< Ibraniyawa 11 >

1 Bangaskiya ita ce kasance tabbacin abin da muke bege a kai da kuma tabbatar da abin da ba mu gani ba.
It is because people trust [God] that they are sure that they will receive the things that they confidently expect [God to give them]. They are also certain [that they will see those things], though no one sees them yet.
2 Abin da aka yabi kakanni na dā a kai ke nan.
It was because our ancestors trusted in God that they pleased him.
3 Ta wurin bangaskiya ne muka fahimci cewa an halicci duniya bisa ga umarnin Allah, saboda an halicce abin da ake gani daga abin da ba a gani. (aiōn g165)
It is because we trust in God that we understand that he formed the universe by commanding [it to exist]. The result is that the things that we see were not made from things that already existed. (aiōn g165)
4 Ta wurin bangaskiya Habila ya miƙa wa Allah hadayar da ta fi wadda Kayinu ya miƙa. Ta wurin bangaskiya aka yabe shi cewa shi mai adalci ne, sa’ad da Allah ya yi magana mai kyau game da bayarwarsa. Ta wurin bangaskiya kuma har yanzu yana magana, ko da yake ya riga ya mutu.
It was because [Adam’s son] Abel trusted God that he sacrificed something better to God than what [his older brother] Cain offered to God. Because Abel did that, when God spoke well about what Abel sacrificed, God declared that Abel was righteous. And although Abel is dead, we still learn from him [about trusting God].
5 Ta wurin bangaskiya ne aka ɗauki Enok daga wannan rayuwa, ta haka bai ɗanɗana mutuwa ba; ba a kuwa same shi ba, domin Allah ya ɗauke shi. Gama kafin a ɗauke shi, an yabe shi a kan ya gamshi Allah.
It was because Enoch believed [God that God] took him [up to heaven]. The result was that he did not die. No one found him, because he was taken up {[God] had removed him} from the earth [to heaven]. Before [God] took him away, [he] testified that Enoch pleased him well.
6 In ba tare da bangaskiya ba kuwa, ba ya yiwuwa a gamshi Allah, domin duk mai zuwa wurin Allah dole yă gaskata cewa yana nan, kuma shi ne yakan sāka wa waɗanda suke nemansa da gaske.
It is possible for people to please God only if they trust God, because anyone who wants to come to God must first believe that God exists and that he rewards those who seek [to know] him.
7 Ta wurin bangaskiya Nuhu, sa’ad da aka yi masa gargaɗi a kan abubuwan da ba a gani ba tukuna, a cikin tsoro mai tsarki ya sassaƙa jirgi don ceton iyalinsa. Ta wurin bangaskiyarsa ya hukunta duniya ya kuma zama magājin adalcin da ake samu ta wurin bangaskiya.
It was because Noah trusted [God] that after he was warned by God {after [God] warned him} about [a flood that] had not yet happened, Noah [showed that he] revered God by building a huge ship to save his family. By doing that, he [showed all the people who did not believe him] [MTY] [that they deserved to be condemned] {[that God would] condemn them}. He was someone whom God declared to be righteous because of his trusting in God.
8 Ta wurin bangaskiya ne Ibrahim, sa’ad da aka kira shi ya fita zuwa wata ƙasar da zai karɓi gādo daga baya, ya kuwa yi biyayya ya tafi, ko da yake bai san inda za shi ba.
It was because Abraham trusted God that when he was told to go {when [God] told him to go}, he obeyed [God], he left [his own country], and went to a place that God would give him. Abraham left his own country, even though he did not know where he would be going.
9 Ta wurin bangaskiya ya yi zama a ƙasar da aka yi masa alkawari kamar baƙo a baƙuwar ƙasa; ya zauna a tentuna, haka ma Ishaku da Yaƙub, waɗanda su ma magādan alkawarin nan ne tare da shi.
It was because Abraham trusted God that he lived as though he was a foreigner in the land that [God] had promised to him. Abraham lived in tents, and his son Isaac and his grandson Jacob did also. God promised to give to Isaac and Jacob the same things that he promised to give Abraham.
