< Ibraniyawa 11 >

1 Bangaskiya ita ce kasance tabbacin abin da muke bege a kai da kuma tabbatar da abin da ba mu gani ba.
Fatokisañe ty mamente o raha tamaeñeo, ty fampibentarañe o raha tsy oniñeo.
2 Abin da aka yabi kakanni na dā a kai ke nan.
Ie ty nahazoa’ o taoloo to.
3 Ta wurin bangaskiya ne muka fahimci cewa an halicci duniya bisa ga umarnin Allah, saboda an halicce abin da ake gani daga abin da ba a gani. (aiōn g165)
Fatokisañe ty ahaoniñan-tika amy Tsinaran’ Añaharey, te tsy nalaha’e amo raha oniñeo o raha miboake amo sào. (aiōn g165)
4 Ta wurin bangaskiya Habila ya miƙa wa Allah hadayar da ta fi wadda Kayinu ya miƙa. Ta wurin bangaskiya aka yabe shi cewa shi mai adalci ne, sa’ad da Allah ya yi magana mai kyau game da bayarwarsa. Ta wurin bangaskiya kuma har yanzu yana magana, ko da yake ya riga ya mutu.
Fatokisañe ty nañengà’ i Abela aman’ Añahare soroñe soa te amy Kaina, vaho nitaroñeñe te vantañe, ie nitsa­raen’ Añahare i banabana’ey, toe misaontsy re ndra te nihomake.
5 Ta wurin bangaskiya ne aka ɗauki Enok daga wannan rayuwa, ta haka bai ɗanɗana mutuwa ba; ba a kuwa same shi ba, domin Allah ya ɗauke shi. Gama kafin a ɗauke shi, an yabe shi a kan ya gamshi Allah.
Fatokisañe ty nampionjoneñe i Enoke tsy handia havilasy, ie tsy nitendreke fa rinamben’ Añahare; ie nitaroñeñe taolo’ ty nampionjonañe aze te nisohen’ Añahare.
6 In ba tare da bangaskiya ba kuwa, ba ya yiwuwa a gamshi Allah, domin duk mai zuwa wurin Allah dole yă gaskata cewa yana nan, kuma shi ne yakan sāka wa waɗanda suke nemansa da gaske.
Tsy mahafale Aze t’ie tsy amam-patokisañe. Amy te ze hañarine aman’ Añahare, tsy mete tsy matoky t’ie eo, naho manambe ty mitsoek’ aze.
7 Ta wurin bangaskiya Nuhu, sa’ad da aka yi masa gargaɗi a kan abubuwan da ba a gani ba tukuna, a cikin tsoro mai tsarki ya sassaƙa jirgi don ceton iyalinsa. Ta wurin bangaskiyarsa ya hukunta duniya ya kuma zama magājin adalcin da ake samu ta wurin bangaskiya.
Fatokisañe am-pañeveñañe ty nandranjia’ i Noe lakan-katae ty amy hatahatan’ Añaharey o raha mbe tsy rendrekeo, handrombaha’e i hasavereña’ey, ie ty namarañe ty tane bey toy, naho nampandovañe i havantañam-patokisañey.
8 Ta wurin bangaskiya ne Ibrahim, sa’ad da aka kira shi ya fita zuwa wata ƙasar da zai karɓi gādo daga baya, ya kuwa yi biyayya ya tafi, ko da yake bai san inda za shi ba.
Fatokisañe ty niantofa’ i Abra­àme, ie kinanjy hienga mb’an-tane ho ram­bese’e afara ho lova, vaho nionjoñe mb’eo tsy nahafohiñe ty hombà’e.
9 Ta wurin bangaskiya ya yi zama a ƙasar da aka yi masa alkawari kamar baƙo a baƙuwar ƙasa; ya zauna a tentuna, haka ma Ishaku da Yaƙub, waɗanda su ma magādan alkawarin nan ne tare da shi.
Fatokisañe ty nañialoa’e an-tane nampitamaeñey, hoe ambahiny, ie nimoneñe an-kivoho mindre am’ Ietsa­ke naho Iakobe, mpitrao-lova ama’e amy fampitamàñey.
10 Gama yana zuba ido ga birnin nan mai tushe, wanda mai zānen gininsa da kuma mai gininsa Allah ne.
Toe i rova reke-manantañey ty nitamà’e, i rinanjin’ Añahare naho tsinene’ey.
11 Ta wurin bangaskiya Ibrahim, ko da yake shekarunsa sun wuce, Saratu kanta kuma bakararriya ce ya iya zama mahaifi domin ya amince cewa shi wanda ya yi alkawarin mai aminci ne.
Fatokisañe ka, ty nampaozatse i Saràe hiareñe, naho nahasamak’ anake ndra te losotse o taoñe nahampela azeo, ie niantoke te migahiñe i Nampitàmay.
12 Saboda haka, daga mutum ɗaya, wanda dā shi ma da matacce kusan ɗaya ne, zuriya masu yawa suka fito kamar taurari a sararin sama da kuma kamar yashin da ba a iya ƙirgawa a bakin teku.
