< Ibraniyawa 10 >

1 Dokar, inuwa ce kawai ta kyawawan abubuwa masu zuwa, wannan inuwar ba ita ce ainihin abubuwan ba ne. Saboda haka ba za tă taɓa mai da masu matsowa kusa don yin sujada cikakku ta wurin irin hadayun da ake maimaitawa ba fasawa shekara-shekara ba.
For the law having a shadow of good things to come, and not the very image of the things, can never with those sacrifices which they offered year by year continually make the comers thereunto perfect.
2 Da a ce za tă iya, da ba su daina miƙa hadayu ba? Ai, da an riga an tsabtacce masu yin sujada sau ɗaya tak, da kuma ba za su ƙara damuwa da zunubansu ba.
For then would they not have ceased to be offered? because that the worshippers once purged should have had no more conscience of sins.
3 Amma waɗancan hadayu abin tunawa da zunubai ne na kowace shekara,
But in those sacrifices there is a remembrance again made of sins every year.
4 domin ba zai taɓa yiwuwa jinin bijimai da na awaki yă kawar da zunubai ba.
For it is not possible that the blood of bulls and of goats should take away sins.
5 Saboda haka, sa’ad da Kiristi ya shigo duniya ya ce, “Hadaya da sadaka kam ba ka so, sai dai ka tanadar mini jiki;
Wherefore when he comes into the world, he says, Sacrifice and offering you would not, but a body have you prepared me:
6 hadayun ƙonawa da kuma hadayun zunubi ba ka ji daɗin.
In burnt offerings and sacrifices for sin you have had no pleasure.
7 Sai na ce, ‘Ga ni nan, a rubuce yake cikin naɗaɗɗen littafi na zo in aikata nufinka, ya Allah.’”
Then said I, Lo, I come (in the volume of the book it is written of me, ) to do your will, O God.
8 Da farko ya ce, “Hadayu da sadakoki, hadayun ƙonawa da hadayun zunubi ba ka so, ba ka kuwa jin daɗinsu” (ko da yake doka ta bukaci a yi su).
Above when he said, Sacrifice and offering and burnt offerings and offering for sin you would not, neither had pleasure therein; which are offered by the law;
9 Sa’an nan ya ce, “Ga ni nan, na zo in aikata nufinka.” Ya kawar da na farkon domin yă kafa na biyun.
Then said he, Lo, I come to do your will, O God. He takes away the first, that he may establish the second.
10 Kuma bisa ga wannan nufi, aka mai da mu masu tsarki ta wurin miƙa hadayar jikin Yesu Kiristi sau ɗaya tak.
By the which will we are sanctified through the offering of the body of Jesus Christ once for all.
11 Kowace rana kowane firist yakan tsaya yin hidimar ibadarsa; sau da sau yakan miƙa hadayu iri ɗaya, waɗanda ba za su taɓa kawar da zunubai ba.
And every priest stands daily ministering and offering oftentimes the same sacrifices, which can never take away sins:
12 Amma da Kiristi ya miƙa hadaya ɗaya ta dukan lokaci saboda zunubai, sai ya zauna a hannun dama na Allah.
But this man, after he had offered one sacrifice for sins for ever, sat down on the right hand of God;
13 Tun daga lokacin nan yana jira a mai da abokan gābansa matashin ƙafafunsa,
From henceforth expecting till his enemies be made his footstool.
14 gama ta wurin hadayan nan guda ɗaya ya kammala har abada waɗanda ake tsarkake.
For by one offering he has perfected for ever them that are sanctified.
15 Ruhu Mai Tsarki ma ya yi mana shaida game da wannan. Da farko ya ce,
Whereof the Holy Spirit (pneuma) also is a witness to us: for after that he had said before,
16 “Wannan shi ne alkawarin da zan yi da su bayan wannan lokaci, in ji Ubangiji. Zan sa dokokina a cikin zukatansu, in kuma rubuta su a kan zukatansu.”
This is the covenant that I will make with them after those days, says the Lord, I will put my laws into their hearts, and in their minds will I write them;
17 Sai ya ƙara da cewa, “Zunubansu da kurakuransu ba zan ƙara tunawa da su ba.”
And their sins and iniquities will I remember no more.
18 In an gafarta zunubai, babu sauran bukatar miƙa hadaya.
Now where remission of these is, there is no more offering for sin.
19 Saboda haka,’yan’uwa, da yake muna da wannan tabbaci na shiga Wuri Mafi Tsarki ta wurin jinin Yesu,
Having therefore, brethren, boldness to enter into the holiest by the blood of Jesus,
20 ta wurin sabuwa, rayayyiyar hanya kuma wadda aka buɗe mana ta labulen nan, wato, jikinsa,
By a new and living way, which he has consecrated for us, through the veil, that is to say, his flesh;
21 da yake kuma muna da babban firist mai mulkin gidan Allah,
And having an high priest over the house of God;
22 bari mu matso kusa da Allah da zuciya mai gaskiya da kuma cikakken tabbaci mai zuwa ta wurin bangaskiya. Bari mu bar zukatan da tsabta, lamirinmu babu mugunta, da kuma jikunanmu a wanke da ruwa.
