< Ibraniyawa 11 >
1 Bangaskiya ita ce kasance tabbacin abin da muke bege a kai da kuma tabbatar da abin da ba mu gani ba.
Now, faith is the confidence of things hoped for, and the conviction of things not seen.
2 Abin da aka yabi kakanni na dā a kai ke nan.
By this, the ancients obtained reputation.
3 Ta wurin bangaskiya ne muka fahimci cewa an halicci duniya bisa ga umarnin Allah, saboda an halicce abin da ake gani daga abin da ba a gani. (aiōn )
By faith, we understand that the worlds were formed by the word of God; so that the things which were seen, were not made of things which do appear. (aiōn )
4 Ta wurin bangaskiya Habila ya miƙa wa Allah hadayar da ta fi wadda Kayinu ya miƙa. Ta wurin bangaskiya aka yabe shi cewa shi mai adalci ne, sa’ad da Allah ya yi magana mai kyau game da bayarwarsa. Ta wurin bangaskiya kuma har yanzu yana magana, ko da yake ya riga ya mutu.
By faith Abel offered to God a better sacrifice than Cain, on account of which he was commended as righteous; God testifying in favor of his oblations: and so, by it, though dead he still speaks.
5 Ta wurin bangaskiya ne aka ɗauki Enok daga wannan rayuwa, ta haka bai ɗanɗana mutuwa ba; ba a kuwa same shi ba, domin Allah ya ɗauke shi. Gama kafin a ɗauke shi, an yabe shi a kan ya gamshi Allah.
By faith Enoch was translated, that he might not see death, and was not found, because God had translated him; for, before his translation, it was testified that he pleased God.
6 In ba tare da bangaskiya ba kuwa, ba ya yiwuwa a gamshi Allah, domin duk mai zuwa wurin Allah dole yă gaskata cewa yana nan, kuma shi ne yakan sāka wa waɗanda suke nemansa da gaske.
But without faith it is impossible to please God. For he who comes to God, must believe that he is, and that he is a rewarder of them who diligently seek him.
7 Ta wurin bangaskiya Nuhu, sa’ad da aka yi masa gargaɗi a kan abubuwan da ba a gani ba tukuna, a cikin tsoro mai tsarki ya sassaƙa jirgi don ceton iyalinsa. Ta wurin bangaskiyarsa ya hukunta duniya ya kuma zama magājin adalcin da ake samu ta wurin bangaskiya.
By faith, Noah, when he received a revelation concerning things not yet seen, being seized with religious fear, prepared an ark for the salvation of his family; by which he condemned the world, and became an heir of the righteousness which is by faith.
8 Ta wurin bangaskiya ne Ibrahim, sa’ad da aka kira shi ya fita zuwa wata ƙasar da zai karɓi gādo daga baya, ya kuwa yi biyayya ya tafi, ko da yake bai san inda za shi ba.
By faith, Abraham, when called to go out into a place which he should afterward receive as an inheritance, obeyed, and went out, not knowing whither he was going.
9 Ta wurin bangaskiya ya yi zama a ƙasar da aka yi masa alkawari kamar baƙo a baƙuwar ƙasa; ya zauna a tentuna, haka ma Ishaku da Yaƙub, waɗanda su ma magādan alkawarin nan ne tare da shi.
By faith, he sojourned in the land of promise, as in a foreign land, dwelling in tents with Isaac and Jacob, the joint heirs of the same promise:
10 Gama yana zuba ido ga birnin nan mai tushe, wanda mai zānen gininsa da kuma mai gininsa Allah ne.
for he expected the city having foundations, whose builder and maker is God.
11 Ta wurin bangaskiya Ibrahim, ko da yake shekarunsa sun wuce, Saratu kanta kuma bakararriya ce ya iya zama mahaifi domin ya amince cewa shi wanda ya yi alkawarin mai aminci ne.
By faith, also, Sarah herself received strength for the conception of seed, and brought forth, when past the time of life; because she judged him faithful who had promised.
12 Saboda haka, daga mutum ɗaya, wanda dā shi ma da matacce kusan ɗaya ne, zuriya masu yawa suka fito kamar taurari a sararin sama da kuma kamar yashin da ba a iya ƙirgawa a bakin teku.