10 Gama yana zuba ido ga birnin nan mai tushe, wanda mai zānen gininsa da kuma mai gininsa Allah ne.
Abraham was waiting to live in a city [in heaven] that would exist forever [MET]. It was a city that God is building [DOU].
11 Ta wurin bangaskiya Ibrahim, ko da yake shekarunsa sun wuce, Saratu kanta kuma bakararriya ce ya iya zama mahaifi domin ya amince cewa shi wanda ya yi alkawarin mai aminci ne.
It was because Abraham trusted God that God gave Abraham strength so that he [was] able to produce a son. Even though his wife Sarah was past the age [when women bear children], [God] promised [that he would give her a son], and Abraham considered that God would do what he promised to do.
12 Saboda haka, daga mutum ɗaya, wanda dā shi ma da matacce kusan ɗaya ne, zuriya masu yawa suka fito kamar taurari a sararin sama da kuma kamar yashin da ba a iya ƙirgawa a bakin teku.
So, although Abraham was also too old to have children, so many people descended from that one man that they were as numerous as the stars in the sky and are as countless as the grains of sand along the seashore, [just like God promised him].
13 Duk mutanen nan suna cikin bangaskiya sa’ad da suka mutu. Ba su kuwa karɓi abubuwan da aka yi alkawari ba; sun dai hango su suka kuma marabce su daga nesa. Suka kuma amince cewa su baƙi ne, bare kuma a duniya.
It was while they still trusted in God that all those people died. Even though they had not yet received the things that God had promised to give them, [it was as though] they saw those things in a distance. They were glad [to know] about what God promised. It was as though they admitted that they were not from this earth, but that they were only here temporarily.
14 Mutane masu faɗin irin abubuwan nan sun nuna cewa suna neman ƙasar da take tasu.
As for those people who talk like that, they clearly show that they long for [a place that will become] their true native land.
15 Da a ce suna tunanin ƙasar da suka bari a baya, da sun riga sun sami damar komawa.
If they had been thinking about [that place being] the place from which they had come, they would have taken the opportunity to return there.
16 A maimako, suna marmarin wata ƙasa mafi kyau, ta sama. Saboda haka Allah ba ya kunya a kira shi Allahnsu, domin ya riga ya shirya musu birni.
But, instead, they desired a better [place in which to live]; that is, they desired [a home] in heaven. So God has prepared a city for them to live [with him], and he is pleased [LIT] for them to say that he is their God.
17 Ta wurin bangaskiya Ibrahim, sa’ad da Allah ya gwada shi, sai ya miƙa Ishaku hadaya. Shi da ya karɓi alkawaran ya yi shirin miƙa makaɗaicin ɗansa,
It was because Abraham trusted [God] that he [was ready to] kill his son Isaac as a sacrifice when [God] tested him. This same man to whom [God] promised [to give] ([a son/many descendants]) was going to sacrifice [that same son], the only son [whom his own wife had borne]!
18 ko da yake Allah ya ce masa, “Ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.”
It was to Abraham that God said, “It is [only] from Isaac that I will consider your family to descend.”
19 Ibrahim ya yi tunani cewa Allah yana iya tā da matattu, a misalce kuwa, ya sāke karɓan Ishaku daga matattu.
Abraham considered that [to fulfill that promise], God could make [Isaac] live again [even if] he had died [after Abraham sacrificed him]! The result was that when Abraham did receive Isaac back [after God told him not to harm Isaac], it was as though he received him back even after he died.
20 Ta wurin bangaskiya ne Ishaku ya albarkaci Yaƙub da Isuwa game da nan gabansu.
It was because Isaac trusted God that he [prayed that after he died, God would] bless [his] sons Jacob and Esau.
21 Ta wurin bangaskiya ne Yaƙub, sa’ad da yake bakin mutuwa, ya albarkaci kowane ɗan Yusuf, ya kuma yi sujada yayinda yake jingine a kan sandansa.