Let us draw near with a true heart in full assurance of faith, having our hearts sprinkled from an evil conscience, and our bodies washed with pure water.
23 Bari mu tsaya da ƙarfi a kan ga begen da muka ce namu ne, gama shi da ya yi alkawarin, mai aminci ne.
Let us hold fast the profession of our faith without wavering; (for he is faithful that promised; )
24 Bari kuma mu yi tunani a kan yadda za mu gargaɗe juna ga ƙauna da kuma ayyuka nagari.
And let us consider one another to provoke unto love (agape) and to good works:
25 Kada mu daina taruwa kamar yadda waɗansu suka saba, sai dai mu ƙarfafa juna, tun ba ma da kuka ga Ranan nan tana kusatowa ba.
Not forsaking the assembling of ourselves together, as the manner of some is; but exhorting one another: and so much the more, as all of you see the day approaching.
26 Ba wata hadayar da za a yi don mutanen da suka yanke shawara su yi ci gaba da yin zunubi da gangan bayan sun sami sanin gaskiya.
For if we sin willfully after that we have received the knowledge of the truth, there remains no more sacrifice for sins,
27 A maimakon haka za su kasance da babban fargabar hukunci da kuma ta ƙunar wuta wadda za tă cinye abokan gāban Allah.
But a certain fearful looking for of judgment and fiery indignation, which shall devour the adversaries.
28 Duk wanda ya ƙi ya kiyaye dokar Musa akan kashe shi ba tausayi, a kan shaidar mutum biyu ko uku.
He that despised Moses' law died without mercy under two or three witnesses:
29 Wane irin hukunci mai tsanani ne kuke tsammani zai dace da mutumin da ya nuna rashin bangirma ga Ɗan Allah, wanda ya yi banza da jinin nan na alkawarin da ya tsarkake shi, wanda kuma ya zargi Ruhun alheri?
Of how much greater punishment, suppose all of you, shall he be thought worthy, who has trodden under foot the Son of God, and has counted the blood of the covenant, wherewith he was sanctified, an unholy thing, and has done despite unto the Spirit (pneuma) of grace?
30 Gama mun san shi, wannan wanda ya ce, “Ramuwa tawa ce; zan rama,” da kuma, “Ubangiji zai yi wa mutanensa hukunci.”
For we know him that has said, Vengeance belongs unto me, I will recompense, says the Lord. And again, The Lord shall judge his people.
31 Abu mai matuƙar bantsoro ne a fāɗa cikin hannuwan Allah mai rai.
It is a fearful thing to fall into the hands of the living God.
32 Ku tuna da kwanakin nan da suka wuce bayan kun sami haske, sa’ad da kuka tsaya daram a tsananin shan wahala.
But call to remembrance the former days, in which, after all of you were illuminated, all of you endured a great fight of afflictions;
33 Wani lokaci a fili an tsananta muku aka kuma zage ku aka kuma tsananta muku; a wani lokaci kuma kuka tsaya tare da waɗanda aka yi musu haka.
Partly, whilst all of you were made a gazing-stock both by reproaches and afflictions; and partly, whilst all of you became companions of them that were so used.
34 Kuka ji tausayin waɗanda suke cikin kurkuku, da farin ciki kuma kuka yarda ku rabu da dukiyar da aka ƙwace muku, domin ku kanku kun san cewa kuna da madawwamiyar dukiya mafi kyau.
For all of you had compassion of me in my bonds, and took joyfully the spoiling of your goods, knowing in yourselves that all of you have in heaven a better and an enduring substance.
35 Saboda haka kada ku yar da tabbacinku; za a sāka muku a yalwace.
Cast not away therefore your confidence, which has great recompence of reward.
36 Kuna bukata ku jimre don sa’ad da kuka aikata nufin Allah, za ku karɓi abin da ya yi alkawari.
For all of you have need of patience, that, after all of you have done the will of God, all of you might receive the promise.
37 Gama, “A cikin ɗan lokaci kaɗan, mai zuwan nan zai zo ba kuwa zai yi jinkiri ba.
For yet a little while, and he that shall come will come, and will not tarry.
38 Amma, “Mai adalcina zai rayu ta wurin bangaskiya. In kuwa ya ja da baya, ba zan ji daɗinsa ba.”
Now the just shall live by faith: but if any man draw back, my soul shall have no pleasure in him.
39 Amma mu ba na waɗanda suke ja da baya, su kuma hallaka ba ne, amma na waɗanda suka gaskata, suka kuma sami ceto ne.
But we are not of them who draw back unto perdition; but of them that believe to the saving of the soul.

< Ibraniyawa 10 >