And, therefore, there sprang from one who was dead, in this respect, a race, as the stars of heaven in multitude, and as the sand, which is on the sea-shore, innumerable.
13 Duk mutanen nan suna cikin bangaskiya sa’ad da suka mutu. Ba su kuwa karɓi abubuwan da aka yi alkawari ba; sun dai hango su suka kuma marabce su daga nesa. Suka kuma amince cewa su baƙi ne, bare kuma a duniya.
All these died in faith, not having received the promises. For, seeing the things promised, afar off, and embracing them, they confessed that they were strangers and pilgrims in the land.
14 Mutane masu faɗin irin abubuwan nan sun nuna cewa suna neman ƙasar da take tasu.
Now they who speak such things, plainly declare that they earnestly seek a country.
15 Da a ce suna tunanin ƙasar da suka bari a baya, da sun riga sun sami damar komawa.
For truly, if they had remembered that from which they came out, they might have had an opportunity to return it.
16 A maimako, suna marmarin wata ƙasa mafi kyau, ta sama. Saboda haka Allah ba ya kunya a kira shi Allahnsu, domin ya riga ya shirya musu birni.
But, indeed, they strongly desired a better country; that is, a heavenly. Therefore, God is not ashamed of them--to be called their God; because he has prepared for them a city.
17 Ta wurin bangaskiya Ibrahim, sa’ad da Allah ya gwada shi, sai ya miƙa Ishaku hadaya. Shi da ya karɓi alkawaran ya yi shirin miƙa makaɗaicin ɗansa,
By faith, Abraham, when tried, offered up Isaac; he who had received the promises offered up his only begotten,
18 ko da yake Allah ya ce masa, “Ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.”
concerning whom it was said, that "In Isaac shall thy seed be called";
19 Ibrahim ya yi tunani cewa Allah yana iya tā da matattu, a misalce kuwa, ya sāke karɓan Ishaku daga matattu.
reasoning that God was able to raise him even from the dead; from whence, indeed, he received him in a figure.
20 Ta wurin bangaskiya ne Ishaku ya albarkaci Yaƙub da Isuwa game da nan gabansu.
By faith, Isaac blessed Jacob and Esau, with respect to things to come.
21 Ta wurin bangaskiya ne Yaƙub, sa’ad da yake bakin mutuwa, ya albarkaci kowane ɗan Yusuf, ya kuma yi sujada yayinda yake jingine a kan sandansa.
By faith, Jacob, when dying, blessed each of the sons of Joseph, and worshiped, bowing on the top of his staff.
22 Ta wurin bangaskiya ne Yusuf, sa’ad da kwanakinsa suka yi kusan ƙarewa, ya yi magana game da fitowar Isra’ilawa daga Masar ya kuma ba da umarni game da ƙasusuwansa.
By faith, Joseph, when dying, made mention concerning the departing of the children of Israel, and gave commandment concerning his bones.
23 Ta wurin bangaskiya ne iyayen Musa suka ɓoye shi har wata uku bayan haihuwarsa, domin sun ga cewa shi ba kamar sauran yara ba ne, ba su kuwa ji tsoron umarnin sarki ba.
By faith, Moses, when born, was hid three months by his parents, because they saw that he was a beautiful child, and were not afraid of the king's commandment.
24 Ta wurin bangaskiya ne Musa, sa’ad da ya yi girma, ya ƙi a kira shi ɗan diyar Fir’auna.
By faith, Moses, when he was grown up, refused to be called the son of Pharaoh's daughter;
25 Ya zaɓa yă sha wahala tare da mutanen Allah, maimakon yă ji daɗin sha’awace-sha’awacen zunubi na ɗan lokaci.
choosing rather to suffer evil with the people of God, than to have the temporary fruition of sin,
26 Ya ɗauki wulaƙancin da yake sha saboda Kiristi ya fi dukiyar Masar daraja, domin ya sa ido ga ladansa.
esteeming the reproach of Christ greater riches than the treasures of Egypt; for he looked forward to the retribution.