It was because Jacob trusted God that, as he was dying, he [prayed that God would] bless each of the sons of [his own son Joseph]. He worshipped God as he leaned upon his walking stick [before he died].
22 Ta wurin bangaskiya ne Yusuf, sa’ad da kwanakinsa suka yi kusan ƙarewa, ya yi magana game da fitowar Isra’ilawa daga Masar ya kuma ba da umarni game da ƙasusuwansa.
It was because Joseph trusted God that, when he was about to die [in Egypt], he anticipated the time when the Israelis would leave Egypt; and he instructed [that] his people [should carry] his bones [with them when they] ([left Egypt/returned to Canaan]).
23 Ta wurin bangaskiya ne iyayen Musa suka ɓoye shi har wata uku bayan haihuwarsa, domin sun ga cewa shi ba kamar sauran yara ba ne, ba su kuwa ji tsoron umarnin sarki ba.
It was because Moses’ father and mother trusted God that they hid [their son] for three months shortly after he was born, because they saw that he was so beautiful. They were not afraid of [disobeying] what the king of Egypt had commanded, [namely, that all the Jewish male babies must be killed].
24 Ta wurin bangaskiya ne Musa, sa’ad da ya yi girma, ya ƙi a kira shi ɗan diyar Fir’auna.
The daughter of the [king, whom they called] Pharaoh, [raised] Moses, but when he had grown up, it was because he trusted God that he refused to [accept the privileges that would have been his if people] considered that he was (the son of the king’s daughter/the king’s own grandson).
25 Ya zaɓa yă sha wahala tare da mutanen Allah, maimakon yă ji daɗin sha’awace-sha’awacen zunubi na ɗan lokaci.
He decided that it was better for others to mistreat him for a time along with the Israeli people, than to temporarily enjoy living sinfully [in the King’s palace].
26 Ya ɗauki wulaƙancin da yake sha saboda Kiristi ya fi dukiyar Masar daraja, domin ya sa ido ga ladansa.
This is because he decided that if he suffered for the Messiah, it would be worth far more [in God’s sight] than his owning all the treasures of Egypt [that he would receive as Pharaoh’s heir. He decided that] because he looked forward to the time when [God would give him] an [eternal] reward.
27 Ta wurin bangaskiya ya bar Masar, ba tare da jin tsoron fushin sarki ba; ya kuwa jure domin ya ga wannan wanda ba a iya gani.
It was because he trusted God that he left Egypt. He was not afraid that the king would be angry [because of his doing that]. He (kept going/did not turn back) because [it was as though] he kept seeing [God], whom no one can see.
28 Ta wurin bangaskiya ya kiyaye Bikin Ƙetarewa ya kuma yayyafa jini, domin kada mai hallakar’ya’yan fari yă taɓa’ya’yan fari na Isra’ila.
It was because Moses believed [that God would save his own people] that he instituted the [festival called] Passover. He did that [by commanding that the people should kill lambs and] sprinkle their blood [on their] doorposts. They did that in order that [the angel who] causes people to die would not kill [EUP] the oldest male Israelites [when he killed the oldest sons in each Egyptian family].
29 Ta wurin bangaskiya ne mutane suka bi ta cikin Jan Teku, sai ka ce a kan busasshiyar ƙasa; amma da Masarawa suka yi ƙoƙari su yi haka, sai aka nutsar da su.
It was because they trusted God that [when] the [Israelite] people walked through [where] the Red Sea [had been, it was] as [though they walked] on dry land! But, when the [army of] Egypt also attempted to [cross that same water], they drowned, because [the sea came back and flooded them]!
30 Ta wurin bangaskiya ne katangar Yeriko ta rushe, bayan mutane suka yi ta kewaye ta har kwana bakwai.
It was because the [Israeli] people trusted God that the walls around Jericho [city] collapsed, after the Israelis marched around the walls for seven days.
31 Ta wurin bangaskiya ne ba a kashe Rahab karuwan nan, ta tare da marasa biyayya ba don ta marabci’yan leƙan asiri.
Rahab [had been] a prostitute, but because she trusted God, she did not perish with those [inside Jericho] who disobeyed [God. Joshua sent some spies] into the city [in order] to find ways to destroy it, but God saved her because she welcomed those spies [peaceably].
