< Ibraniyawa 10 >

1 Dokar, inuwa ce kawai ta kyawawan abubuwa masu zuwa, wannan inuwar ba ita ce ainihin abubuwan ba ne. Saboda haka ba za tă taɓa mai da masu matsowa kusa don yin sujada cikakku ta wurin irin hadayun da ake maimaitawa ba fasawa shekara-shekara ba.
For the law is only a shadow of the good things to come, not the realities themselves. It can never, by the same sacrifices offered year after year, make perfect those who draw near to worship.
2 Da a ce za tă iya, da ba su daina miƙa hadayu ba? Ai, da an riga an tsabtacce masu yin sujada sau ɗaya tak, da kuma ba za su ƙara damuwa da zunubansu ba.
If it could, would not the offerings have ceased? For the worshipers would have been cleansed once for all, and would no longer have felt the guilt of their sins.
3 Amma waɗancan hadayu abin tunawa da zunubai ne na kowace shekara,
Instead, those sacrifices are an annual reminder of sins,
4 domin ba zai taɓa yiwuwa jinin bijimai da na awaki yă kawar da zunubai ba.
because it is impossible for the blood of bulls and goats to take away sins.
5 Saboda haka, sa’ad da Kiristi ya shigo duniya ya ce, “Hadaya da sadaka kam ba ka so, sai dai ka tanadar mini jiki;
Therefore, when Christ came into the world, He said: “Sacrifice and offering You did not desire, but a body You prepared for Me.
6 hadayun ƙonawa da kuma hadayun zunubi ba ka ji daɗin.
In burnt offerings and sin offerings You took no delight.
7 Sai na ce, ‘Ga ni nan, a rubuce yake cikin naɗaɗɗen littafi na zo in aikata nufinka, ya Allah.’”
Then I said, ‘Here I am, it is written about Me in the scroll: I have come to do Your will, O God.’”
8 Da farko ya ce, “Hadayu da sadakoki, hadayun ƙonawa da hadayun zunubi ba ka so, ba ka kuwa jin daɗinsu” (ko da yake doka ta bukaci a yi su).
In the passage above He says, “Sacrifices and offerings, burnt offerings and sin offerings You did not desire, nor did You delight in them” (although they are offered according to the law).
9 Sa’an nan ya ce, “Ga ni nan, na zo in aikata nufinka.” Ya kawar da na farkon domin yă kafa na biyun.
Then He adds, “Here I am, I have come to do Your will.” He takes away the first to establish the second.
10 Kuma bisa ga wannan nufi, aka mai da mu masu tsarki ta wurin miƙa hadayar jikin Yesu Kiristi sau ɗaya tak.
And by that will, we have been sanctified through the sacrifice of the body of Jesus Christ once for all.
11 Kowace rana kowane firist yakan tsaya yin hidimar ibadarsa; sau da sau yakan miƙa hadayu iri ɗaya, waɗanda ba za su taɓa kawar da zunubai ba.
Day after day every priest stands to minister and to offer again and again the same sacrifices, which can never take away sins.
12 Amma da Kiristi ya miƙa hadaya ɗaya ta dukan lokaci saboda zunubai, sai ya zauna a hannun dama na Allah.
But when this Priest had offered for all time one sacrifice for sins, He sat down at the right hand of God.
13 Tun daga lokacin nan yana jira a mai da abokan gābansa matashin ƙafafunsa,
Since that time, He waits for His enemies to be made a footstool for His feet,
14 gama ta wurin hadayan nan guda ɗaya ya kammala har abada waɗanda ake tsarkake.
because by a single offering He has made perfect for all time those who are being sanctified.
15 Ruhu Mai Tsarki ma ya yi mana shaida game da wannan. Da farko ya ce,
The Holy Spirit also testifies to us about this. First He says:
16 “Wannan shi ne alkawarin da zan yi da su bayan wannan lokaci, in ji Ubangiji. Zan sa dokokina a cikin zukatansu, in kuma rubuta su a kan zukatansu.”
“This is the covenant I will make with them after those days, declares the Lord. I will put My laws in their hearts and inscribe them on their minds.”
17 Sai ya ƙara da cewa, “Zunubansu da kurakuransu ba zan ƙara tunawa da su ba.”
Then He adds: “Their sins and lawless acts I will remember no more.”
18 In an gafarta zunubai, babu sauran bukatar miƙa hadaya.
And where these have been forgiven, an offering for sin is no longer needed.
