< Ibraniyawa 10 >

1 Dokar, inuwa ce kawai ta kyawawan abubuwa masu zuwa, wannan inuwar ba ita ce ainihin abubuwan ba ne. Saboda haka ba za tă taɓa mai da masu matsowa kusa don yin sujada cikakku ta wurin irin hadayun da ake maimaitawa ba fasawa shekara-shekara ba.
For the law, having a shadow of the good to come, not the very image of the things, can never with the same sacrifices year by year, which they offer continually, make perfect those who draw near.
2 Da a ce za tă iya, da ba su daina miƙa hadayu ba? Ai, da an riga an tsabtacce masu yin sujada sau ɗaya tak, da kuma ba za su ƙara damuwa da zunubansu ba.
Or else wouldn’t they have ceased to be offered, because the worshipers, having been once cleansed, would have had no more consciousness of sins?
3 Amma waɗancan hadayu abin tunawa da zunubai ne na kowace shekara,
But in those sacrifices there is a yearly reminder of sins.
4 domin ba zai taɓa yiwuwa jinin bijimai da na awaki yă kawar da zunubai ba.
For it is impossible that the blood of bulls and goats should take away sins.
5 Saboda haka, sa’ad da Kiristi ya shigo duniya ya ce, “Hadaya da sadaka kam ba ka so, sai dai ka tanadar mini jiki;
Therefore when he comes into the world, he says, “You didn’t desire sacrifice and offering, but you prepared a body for me.
6 hadayun ƙonawa da kuma hadayun zunubi ba ka ji daɗin.
You had no pleasure in whole burnt offerings and sacrifices for sin.
7 Sai na ce, ‘Ga ni nan, a rubuce yake cikin naɗaɗɗen littafi na zo in aikata nufinka, ya Allah.’”
Then I said, ‘Behold, I have come (in the scroll of the book it is written of me) to do your will, O God.’”
8 Da farko ya ce, “Hadayu da sadakoki, hadayun ƙonawa da hadayun zunubi ba ka so, ba ka kuwa jin daɗinsu” (ko da yake doka ta bukaci a yi su).
Previously saying, “Sacrifices and offerings and whole burnt offerings and sacrifices for sin you didn’t desire, neither had pleasure in them” (those which are offered according to the law),
9 Sa’an nan ya ce, “Ga ni nan, na zo in aikata nufinka.” Ya kawar da na farkon domin yă kafa na biyun.
then he has said, “Behold, I have come to do your will.” He takes away the first, that he may establish the second,
10 Kuma bisa ga wannan nufi, aka mai da mu masu tsarki ta wurin miƙa hadayar jikin Yesu Kiristi sau ɗaya tak.
by which will we have been sanctified through the offering of the body of Jesus Christ once for all.
11 Kowace rana kowane firist yakan tsaya yin hidimar ibadarsa; sau da sau yakan miƙa hadayu iri ɗaya, waɗanda ba za su taɓa kawar da zunubai ba.
Every priest indeed stands day by day serving and offering often the same sacrifices, which can never take away sins,
12 Amma da Kiristi ya miƙa hadaya ɗaya ta dukan lokaci saboda zunubai, sai ya zauna a hannun dama na Allah.
but he, when he had offered one sacrifice for sins forever, sat down on the right hand of God,
13 Tun daga lokacin nan yana jira a mai da abokan gābansa matashin ƙafafunsa,
from that time waiting until his enemies are made the footstool of his feet.
14 gama ta wurin hadayan nan guda ɗaya ya kammala har abada waɗanda ake tsarkake.
For by one offering he has perfected forever those who are being sanctified.
15 Ruhu Mai Tsarki ma ya yi mana shaida game da wannan. Da farko ya ce,
The Holy Spirit also testifies to us, for after saying,
16 “Wannan shi ne alkawarin da zan yi da su bayan wannan lokaci, in ji Ubangiji. Zan sa dokokina a cikin zukatansu, in kuma rubuta su a kan zukatansu.”
“This is the covenant that I will make with them after those days,” says the Lord, “I will put my laws on their heart, I will also write them on their mind;” then he says,
17 Sai ya ƙara da cewa, “Zunubansu da kurakuransu ba zan ƙara tunawa da su ba.”
“I will remember their sins and their iniquities no more.”
18 In an gafarta zunubai, babu sauran bukatar miƙa hadaya.
Now where remission of these is, there is no more offering for sin.