Aa le sinama’ i fa hihomakey, ty mira ami’ty hatozantoza’ o vasian-dikerañeo naho o faseñe añ’ olon-driake tsy lefe iaheñeo.
13 Duk mutanen nan suna cikin bangaskiya sa’ad da suka mutu. Ba su kuwa karɓi abubuwan da aka yi alkawari ba; sun dai hango su suka kuma marabce su daga nesa. Suka kuma amince cewa su baƙi ne, bare kuma a duniya.
Songa nivilasy am-patokisañe, tsy tam’ iereo o nampitamañeo; fe nioni’ iereo tsietoimoneñe añe, le nisalalaeñe, vaho niantofa’ iereo t'ie renetane, mpañialo an-tane atoy.
14 Mutane masu faɗin irin abubuwan nan sun nuna cewa suna neman ƙasar da take tasu.
Ampalangese’ o mitaroñe izaio te mitamà tanen-droae.
15 Da a ce suna tunanin ƙasar da suka bari a baya, da sun riga sun sami damar komawa.
Aa naho nimaniña’ iareo i tane niboahañey, le nalalake t'ie ho nimpoly.
16 A maimako, suna marmarin wata ƙasa mafi kyau, ta sama. Saboda haka Allah ba ya kunya a kira shi Allahnsu, domin ya riga ya shirya musu birni.
F’ie nitamà ty soa—toe i andindìñe añey. Ie amy zay, tsy mahasalatse an’ Andrianañahare ty atao Andrianañahare’ iareo vaho nihalankàña’e rova.
17 Ta wurin bangaskiya Ibrahim, sa’ad da Allah ya gwada shi, sai ya miƙa Ishaku hadaya. Shi da ya karɓi alkawaran ya yi shirin miƙa makaɗaicin ɗansa,
Fatokisañe ty nañengà’ i Abraàme t’Ietsake, ie nitsoheñe; nen­gae’ i nandrambe i fitamañeiy i bako toka’ey,
18 ko da yake Allah ya ce masa, “Ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.”
ie nanoañe ty hoe: Am’ Isaka ty hikanjiañe o tarira’oo.
19 Ibrahim ya yi tunani cewa Allah yana iya tā da matattu, a misalce kuwa, ya sāke karɓan Ishaku daga matattu.
Natokisa’e te lefen’ Añahare ty hampitroatse ty nihomake, le ao ty nandrambesa’e aze am-pandrazañañe.
20 Ta wurin bangaskiya ne Ishaku ya albarkaci Yaƙub da Isuwa game da nan gabansu.
Fatokisañe ty nitatà’ Isaka t’Iakobe naho i Esave amo raha ho avio.
21 Ta wurin bangaskiya ne Yaƙub, sa’ad da yake bakin mutuwa, ya albarkaci kowane ɗan Yusuf, ya kuma yi sujada yayinda yake jingine a kan sandansa.
Fatokisañe ty nitatà’ Iakobe fa hihomakey i ana’ Iosefe rey vaho nitalaho t’ie niato andoham-pitoño’e.
22 Ta wurin bangaskiya ne Yusuf, sa’ad da kwanakinsa suka yi kusan ƙarewa, ya yi magana game da fitowar Isra’ilawa daga Masar ya kuma ba da umarni game da ƙasusuwansa.
Fatokisañe ty nitokia’ Iosefe, ie fa hèta’ey, ty hiavota’ o nte-Israeleo vaho toe nafè’e o taola’eo.
23 Ta wurin bangaskiya ne iyayen Musa suka ɓoye shi har wata uku bayan haihuwarsa, domin sun ga cewa shi ba kamar sauran yara ba ne, ba su kuwa ji tsoron umarnin sarki ba.
Fatokisañe ty nañetahan-droae’ i Mosè aze te nitoly, naho nioni’ iareo t’ie ajaja soa, vaho tsy nahahembañe iareo ty nafè’ i mpanjakay.
24 Ta wurin bangaskiya ne Musa, sa’ad da ya yi girma, ya ƙi a kira shi ɗan diyar Fir’auna.
Fatokisañe ty nifoneña’ i Mosè tsy hatao ana’ ty anak’ ampela’ i Farao, ie fa niañoñ’ay,
25 Ya zaɓa yă sha wahala tare da mutanen Allah, maimakon yă ji daɗin sha’awace-sha’awacen zunubi na ɗan lokaci.
te mone jinobo’e ty hifeake fampisoañañe mindre am’ondatin’ Añahareo, ta t’ie hanañ’andro hieranerañe an-kakeo;
26 Ya ɗauki wulaƙancin da yake sha saboda Kiristi ya fi dukiyar Masar daraja, domin ya sa ido ga ladansa.
natao’e te vara mandikoatse ty harea’ i Egipte ty ìnje’ i Norizañey, amy te nitalakese’e i tambe’ey.
27 Ta wurin bangaskiya ya bar Masar, ba tare da jin tsoron fushin sarki ba; ya kuwa jure domin ya ga wannan wanda ba a iya gani.
