< Ibraniyawa 11 >

1 Bangaskiya ita ce kasance tabbacin abin da muke bege a kai da kuma tabbatar da abin da ba mu gani ba.
Now faith is a realization of things being hoped for, an evidence of things not seen.
2 Abin da aka yabi kakanni na dā a kai ke nan.
By it the ancients were approved.
3 Ta wurin bangaskiya ne muka fahimci cewa an halicci duniya bisa ga umarnin Allah, saboda an halicce abin da ake gani daga abin da ba a gani. (aiōn g165)
By faith we understand that the ages were created by a word from God, so that the things that are seen were made out of things invisible. (aiōn g165)
4 Ta wurin bangaskiya Habila ya miƙa wa Allah hadayar da ta fi wadda Kayinu ya miƙa. Ta wurin bangaskiya aka yabe shi cewa shi mai adalci ne, sa’ad da Allah ya yi magana mai kyau game da bayarwarsa. Ta wurin bangaskiya kuma har yanzu yana magana, ko da yake ya riga ya mutu.
By faith Abel offered to God a better sacrifice than did Cain, through which he obtained witness that he was righteous, God testifying concerning his gifts; and by means of it he still speaks, even though being dead.
5 Ta wurin bangaskiya ne aka ɗauki Enok daga wannan rayuwa, ta haka bai ɗanɗana mutuwa ba; ba a kuwa same shi ba, domin Allah ya ɗauke shi. Gama kafin a ɗauke shi, an yabe shi a kan ya gamshi Allah.
By faith Enoch was transferred so as not to see death, and could not be found because God had translated him; before his translation he had obtained witness that he was pleasing to God.
6 In ba tare da bangaskiya ba kuwa, ba ya yiwuwa a gamshi Allah, domin duk mai zuwa wurin Allah dole yă gaskata cewa yana nan, kuma shi ne yakan sāka wa waɗanda suke nemansa da gaske.
Now without faith it is impossible to please Him, because the one approaching God must believe that He exists and that He becomes a rewarder of those who earnestly seek Him.
7 Ta wurin bangaskiya Nuhu, sa’ad da aka yi masa gargaɗi a kan abubuwan da ba a gani ba tukuna, a cikin tsoro mai tsarki ya sassaƙa jirgi don ceton iyalinsa. Ta wurin bangaskiyarsa ya hukunta duniya ya kuma zama magājin adalcin da ake samu ta wurin bangaskiya.
By faith Noah, being divinely warned of things not yet seen, moved with godly fear, prepared an ark for the salvation of his household, by which he condemned the world and became an heir of the righteousness that is according to faith.
8 Ta wurin bangaskiya ne Ibrahim, sa’ad da aka kira shi ya fita zuwa wata ƙasar da zai karɓi gādo daga baya, ya kuwa yi biyayya ya tafi, ko da yake bai san inda za shi ba.
By faith Abraham, upon being called to go forth to the place that he would receive as an inheritance, obeyed and went, though not being acquainted with where he was going.
9 Ta wurin bangaskiya ya yi zama a ƙasar da aka yi masa alkawari kamar baƙo a baƙuwar ƙasa; ya zauna a tentuna, haka ma Ishaku da Yaƙub, waɗanda su ma magādan alkawarin nan ne tare da shi.
By faith he migrated into the land of promise as into a foreign country, dwelling in tents, along with Isaac and Jacob, the fellow heirs of the same promise;
10 Gama yana zuba ido ga birnin nan mai tushe, wanda mai zānen gininsa da kuma mai gininsa Allah ne.
for he was waiting expectantly for the city with the real foundations, whose designer and builder is God.
11 Ta wurin bangaskiya Ibrahim, ko da yake shekarunsa sun wuce, Saratu kanta kuma bakararriya ce ya iya zama mahaifi domin ya amince cewa shi wanda ya yi alkawarin mai aminci ne.
By faith Sarah herself also received power to conceive seed, and she bore a child when she was past the normal age, since she judged Him faithful who had promised.
12 Saboda haka, daga mutum ɗaya, wanda dā shi ma da matacce kusan ɗaya ne, zuriya masu yawa suka fito kamar taurari a sararin sama da kuma kamar yashin da ba a iya ƙirgawa a bakin teku.
