< Ibraniyawa 1 >

1 A dā Allah ya yi wa kakanni-kakanninmu magana ta bakin annabawa a lokuta dabam-dabam da kuma a hanyoyi iri-iri,
Tanrı eski zamanlarda peygamberler aracılığıyla birçok kez çeşitli yollardan atalarımıza seslendi.
2 amma a waɗannan kwanaki a ƙarshe ya yi magana da mu ta wurin Ɗansa, wanda ya naɗa magājin dukan abubuwa, wanda kuma ta wurinsa ya halicci duniya. (aiōn g165)
Bu son çağda da her şeye mirasçı kıldığı ve aracılığıyla evreni yarattığı kendi Oğlu'yla bize seslenmiştir. (aiōn g165)
3 Ɗan shi ne hasken ɗaukakar Allah, shi ne kuma ainihin kamanninsa, yana riƙe da dukan abubuwa ta wurin kalmarsa mai iko. Bayan ya yi tsarkakewa don zunubai, sai ya zauna a hannun daman Maɗaukaki a sama.
Oğul, Tanrı yüceliğinin parıltısı, O'nun varlığının öz görünümüdür. Güçlü sözüyle her şeyi devam ettirir. Günahlardan arınmayı sağladıktan sonra, yücelerde ulu Tanrı'nın sağında oturdu.
4 Ta haka yake da fifiko a kan mala’iku kamar yadda sunan da ya gāda ya fi nasu fifiko.
Meleklerden ne denli üstün bir adı miras aldıysa, onlardan o denli üstün oldu.
5 Gama ga wane daga cikin mala’ikun Allah ya taɓa cewa, “Kai Ɗana ne; yau na zama Uba a gare ka”? Ko kuwa, “Zan zama Ubansa, shi kuma zai zama Ɗana”?
Çünkü Tanrı meleklerin herhangi birine, “Sen benim Oğlum'sun, Bugün ben sana Baba oldum” Ya da, “Ben O'na Baba olacağım, O da bana Oğul olacak” demiş midir?
6 Haka kuma, sa’ad da Allah ya kawo ɗan farinsa a duniya ya ce, “Bari dukan mala’ikun Allah su yi masa sujada.”
Yine Tanrı ilk doğanı dünyaya gönderirken diyor ki, “Tanrı'nın bütün melekleri O'na tapınsın.”
7 Da yake magana game da mala’iku kuwa ya ce, “Ya mai da mala’ikunsa iska, bayinsa kuma harsunan wuta.”
Melekler için, “Kendi meleklerini rüzgar, Hizmetkârlarını ateş alevi yapar” diyor.
8 Amma game da Ɗan ya ce, “Kursiyinka, ya Allah, zai kasance har abada abadin, adalci kuma zai zama sandan mulkinka. (aiōn g165)
Ama Oğul için şöyle diyor: “Ey Tanrı, tahtın sonsuzluklar boyunca kalıcıdır, Egemenliğinin asası adalet asasıdır. (aiōn g165)
9 Ka ƙaunaci abin da yake daidai, ka kuma ƙi mugunta; saboda haka Allah, Allahnka, ya ɗora ka a bisan abokan zamanka, ta wurin shafan da ya yi maka da man farin ciki.”
Doğruluğu sevdin, kötülükten nefret ettin. Bunun için Tanrı, senin Tanrın, Seni sevinç yağıyla Arkadaşlarından daha çok meshetti.”
10 Ya kuma ce, “Tun da farko, ya Ubangiji, ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
Yine diyor ki, “Ya Rab, başlangıçta Dünyanın temellerini sen attın. Gökler de senin ellerinin yapıtıdır.
11 Su za su hallaka, amma kai kana nan; dukansu za su tsufa kamar riga.
Onlar yok olacak, ama sen kalıcısın. Hepsi bir giysi gibi eskiyecek.
12 Za ka naɗe su kamar mayafi, kamar riga za su sauya. Amma kai ba za ka canja ba, shekarunka kuma ba za su taɓa ƙarewa ba.”
Bir kaftan gibi düreceksin onları, Bir giysi gibi değiştirilecekler. Ama sen hep aynısın, Yılların tükenmeyecek.”
13 Ga wane daga cikin mala’iku Allah ya taɓa cewa, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka”?
Tanrı meleklerin herhangi birine, “Ben düşmanlarını Ayaklarının altına serinceye dek, Sağımda otur” demiş midir?
14 Ashe, dukan mala’iku ba ruhohi masu hidima ba ne da aka aika don su yi wa waɗanda za su gāji ceto hidima?
Bütün melekler kurtuluşu miras alacaklara hizmet etmek için gönderilen görevli ruhlar değil midir?

< Ibraniyawa 1 >