19 Saboda haka,’yan’uwa, da yake muna da wannan tabbaci na shiga Wuri Mafi Tsarki ta wurin jinin Yesu,
Therefore, brothers, since we have confidence to enter the Most Holy Place by the blood of Jesus,
20 ta wurin sabuwa, rayayyiyar hanya kuma wadda aka buɗe mana ta labulen nan, wato, jikinsa,
by the new and living way opened for us through the curtain of His body,
21 da yake kuma muna da babban firist mai mulkin gidan Allah,
and since we have a great priest over the house of God,
22 bari mu matso kusa da Allah da zuciya mai gaskiya da kuma cikakken tabbaci mai zuwa ta wurin bangaskiya. Bari mu bar zukatan da tsabta, lamirinmu babu mugunta, da kuma jikunanmu a wanke da ruwa.
let us draw near with a sincere heart in full assurance of faith, having our hearts sprinkled to cleanse us from a guilty conscience and our bodies washed with pure water.
23 Bari mu tsaya da ƙarfi a kan ga begen da muka ce namu ne, gama shi da ya yi alkawarin, mai aminci ne.
Let us hold resolutely to the hope we profess, for He who promised is faithful.
24 Bari kuma mu yi tunani a kan yadda za mu gargaɗe juna ga ƙauna da kuma ayyuka nagari.
And let us consider how to spur one another on to love and good deeds.
25 Kada mu daina taruwa kamar yadda waɗansu suka saba, sai dai mu ƙarfafa juna, tun ba ma da kuka ga Ranan nan tana kusatowa ba.
Let us not neglect meeting together, as some have made a habit, but let us encourage one another, and all the more as you see the Day approaching.
26 Ba wata hadayar da za a yi don mutanen da suka yanke shawara su yi ci gaba da yin zunubi da gangan bayan sun sami sanin gaskiya.
If we deliberately go on sinning after we have received the knowledge of the truth, no further sacrifice for sins remains,
27 A maimakon haka za su kasance da babban fargabar hukunci da kuma ta ƙunar wuta wadda za tă cinye abokan gāban Allah.
but only a fearful expectation of judgment and of raging fire that will consume all adversaries.
28 Duk wanda ya ƙi ya kiyaye dokar Musa akan kashe shi ba tausayi, a kan shaidar mutum biyu ko uku.
Anyone who rejected the law of Moses died without mercy on the testimony of two or three witnesses.
29 Wane irin hukunci mai tsanani ne kuke tsammani zai dace da mutumin da ya nuna rashin bangirma ga Ɗan Allah, wanda ya yi banza da jinin nan na alkawarin da ya tsarkake shi, wanda kuma ya zargi Ruhun alheri?
How much more severely do you think one deserves to be punished who has trampled on the Son of God, profaned the blood of the covenant that sanctified him, and insulted the Spirit of grace?
30 Gama mun san shi, wannan wanda ya ce, “Ramuwa tawa ce; zan rama,” da kuma, “Ubangiji zai yi wa mutanensa hukunci.”
For we know Him who said, “Vengeance is Mine; I will repay,” and again, “The Lord will judge His people.”
31 Abu mai matuƙar bantsoro ne a fāɗa cikin hannuwan Allah mai rai.
It is a fearful thing to fall into the hands of the living God.
32 Ku tuna da kwanakin nan da suka wuce bayan kun sami haske, sa’ad da kuka tsaya daram a tsananin shan wahala.
Remember the early days that you were in the light. In those days, you endured a great conflict in the face of suffering.
33 Wani lokaci a fili an tsananta muku aka kuma zage ku aka kuma tsananta muku; a wani lokaci kuma kuka tsaya tare da waɗanda aka yi musu haka.
Sometimes you were publicly exposed to ridicule and persecution; at other times you were partners with those who were so treated.
34 Kuka ji tausayin waɗanda suke cikin kurkuku, da farin ciki kuma kuka yarda ku rabu da dukiyar da aka ƙwace muku, domin ku kanku kun san cewa kuna da madawwamiyar dukiya mafi kyau.
You sympathized with those in prison and joyfully accepted the confiscation of your property, knowing that you yourselves had a better and permanent possession.
35 Saboda haka kada ku yar da tabbacinku; za a sāka muku a yalwace.
So do not throw away your confidence; it holds a great reward.
36 Kuna bukata ku jimre don sa’ad da kuka aikata nufin Allah, za ku karɓi abin da ya yi alkawari.
You need to persevere, so that after you have done the will of God, you will receive what He has promised.
37 Gama, “A cikin ɗan lokaci kaɗan, mai zuwan nan zai zo ba kuwa zai yi jinkiri ba.
For, “In just a little while, He who is coming will come and will not delay.
38 Amma, “Mai adalcina zai rayu ta wurin bangaskiya. In kuwa ya ja da baya, ba zan ji daɗinsa ba.”
But My righteous one will live by faith; and if he shrinks back, I will take no pleasure in him.”
39 Amma mu ba na waɗanda suke ja da baya, su kuma hallaka ba ne, amma na waɗanda suka gaskata, suka kuma sami ceto ne.
But we are not of those who shrink back and are destroyed, but of those who have faith and preserve their souls.

< Ibraniyawa 10 >