Fatokisañe ty niengà’e i Egipte, tsy nihembaña’e ty haviñera’ i mpanjakay; fe nifeake hoe te niisa’e i tsy isakey.
28 Ta wurin bangaskiya ya kiyaye Bikin Ƙetarewa ya kuma yayyafa jini, domin kada mai hallakar’ya’yan fari yă taɓa’ya’yan fari na Isra’ila.
Fatokisañe ty nahahenefa’e i Fihelañey, naho i fitse-lioy, tsy hipaoha’ i mpanjaman-tañoloñolòñañey iareo.
29 Ta wurin bangaskiya ne mutane suka bi ta cikin Jan Teku, sai ka ce a kan busasshiyar ƙasa; amma da Masarawa suka yi ƙoƙari su yi haka, sai aka nutsar da su.
Fatokisañe ty nitoaña’ iareo i Riake Menay hoe an-tane maike, fe nagedra’e o nte Egipte nahavany nisoroke ama'eo.
30 Ta wurin bangaskiya ne katangar Yeriko ta rushe, bayan mutane suka yi ta kewaye ta har kwana bakwai.
Fatokisañe ty nampiforetrake o kijoli’ i Jerikòo, ie niariaria’ iareo fito andro.
31 Ta wurin bangaskiya ne ba a kashe Rahab karuwan nan, ta tare da marasa biyayya ba don ta marabci’yan leƙan asiri.
Fatokisañe ty tsy nitraofa’ i Rahaba karapilo fivetrak’ amo nanjehatseo ie nandrambe i mpifilo rey am-panintsiñañe.
32 Me kuma zan faɗa? Ba ni da lokacin da zan ba da labari a kan Gideyon, Barak, Samson, Yefta, Dawuda, Sama’ila, da kuma annabawa,
Aa inon-ka ty hataliliko? Fa hilesa ty andro naho taroñeko i Gideona naho i Baraka naho i Samsone naho i Jefta, i Davide ka, naho i Samoela vaho o mpitokio,
33 waɗanda ta wurin bangaskiya ne suka ci nasara a kan mulkoki, suka aikata adalci, suka kuma sami abin da aka yi alkawari; waɗanda suka rurrufe bakunan zakoki,
ie am-patokisañe ro nampiambane fifeheañe, nitolon-kavantañañe, nahazo fampitamàñe, nampitsiteke ty vavan-diona,
34 suka kashe harshen wuta, suka kuma tsere wa kaifin takobi; waɗanda aka mai da rashin ƙarfinsu ya zama ƙarfi; waɗanda suka yi jaruntaka wajen yaƙi suka kuma fatattaki mayaƙan waɗansu ƙasashe.
namono ty afo nisotratràke, nibolititse ami’ty lelam-pibara, ni-haozareñe te naifo­ifo, nifanalolahy añ’aly vaho nampitriban-day o lahin-defon’ ambahinio.
35 Mata suka karɓi ƙaunatattunsu da aka sāke tasar daga matattu. Aka azabtar da yawancin mutanen nan, amma suka ƙi a sake su, domin sun tabbata za su sami lada mafi kyau sa’ad da aka tā da matattu.
Rinambe’ o rakembao o vilasi’ iareoo te vinañon-ko veloñe; nisamporeraheñe ty ila’e nitoky tsy hahañe, handrambesa’ iareo ty fitroarañe soa,
36 Waɗansu suka sha ba’a da bulala, har da dauri da sarƙa, da kuma jefa su cikin kurkuku.
nitsoehem-pañinjeañe naho firiso ty ila’e, mbore vinahotse vaho najo am-pandrohizañe ao.
37 Aka jajjefe su da duwatsu; aka raba su biyu da zarto; aka kashe su da takobi. Suka yi ta yawo saye da fatun tumaki da na awaki, suka yi zaman rashi, suka sha tsanani da kuma wulaƙanci
Finetsa-bato iereo, linily lasý, nizizieñe, vinono am-pibara, nirere­rere an-kolits’ añondry naho holits’ ose, nibangý, niforekekèñe, nivolevolèñe—
38 duniya ba tă ma cancanci su zauna a cikinta ba. Suka yi ta yawo a cikin hamada da a kan duwatsu, da cikin kogwanni da kuma cikin ramummuka.
tsy nañeva iareo ty voatse toy—nisariosario an-dratraratra añe naho am-bohitse ao naho an-dakato vaho an-kobo’ ty tane toy ao.
39 Waɗannan duka an yabe su saboda bangaskiyarsu, duk da haka babu waninsu da ya sami abin da aka yi alkawari.
Ie iaby rezay, niventem-patokisañe, fe tsy nandrambe i nampitamaeñey.
40 Allah ya shirya mana wani abu mafi kyau. Kuma bai so su kai ga maƙasudin bangaskiyarsu ba sai tare da mu.
Amy te lombolombon-kasoa ty natolon’ Añahare aman-tika, te tsy ho fonireñe iereo naho tsy itika.

< Ibraniyawa 11 >