And so from one man, actually an impotent, were begotten descendants as numerous as the stars in the sky, and as countless as the sand on the seashore.
13 Duk mutanen nan suna cikin bangaskiya sa’ad da suka mutu. Ba su kuwa karɓi abubuwan da aka yi alkawari ba; sun dai hango su suka kuma marabce su daga nesa. Suka kuma amince cewa su baƙi ne, bare kuma a duniya.
These all died believing—not having received the promises, but having seen and welcomed them from a distance, thus confessing that they were aliens and sojourners on the earth.
14 Mutane masu faɗin irin abubuwan nan sun nuna cewa suna neman ƙasar da take tasu.
Now those who say such things make it clear that they are seeking a homeland.
15 Da a ce suna tunanin ƙasar da suka bari a baya, da sun riga sun sami damar komawa.
If they were actually remembering that land from which they had departed, they would have had opportunity to return.
16 A maimako, suna marmarin wata ƙasa mafi kyau, ta sama. Saboda haka Allah ba ya kunya a kira shi Allahnsu, domin ya riga ya shirya musu birni.
Instead they are aspiring to a better home—a heavenly one. Therefore God is not ashamed to be called their God; in fact He has prepared a city for them.
17 Ta wurin bangaskiya Ibrahim, sa’ad da Allah ya gwada shi, sai ya miƙa Ishaku hadaya. Shi da ya karɓi alkawaran ya yi shirin miƙa makaɗaicin ɗansa,
By faith Abraham, upon being tested, offered up Isaac; yes, he who had received the promises was about to sacrifice his only begotten,
18 ko da yake Allah ya ce masa, “Ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.”
of whom it had been said, “Through Isaac will your seed be reckoned,”
19 Ibrahim ya yi tunani cewa Allah yana iya tā da matattu, a misalce kuwa, ya sāke karɓan Ishaku daga matattu.
calculating that God was indeed able to raise him from the dead; from whence in fact he did receive him, figuratively speaking.
20 Ta wurin bangaskiya ne Ishaku ya albarkaci Yaƙub da Isuwa game da nan gabansu.
By faith Isaac blessed Jacob and Esau concerning things to come.
21 Ta wurin bangaskiya ne Yaƙub, sa’ad da yake bakin mutuwa, ya albarkaci kowane ɗan Yusuf, ya kuma yi sujada yayinda yake jingine a kan sandansa.
By faith Jacob, when he was dying, blessed each of Joseph's sons and worshiped, leaning on the top of his staff.
22 Ta wurin bangaskiya ne Yusuf, sa’ad da kwanakinsa suka yi kusan ƙarewa, ya yi magana game da fitowar Isra’ilawa daga Masar ya kuma ba da umarni game da ƙasusuwansa.
By faith Joseph, near the end, thought of the exodus of the sons of Israel and gave orders concerning his bones.
23 Ta wurin bangaskiya ne iyayen Musa suka ɓoye shi har wata uku bayan haihuwarsa, domin sun ga cewa shi ba kamar sauran yara ba ne, ba su kuwa ji tsoron umarnin sarki ba.
By faith Moses was hidden for three months by his parents, after he was born, because they saw he was a fine child, and they were not afraid of the king's edict.
24 Ta wurin bangaskiya ne Musa, sa’ad da ya yi girma, ya ƙi a kira shi ɗan diyar Fir’auna.
By faith Moses, when he had grown up, refused to be called the son of Pharaoh's daughter,
25 Ya zaɓa yă sha wahala tare da mutanen Allah, maimakon yă ji daɗin sha’awace-sha’awacen zunubi na ɗan lokaci.
choosing rather to be maltreated along with God's people than to have the temporary pleasure of sin,
26 Ya ɗauki wulaƙancin da yake sha saboda Kiristi ya fi dukiyar Masar daraja, domin ya sa ido ga ladansa.
considering the reproach of Christ to be greater riches than the treasures of Egypt; because he was looking ahead to the reward.
27 Ta wurin bangaskiya ya bar Masar, ba tare da jin tsoron fushin sarki ba; ya kuwa jure domin ya ga wannan wanda ba a iya gani.
