< Ibraniyawa 1 >
1 A dā Allah ya yi wa kakanni-kakanninmu magana ta bakin annabawa a lokuta dabam-dabam da kuma a hanyoyi iri-iri,
C'est à plusieurs reprises et de plusieurs manières que Dieu a autrefois parlé à nos pères par les prophètes; et, de nos jours, qui sont les derniers,
2 amma a waɗannan kwanaki a ƙarshe ya yi magana da mu ta wurin Ɗansa, wanda ya naɗa magājin dukan abubuwa, wanda kuma ta wurinsa ya halicci duniya. (aiōn )
il nous a parlé, à nous, par un Fils, qu'il a fait héritier de toutes choses et par lequel il a aussi créé le monde. (aiōn )
3 Ɗan shi ne hasken ɗaukakar Allah, shi ne kuma ainihin kamanninsa, yana riƙe da dukan abubuwa ta wurin kalmarsa mai iko. Bayan ya yi tsarkakewa don zunubai, sai ya zauna a hannun daman Maɗaukaki a sama.
Étant un reflet de sa gloire et une empreinte de son essence, soutenant toutes choses par sa puissante parole, ce Fils a accompli l'oeuvre de la purification des péchés et «...s'est assis à la droite...» de la majesté divine dans les régions célestes,
4 Ta haka yake da fifiko a kan mala’iku kamar yadda sunan da ya gāda ya fi nasu fifiko.
devenu d'autant supérieur aux anges que le nom dont il a hérité est plus éminent que le leur.
5 Gama ga wane daga cikin mala’ikun Allah ya taɓa cewa, “Kai Ɗana ne; yau na zama Uba a gare ka”? Ko kuwa, “Zan zama Ubansa, shi kuma zai zama Ɗana”?
Auquel des anges, en effet, Dieu a-t-il jamais dit: «Tu es mon Fils; Je t'ai engendré aujourd'hui», et ailleurs: «Je serai son Père, et il sera mon Fils.»
6 Haka kuma, sa’ad da Allah ya kawo ɗan farinsa a duniya ya ce, “Bari dukan mala’ikun Allah su yi masa sujada.”
Et lorsque, dans un autre passage, il introduit le premier-né dans le monde, il dit: «Que tous les anges de Dieu l'adorent.»
7 Da yake magana game da mala’iku kuwa ya ce, “Ya mai da mala’ikunsa iska, bayinsa kuma harsunan wuta.”
Quant aux anges, il en dit ceci «...Celui qui fait de ses anges des esprits Et de ses serviteurs une flamme de feu...»
8 Amma game da Ɗan ya ce, “Kursiyinka, ya Allah, zai kasance har abada abadin, adalci kuma zai zama sandan mulkinka. (aiōn )
Il dit, au contraire, du Fils: «Ton trône, Dieu, est éternel. Le sceptre de ta royauté est un sceptre de droiture. (aiōn )
9 Ka ƙaunaci abin da yake daidai, ka kuma ƙi mugunta; saboda haka Allah, Allahnka, ya ɗora ka a bisan abokan zamanka, ta wurin shafan da ya yi maka da man farin ciki.”
Tu as aimé la justice et tu as haï l'iniquité. Voilà pourquoi, Dieu, ton Dieu t'a oint D'une huile de réjouissance, de préférence à tes égaux.»
10 Ya kuma ce, “Tun da farko, ya Ubangiji, ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
Et ensuite: «C'est toi, Seigneur, qui, au commencement, as fondé la terre Et les cieux sont l'oeuvre de tes mains.
11 Su za su hallaka, amma kai kana nan; dukansu za su tsufa kamar riga.
Ils périront, toi tu restes. Ils vieilliront tous comme un manteau,
12 Za ka naɗe su kamar mayafi, kamar riga za su sauya. Amma kai ba za ka canja ba, shekarunka kuma ba za su taɓa ƙarewa ba.”
Tu les plieras comme une couverture, comme un manteau, et ils se transformeront, Mais toi tu restes le même Et tes années ne finiront pas.»
13 Ga wane daga cikin mala’iku Allah ya taɓa cewa, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka”?
Auquel des anges Dieu a-t-il jamais dit: «Assieds-toi à ma droite Jusqu'à ce que j'aie mis tes ennemis sous tes pieds comme un marchepied?»
14 Ashe, dukan mala’iku ba ruhohi masu hidima ba ne da aka aika don su yi wa waɗanda za su gāji ceto hidima?
Les anges ne sont-ils pas tous des esprits subalternes, employés au service de Dieu, pour ceux qui doivent hériter du salut?