aka nutsar da su.
Biswas pora Yehudi khan dangor samundar to ekta sukha matite jai thaka nisena paar kori bole parise. Jitia Egypt khan eneka kori bole bisarise, taikhan ke pani pora khai loise.
30 Ta wurin bangaskiya ne katangar Yeriko ta rushe, bayan mutane suka yi ta kewaye ta har kwana bakwai.
Biswas pora Jericho sheher laga dewar khan giri jaise, jitia Israel manu khan sath din tak ta te ghuri kene thakise.
31 Ta wurin bangaskiya ne ba a kashe Rahab karuwan nan, ta tare da marasa biyayya ba don ta marabci’yan leƙan asiri.
Biswas pora Rahab, ekjon bebichari, tai dusra biya kaam kori kene thaka khan nisena mora nai, kelemane tai shanti pora jasus kori kene sipahi khan ke modot korise.
32 Me kuma zan faɗa? Ba ni da lokacin da zan ba da labari a kan Gideyon, Barak, Samson, Yefta, Dawuda, Sama’ila, da kuma annabawa,
Etu pora aru moi bisi ki kobo? Jodi moi Gideon, Barak, Samson, Jephtath, David, Samuel aru dusra bhabobadi khan laga kotha kore titia hoile homoi pora eitu khan laga sob kotha kori bole naponchibo.
33 waɗanda ta wurin bangaskiya ne suka ci nasara a kan mulkoki, suka aikata adalci, suka kuma sami abin da aka yi alkawari; waɗanda suka rurrufe bakunan zakoki,
Biswas pora taikhan rajyo to jiti loise, niyai laga kaam korise, aru asirbad paise. Taikhan bagh laga mukh bhi bondh kori dise,
34 suka kashe harshen wuta, suka kuma tsere wa kaifin takobi; waɗanda aka mai da rashin ƙarfinsu ya zama ƙarfi; waɗanda suka yi jaruntaka wajen yaƙi suka kuma fatattaki mayaƙan waɗansu ƙasashe.
jui laga takot to bhujai dise, aru talwar laga dhar pora polabole parise, bemar pora bhal hoi jaise, lorai kora homoi te takot hoi jaise, aru dusra desh laga sipahi khan ke harai dise.
35 Mata suka karɓi ƙaunatattunsu da aka sāke tasar daga matattu. Aka azabtar da yawancin mutanen nan, amma suka ƙi a sake su, domin sun tabbata za su sami lada mafi kyau sa’ad da aka tā da matattu.
Biswas pora mahila khan punoruthan pora taikhan nijor khandan morija khan paise. Kintu dusra khan ke dukh dise, taikhan ke chari dibo koi kene asha thaka nai, aru etu pora taikhan aru bhi bhal ula punoruthan pabo bhabise.
36 Waɗansu suka sha ba’a da bulala, har da dauri da sarƙa, da kuma jefa su cikin kurkuku.
Aru dusra kunba khan to ninda kori kene pitise aru luha rusi pora bandhi kene bondhi ghor te rakhidise.
37 Aka jajjefe su da duwatsu; aka raba su biyu da zarto; aka kashe su da takobi. Suka yi ta yawo saye da fatun tumaki da na awaki, suka yi zaman rashi, suka sha tsanani da kuma wulaƙanci
Kunba khan ke pathor marise, aru kati kene dui tukra korise, taikhan ke porikha korise, aru taikhan ke talwar pora morai dise. Taikhan saguli aru mer laga chamra pindhise, aru bisi gorib hoi jaise, chinta bhabona bisi hoi jaise, aru manu khan pora taikhan ke biya kori thakise.
38 duniya ba tă ma cancanci su zauna a cikinta ba. Suka yi ta yawo a cikin hamada da a kan duwatsu, da cikin kogwanni da kuma cikin ramummuka.
Etu duniya to taikhan nimite eku yogya nathaka hoi jaise. Taikhan jongol aru pahar khan te berai thakise, aru mati laga nichete jai kene thakise.
39 Waɗannan duka an yabe su saboda bangaskiyarsu, duk da haka babu waninsu da ya sami abin da aka yi alkawari.
Taikhan laga biswas nimite manu khan pora mohima dise, hoile bhi taikhan Isor laga vachan panai.
40 Allah ya shirya mana wani abu mafi kyau. Kuma bai so su kai ga maƙasudin bangaskiyarsu ba sai tare da mu.
Isor he amikhan nimite kiba ekta bhal bhabona kori kene ase, aru amikhan nathakile, taikhan sob to thik hobole na paribo.

< Ibraniyawa 11 >