< Ibraniyawa 10 >

1 Dokar, inuwa ce kawai ta kyawawan abubuwa masu zuwa, wannan inuwar ba ita ce ainihin abubuwan ba ne. Saboda haka ba za tă taɓa mai da masu matsowa kusa don yin sujada cikakku ta wurin irin hadayun da ake maimaitawa ba fasawa shekara-shekara ba.
For, since the Law exhibits only an outline of the blessings to come and not a perfect representation of the things themselves, the priests can never, by repeating the same sacrifices which they continually offer year after year, give complete freedom from sin to those who draw near.
2 Da a ce za tă iya, da ba su daina miƙa hadayu ba? Ai, da an riga an tsabtacce masu yin sujada sau ɗaya tak, da kuma ba za su ƙara damuwa da zunubansu ba.
For then would not the sacrifices have ceased to be offered, because the consciences of the worshippers--who in that case would now have been cleansed once for all--would no longer be burdened with sins?
3 Amma waɗancan hadayu abin tunawa da zunubai ne na kowace shekara,
But in those sacrifices sins are recalled to memory year after year.
4 domin ba zai taɓa yiwuwa jinin bijimai da na awaki yă kawar da zunubai ba.
For it is impossible for the blood of bulls and goats to take away sins.
5 Saboda haka, sa’ad da Kiristi ya shigo duniya ya ce, “Hadaya da sadaka kam ba ka so, sai dai ka tanadar mini jiki;
That is why, when He comes into the world, He says, "Sacrifice and offering Thou has not desired, but a body Thou hast prepared for Me.
6 hadayun ƙonawa da kuma hadayun zunubi ba ka ji daɗin.
In whole burnt-offerings and in sin-offerings Thou hast taken no pleasure.
7 Sai na ce, ‘Ga ni nan, a rubuce yake cikin naɗaɗɗen littafi na zo in aikata nufinka, ya Allah.’”
Then I said, 'I have come--in the roll of the book it is written concerning Me--to do Thy will, O God.'"
8 Da farko ya ce, “Hadayu da sadakoki, hadayun ƙonawa da hadayun zunubi ba ka so, ba ka kuwa jin daɗinsu” (ko da yake doka ta bukaci a yi su).
After saying the words I have just quoted, "Sacrifices and offerings or whole burnt-offerings and sin-offerings Thou hast not desired or taken pleasure in" --all such being offered in obedience to the Law--
9 Sa’an nan ya ce, “Ga ni nan, na zo in aikata nufinka.” Ya kawar da na farkon domin yă kafa na biyun.
He then adds, "I have come to do Thy will." He does away with the first in order to establish the second.
10 Kuma bisa ga wannan nufi, aka mai da mu masu tsarki ta wurin miƙa hadayar jikin Yesu Kiristi sau ɗaya tak.
It is through that divine will that we have been set free from sin, through the offering of Jesus Christ as our sacrifice once for all.
11 Kowace rana kowane firist yakan tsaya yin hidimar ibadarsa; sau da sau yakan miƙa hadayu iri ɗaya, waɗanda ba za su taɓa kawar da zunubai ba.
And while every priest stands ministering, day after day, and constantly offering the same sacrifices--though such can never rid us of our sins--
12 Amma da Kiristi ya miƙa hadaya ɗaya ta dukan lokaci saboda zunubai, sai ya zauna a hannun dama na Allah.
this Priest, on the contrary, after offering for sins a single sacrifice of perpetual efficacy, took His seat at God's right hand,
13 Tun daga lokacin nan yana jira a mai da abokan gābansa matashin ƙafafunsa,
waiting from that time onward until His enemies be put as a footstool under His feet.
14 gama ta wurin hadayan nan guda ɗaya ya kammala har abada waɗanda ake tsarkake.
For by a single offering He has for ever completed the blessing for those whom He is setting free from sin.
15 Ruhu Mai Tsarki ma ya yi mana shaida game da wannan. Da farko ya ce,
And the Holy Spirit also gives us His testimony; for when He had said,
16 “Wannan shi ne alkawarin da zan yi da su bayan wannan lokaci, in ji Ubangiji. Zan sa dokokina a cikin zukatansu, in kuma rubuta su a kan zukatansu.”
"'This is the Covenant that I will make with them after those days,' says the Lord: 'I will put My laws upon their hearts and will write them on their minds;'"
17 Sai ya ƙara da cewa, “Zunubansu da kurakuransu ba zan ƙara tunawa da su ba.”
He adds, "And their sins and offences I will remember no longer."
18 In an gafarta zunubai, babu sauran bukatar miƙa hadaya.
But where these have been forgiven no further offering for sin is required.