19 Saboda haka,’yan’uwa, da yake muna da wannan tabbaci na shiga Wuri Mafi Tsarki ta wurin jinin Yesu,
Having therefore, brothers, boldness to enter into the holy place by the blood of Jesus,
20 ta wurin sabuwa, rayayyiyar hanya kuma wadda aka buɗe mana ta labulen nan, wato, jikinsa,
by the way which he dedicated for us, a new and living way, through the veil, that is to say, his flesh,
21 da yake kuma muna da babban firist mai mulkin gidan Allah,
and having a great priest over God’s house,
22 bari mu matso kusa da Allah da zuciya mai gaskiya da kuma cikakken tabbaci mai zuwa ta wurin bangaskiya. Bari mu bar zukatan da tsabta, lamirinmu babu mugunta, da kuma jikunanmu a wanke da ruwa.
let’s draw near with a true heart in fullness of faith, having our hearts sprinkled from an evil conscience and having our body washed with pure water,
23 Bari mu tsaya da ƙarfi a kan ga begen da muka ce namu ne, gama shi da ya yi alkawarin, mai aminci ne.
let’s hold fast the confession of our hope without wavering; for he who promised is faithful.
24 Bari kuma mu yi tunani a kan yadda za mu gargaɗe juna ga ƙauna da kuma ayyuka nagari.
Let’s consider how to provoke one another to love and good works,
25 Kada mu daina taruwa kamar yadda waɗansu suka saba, sai dai mu ƙarfafa juna, tun ba ma da kuka ga Ranan nan tana kusatowa ba.
not forsaking our own assembling together, as the custom of some is, but exhorting one another, and so much the more as you see the Day approaching.
26 Ba wata hadayar da za a yi don mutanen da suka yanke shawara su yi ci gaba da yin zunubi da gangan bayan sun sami sanin gaskiya.
For if we sin willfully after we have received the knowledge of the truth, there remains no more a sacrifice for sins,
27 A maimakon haka za su kasance da babban fargabar hukunci da kuma ta ƙunar wuta wadda za tă cinye abokan gāban Allah.
but a certain fearful expectation of judgment, and a fierceness of fire which will devour the adversaries.
28 Duk wanda ya ƙi ya kiyaye dokar Musa akan kashe shi ba tausayi, a kan shaidar mutum biyu ko uku.
A man who disregards Moses’ law dies without compassion on the word of two or three witnesses.
29 Wane irin hukunci mai tsanani ne kuke tsammani zai dace da mutumin da ya nuna rashin bangirma ga Ɗan Allah, wanda ya yi banza da jinin nan na alkawarin da ya tsarkake shi, wanda kuma ya zargi Ruhun alheri?
How much worse punishment do you think he will be judged worthy of who has trodden under foot the Son of God, and has counted the blood of the covenant with which he was sanctified an unholy thing, and has insulted the Spirit of grace?
30 Gama mun san shi, wannan wanda ya ce, “Ramuwa tawa ce; zan rama,” da kuma, “Ubangiji zai yi wa mutanensa hukunci.”
For we know him who said, “Vengeance belongs to me. I will repay,” says the Lord. Again, “The Lord will judge his people.”
31 Abu mai matuƙar bantsoro ne a fāɗa cikin hannuwan Allah mai rai.
It is a fearful thing to fall into the hands of the living God.
32 Ku tuna da kwanakin nan da suka wuce bayan kun sami haske, sa’ad da kuka tsaya daram a tsananin shan wahala.
But remember the former days, in which, after you were enlightened, you endured a great struggle with sufferings:
33 Wani lokaci a fili an tsananta muku aka kuma zage ku aka kuma tsananta muku; a wani lokaci kuma kuka tsaya tare da waɗanda aka yi musu haka.
partly, being exposed to both reproaches and oppressions, and partly, becoming partakers with those who were treated so.
34 Kuka ji tausayin waɗanda suke cikin kurkuku, da farin ciki kuma kuka yarda ku rabu da dukiyar da aka ƙwace muku, domin ku kanku kun san cewa kuna da madawwamiyar dukiya mafi kyau.
For you both had compassion on me in my chains and joyfully accepted the plundering of your possessions, knowing that you have for yourselves a better possession and an enduring one in the heavens.
35 Saboda haka kada ku yar da tabbacinku; za a sāka muku a yalwace.
Therefore don’t throw away your boldness, which has a great reward.
36 Kuna bukata ku jimre don sa’ad da kuka aikata nufin Allah, za ku karɓi abin da ya yi alkawari.
For you need endurance so that, having done the will of God, you may receive the promise.
37 Gama, “A cikin ɗan lokaci kaɗan, mai zuwan nan zai zo ba kuwa zai yi jinkiri ba.
“In a very little while, he who comes will come and will not wait.
38 Amma, “Mai adalcina zai rayu ta wurin bangaskiya. In kuwa ya ja da baya, ba zan ji daɗinsa ba.”
But the righteous one will live by faith. If he shrinks back, my soul has no pleasure in him.”
39 Amma mu ba na waɗanda suke ja da baya, su kuma hallaka ba ne, amma na waɗanda suka gaskata, suka kuma sami ceto ne.
But we are not of those who shrink back to destruction, but of those who have faith to the saving of the soul.

< Ibraniyawa 10 >