By faith he left Egypt behind, not fearing the king's rage, because he persevered as though seeing Him who is invisible.
28 Ta wurin bangaskiya ya kiyaye Bikin Ƙetarewa ya kuma yayyafa jini, domin kada mai hallakar’ya’yan fari yă taɓa’ya’yan fari na Isra’ila.
By faith he kept the Passover and the sprinkling of the blood, so that the destroyer of the firstborn would not touch them.
29 Ta wurin bangaskiya ne mutane suka bi ta cikin Jan Teku, sai ka ce a kan busasshiyar ƙasa; amma da Masarawa suka yi ƙoƙari su yi haka, sai aka nutsar da su.
By faith they passed through the Red Sea as on dry ground, whereas the Egyptians, attempting to do so, were swallowed up.
30 Ta wurin bangaskiya ne katangar Yeriko ta rushe, bayan mutane suka yi ta kewaye ta har kwana bakwai.
By faith the walls of Jericho fell down, having been encircled for seven days.
31 Ta wurin bangaskiya ne ba a kashe Rahab karuwan nan, ta tare da marasa biyayya ba don ta marabci’yan leƙan asiri.
By faith the prostitute Rahab, having received the spies in peace, did not perish with the disobedient.
32 Me kuma zan faɗa? Ba ni da lokacin da zan ba da labari a kan Gideyon, Barak, Samson, Yefta, Dawuda, Sama’ila, da kuma annabawa,
And what more shall I say? For the time would fail me to tell about Gideon, about Barak and Samson and Jephtha, about David and Samuel and the prophets,
33 waɗanda ta wurin bangaskiya ne suka ci nasara a kan mulkoki, suka aikata adalci, suka kuma sami abin da aka yi alkawari; waɗanda suka rurrufe bakunan zakoki,
who through faith subdued kingdoms, administered justice, obtained promises, closed lions' mouths,
34 suka kashe harshen wuta, suka kuma tsere wa kaifin takobi; waɗanda aka mai da rashin ƙarfinsu ya zama ƙarfi; waɗanda suka yi jaruntaka wajen yaƙi suka kuma fatattaki mayaƙan waɗansu ƙasashe.
quenched the power of fire, escaped the edge of the sword, out of weakness were made strong, became mighty in battle, put to flight foreign armies.
35 Mata suka karɓi ƙaunatattunsu da aka sāke tasar daga matattu. Aka azabtar da yawancin mutanen nan, amma suka ƙi a sake su, domin sun tabbata za su sami lada mafi kyau sa’ad da aka tā da matattu.
Women received their dead back by resurrection; while others were tortured, not accepting their deliverance, so that they might obtain a better resurrection.
36 Waɗansu suka sha ba’a da bulala, har da dauri da sarƙa, da kuma jefa su cikin kurkuku.
Still others were tried by mockings and scourgings, and even by chains and imprisonment.
37 Aka jajjefe su da duwatsu; aka raba su biyu da zarto; aka kashe su da takobi. Suka yi ta yawo saye da fatun tumaki da na awaki, suka yi zaman rashi, suka sha tsanani da kuma wulaƙanci
They were stoned, they were sawed in two, they were tempted, they were murdered by sword. They went about in sheepskins and goatskins; being destitute, afflicted, mistreated
38 duniya ba tă ma cancanci su zauna a cikinta ba. Suka yi ta yawo a cikin hamada da a kan duwatsu, da cikin kogwanni da kuma cikin ramummuka.
—of whom the world was not worthy—wandering in deserts and mountains and caves and holes in the ground.
39 Waɗannan duka an yabe su saboda bangaskiyarsu, duk da haka babu waninsu da ya sami abin da aka yi alkawari.
Now all these did not receive the promise, though having been approved through faith,
40 Allah ya shirya mana wani abu mafi kyau. Kuma bai so su kai ga maƙasudin bangaskiyarsu ba sai tare da mu.
God having planned something better for us, so that they should not be perfected without us.

< Ibraniyawa 11 >

A Dove is Sent Forth from the Ark
A Dove is Sent Forth from the Ark