19 Saboda haka,’yan’uwa, da yake muna da wannan tabbaci na shiga Wuri Mafi Tsarki ta wurin jinin Yesu,
Since then, brethren, we have free access to the Holy place through the blood of Jesus,
20 ta wurin sabuwa, rayayyiyar hanya kuma wadda aka buɗe mana ta labulen nan, wato, jikinsa,
by the new and ever-living way which He opened up for us through the rending of the veil--that is to say, of His earthly nature--
21 da yake kuma muna da babban firist mai mulkin gidan Allah,
and since we have a great Priest who has authority over the house of God,
22 bari mu matso kusa da Allah da zuciya mai gaskiya da kuma cikakken tabbaci mai zuwa ta wurin bangaskiya. Bari mu bar zukatan da tsabta, lamirinmu babu mugunta, da kuma jikunanmu a wanke da ruwa.
let us draw near with sincerity and unfaltering faith, having had our hearts sprinkled, once for all, from consciences oppressed with sin, and our bodies bathed in pure water.
23 Bari mu tsaya da ƙarfi a kan ga begen da muka ce namu ne, gama shi da ya yi alkawarin, mai aminci ne.
Let us hold firmly to an unflinching avowal of our hope, for He is faithful who gave us the promises.
24 Bari kuma mu yi tunani a kan yadda za mu gargaɗe juna ga ƙauna da kuma ayyuka nagari.
And let us bestow thought on one another with a view to arousing one another to brotherly love and right conduct;
25 Kada mu daina taruwa kamar yadda waɗansu suka saba, sai dai mu ƙarfafa juna, tun ba ma da kuka ga Ranan nan tana kusatowa ba.
not neglecting--as some habitually do--to meet together, but encouraging one another, and doing this all the more since you can see the day of Christ approaching.
26 Ba wata hadayar da za a yi don mutanen da suka yanke shawara su yi ci gaba da yin zunubi da gangan bayan sun sami sanin gaskiya.
For if we wilfully persist in sin after having received the full knowledge of the truth, there no longer remains in reserve any other sacrifice for sins.
27 A maimakon haka za su kasance da babban fargabar hukunci da kuma ta ƙunar wuta wadda za tă cinye abokan gāban Allah.
There remains nothing but a certain awful expectation of judgement, and the fury of a fire which before long will devour the enemies of the truth.
28 Duk wanda ya ƙi ya kiyaye dokar Musa akan kashe shi ba tausayi, a kan shaidar mutum biyu ko uku.
Any one who bids defiance to the Law of Moses is put to death without mercy on the testimony of two or three witnesses.
29 Wane irin hukunci mai tsanani ne kuke tsammani zai dace da mutumin da ya nuna rashin bangirma ga Ɗan Allah, wanda ya yi banza da jinin nan na alkawarin da ya tsarkake shi, wanda kuma ya zargi Ruhun alheri?
How much severer punishment, think you, will he be held to deserve who has trampled under foot the Son of God, has not regarded as holy that Covenant-blood with which he was set free from sin, and has insulted the Spirit from whom comes grace?
30 Gama mun san shi, wannan wanda ya ce, “Ramuwa tawa ce; zan rama,” da kuma, “Ubangiji zai yi wa mutanensa hukunci.”
For we know who it is that has said, "Vengeance belongs to Me: I will pay back;" and again, "The Lord will be His people's judge."
31 Abu mai matuƙar bantsoro ne a fāɗa cikin hannuwan Allah mai rai.
It is an awful thing to fall into the hands of the ever-living God.
32 Ku tuna da kwanakin nan da suka wuce bayan kun sami haske, sa’ad da kuka tsaya daram a tsananin shan wahala.
But continually recall to mind the days now past, when on being first enlightened you went through a great conflict and many sufferings.
33 Wani lokaci a fili an tsananta muku aka kuma zage ku aka kuma tsananta muku; a wani lokaci kuma kuka tsaya tare da waɗanda aka yi musu haka.
This was partly through allowing yourselves to be made a public spectacle amid reproaches and persecutions, and partly through coming forward to share the sufferings of those who were thus treated.
34 Kuka ji tausayin waɗanda suke cikin kurkuku, da farin ciki kuma kuka yarda ku rabu da dukiyar da aka ƙwace muku, domin ku kanku kun san cewa kuna da madawwamiyar dukiya mafi kyau.
For you not only showed sympathy with those who were imprisoned, but you even submitted with joy when your property was taken from you, being well aware that you have in your own selves a more valuable possession and one which will remain.
35 Saboda haka kada ku yar da tabbacinku; za a sāka muku a yalwace.
Therefore do not cast from you your confident hope, for it will receive a vast reward.
36 Kuna bukata ku jimre don sa’ad da kuka aikata nufin Allah, za ku karɓi abin da ya yi alkawari.
For you stand in need of patient endurance, so that, as the result of having done the will of God, you may receive the promised blessing.
37 Gama, “A cikin ɗan lokaci kaɗan, mai zuwan nan zai zo ba kuwa zai yi jinkiri ba.
For there is still but a short time and then "The coming One will come and will not delay.
38 Amma, “Mai adalcina zai rayu ta wurin bangaskiya. In kuwa ya ja da baya, ba zan ji daɗinsa ba.”
But it is by faith that My righteous servant shall live; and if he shrinks back, My soul takes no pleasure in him."
39 Amma mu ba na waɗanda suke ja da baya, su kuma hallaka ba ne, amma na waɗanda suka gaskata, suka kuma sami ceto ne.
But we are not people who shrink back and perish, but are among those who believe and gain possession of their souls.

< Ibraniyawa 10 >