27 Ta wurin bangaskiya ya bar Masar, ba tare da jin tsoron fushin sarki ba; ya kuwa jure domin ya ga wannan wanda ba a iya gani.
By faith, he left Egypt, not being afraid of the wrath of the king. For he courageously persevered, as perceiving the invisible God.
28 Ta wurin bangaskiya ya kiyaye Bikin Ƙetarewa ya kuma yayyafa jini, domin kada mai hallakar’ya’yan fari yă taɓa’ya’yan fari na Isra’ila.
By faith, he appointed the passover, and the sprinkling of the blood; that he who destroyed the first-born, might not touch them.
29 Ta wurin bangaskiya ne mutane suka bi ta cikin Jan Teku, sai ka ce a kan busasshiyar ƙasa; amma da Masarawa suka yi ƙoƙari su yi haka, sai aka nutsar da su.
By faith, they passed through the Red Sea, as by dry land, which the Egyptians attempting to do, were drowned.
30 Ta wurin bangaskiya ne katangar Yeriko ta rushe, bayan mutane suka yi ta kewaye ta har kwana bakwai.
By faith, the walls of Jericho fell down, having been encompassed seven days.
31 Ta wurin bangaskiya ne ba a kashe Rahab karuwan nan, ta tare da marasa biyayya ba don ta marabci’yan leƙan asiri.
By faith, Rahab, the harlot, was not destroyed with the unbelievers, having received the spies in peace.
32 Me kuma zan faɗa? Ba ni da lokacin da zan ba da labari a kan Gideyon, Barak, Samson, Yefta, Dawuda, Sama’ila, da kuma annabawa,
And what shall I say more? for the time would fail me, to speak of Gideon, and Barak, and Samson, and Jepthah, and David, also, and Samuel, and the prophets--
33 waɗanda ta wurin bangaskiya ne suka ci nasara a kan mulkoki, suka aikata adalci, suka kuma sami abin da aka yi alkawari; waɗanda suka rurrufe bakunan zakoki,
who, through faith, subdued kingdom, wrought righteousness, obtained promises, stopped the mouths of lions,
34 suka kashe harshen wuta, suka kuma tsere wa kaifin takobi; waɗanda aka mai da rashin ƙarfinsu ya zama ƙarfi; waɗanda suka yi jaruntaka wajen yaƙi suka kuma fatattaki mayaƙan waɗansu ƙasashe.
quenched the strength of fire, escaped the edges of the sword, grew strong from sickness, became valiant in battle, overturned the camps of the aliens.
35 Mata suka karɓi ƙaunatattunsu da aka sāke tasar daga matattu. Aka azabtar da yawancin mutanen nan, amma suka ƙi a sake su, domin sun tabbata za su sami lada mafi kyau sa’ad da aka tā da matattu.
Women received their dead by a resurrection, and others were tortured, not accepting deliverance, that they might obtain a better resurrection.
36 Waɗansu suka sha ba’a da bulala, har da dauri da sarƙa, da kuma jefa su cikin kurkuku.
And others had trial of mockings and scourgings; and, moreover of bonds and imprisonment.
37 Aka jajjefe su da duwatsu; aka raba su biyu da zarto; aka kashe su da takobi. Suka yi ta yawo saye da fatun tumaki da na awaki, suka yi zaman rashi, suka sha tsanani da kuma wulaƙanci
They were stoned, they were sawn asunder, they were tempted, they died by the slaughter of the sword, they went about in sheep skins, and in goat skins, being destitute, afflicted, maltreated;
38 duniya ba tă ma cancanci su zauna a cikinta ba. Suka yi ta yawo a cikin hamada da a kan duwatsu, da cikin kogwanni da kuma cikin ramummuka.
of these the world was not worthy: they wandered in deserts, and mountains, and in caves, and holes of the earth.
39 Waɗannan duka an yabe su saboda bangaskiyarsu, duk da haka babu waninsu da ya sami abin da aka yi alkawari.
Now, all these, though commanded on account of faith, did not receive the promise,
40 Allah ya shirya mana wani abu mafi kyau. Kuma bai so su kai ga maƙasudin bangaskiyarsu ba sai tare da mu.
God having provided something better for us, that they, without us, should not be made perfect.