32 Me kuma zan faɗa? Ba ni da lokacin da zan ba da labari a kan Gideyon, Barak, Samson, Yefta, Dawuda, Sama’ila, da kuma annabawa,
I do not know what more I should say [RHQ] [about others who trusted in God]. It would take too much time to tell about Gideon, Barak, Samson, Jephthah, David, Samuel, and the [other] prophets.
33 waɗanda ta wurin bangaskiya ne suka ci nasara a kan mulkoki, suka aikata adalci, suka kuma sami abin da aka yi alkawari; waɗanda suka rurrufe bakunan zakoki,
It was because they trusted God that some of them [did great things for him]. Some conquered lands ruled by powerful men. Some ruled [Israel] and justly [punished those men and nations who rebelled against God]. Some obtained [from God] the things that he promised to give them [MTY].
34 suka kashe harshen wuta, suka kuma tsere wa kaifin takobi; waɗanda aka mai da rashin ƙarfinsu ya zama ƙarfi; waɗanda suka yi jaruntaka wajen yaƙi suka kuma fatattaki mayaƙan waɗansu ƙasashe.
Some forced lions to keep their mouths shut. Some escaped from being destroyed by fire. Some of those people escaped from [being killed with] a sword [MTY]. Some of those [people who trusted God] were made strong {became mighty} again after they had once been weak. Some became powerful when they fought wars. Some caused armies [that came from foreign lands] to run away from them.
35 Mata suka karɓi ƙaunatattunsu da aka sāke tasar daga matattu. Aka azabtar da yawancin mutanen nan, amma suka ƙi a sake su, domin sun tabbata za su sami lada mafi kyau sa’ad da aka tā da matattu.
Some women [who trusted God] received [their relatives] back again when [God] ([made them live again after they had died/raised them from the dead]). But [others who trusted God] were tortured until they died. They were tortured because they refused to agree when [their captors said, “We will] release you [if you deny that you believe in God.” They refused to do that], because they wanted to live with God forever, which is better than [continuing to live on earth] after having almost died.
36 Waɗansu suka sha ba’a da bulala, har da dauri da sarƙa, da kuma jefa su cikin kurkuku.
Other [people who trusted God] were mocked; [some had their backs] cut [open by being struck] with leaded whips. Some were chained and put in prison.
37 Aka jajjefe su da duwatsu; aka raba su biyu da zarto; aka kashe su da takobi. Suka yi ta yawo saye da fatun tumaki da na awaki, suka yi zaman rashi, suka sha tsanani da kuma wulaƙanci
[Some of] those believers were stoned to death {People [killed some of those believers by] throwing stones at them}. Others were cut completely in two. Others were killed with swords. Others of these people who trusted God wandered around the land [wearing garments made only of] skins from sheep and goats. They did not have any money. They were continually oppressed and tormented {People continuously oppressed them and tormented them}.
38 duniya ba tă ma cancanci su zauna a cikinta ba. Suka yi ta yawo a cikin hamada da a kan duwatsu, da cikin kogwanni da kuma cikin ramummuka.
[The people on earth who caused those who trusted in God to suffer were so bad that] they did not deserve [to live with people who trusted God. Some who trusted God] wandered in deserts and on mountains. Some lived in caves and in other [large] holes in the ground.
39 Waɗannan duka an yabe su saboda bangaskiyarsu, duk da haka babu waninsu da ya sami abin da aka yi alkawari.
Although all these people were commended [by God] {[God] commended all these people} because they trusted him, God did not give them all that he promised them [while they were alive].
40 Allah ya shirya mana wani abu mafi kyau. Kuma bai so su kai ga maƙasudin bangaskiyarsu ba sai tare da mu.
God knew ahead of time that what he would give us and them [later] would be better than giving [them immediately what he promised]. What God intends is that only when they and we are together will we have all that God intends us to have.

< Ibraniyawa 11 >