< Ibraniyawa 1 >

1 A dā Allah ya yi wa kakanni-kakanninmu magana ta bakin annabawa a lokuta dabam-dabam da kuma a hanyoyi iri-iri,
Dieu, ayant autrefois, en plusieurs temps et de diverses manières, parlé aux pères par les prophètes,
2 amma a waɗannan kwanaki a ƙarshe ya yi magana da mu ta wurin Ɗansa, wanda ya naɗa magājin dukan abubuwa, wanda kuma ta wurinsa ya halicci duniya. (aiōn g165)
nous a parlé, à la fin de ces jours, par son Fils, qu'il a établi héritier de toutes choses, par lequel il a aussi créé le monde. (aiōn g165)
3 Ɗan shi ne hasken ɗaukakar Allah, shi ne kuma ainihin kamanninsa, yana riƙe da dukan abubuwa ta wurin kalmarsa mai iko. Bayan ya yi tsarkakewa don zunubai, sai ya zauna a hannun daman Maɗaukaki a sama.
Son Fils est le rayonnement de sa gloire, l'image même de sa substance, et il soutient toutes choses par la parole de sa puissance; après nous avoir purifiés par lui-même de nos péchés, il s'est assis à la droite de la majesté des cieux,
4 Ta haka yake da fifiko a kan mala’iku kamar yadda sunan da ya gāda ya fi nasu fifiko.
étant devenu aussi supérieur aux anges que le nom plus excellent dont il a hérité est supérieur au leur.
5 Gama ga wane daga cikin mala’ikun Allah ya taɓa cewa, “Kai Ɗana ne; yau na zama Uba a gare ka”? Ko kuwa, “Zan zama Ubansa, shi kuma zai zama Ɗana”?
Car auquel des anges a-t-il jamais dit, « Tu es mon fils. Aujourd'hui, je suis devenu ton père? » et encore, « Je serai pour lui un Père, et il sera pour moi un Fils? »
6 Haka kuma, sa’ad da Allah ya kawo ɗan farinsa a duniya ya ce, “Bari dukan mala’ikun Allah su yi masa sujada.”
Lorsqu'il introduit à nouveau le premier-né dans le monde, il dit: « Que tous les anges de Dieu se prosternent devant lui. »
7 Da yake magana game da mala’iku kuwa ya ce, “Ya mai da mala’ikunsa iska, bayinsa kuma harsunan wuta.”
Des anges, il dit, « Il fait des vents à ses anges, et ses serviteurs une flamme de feu. »
8 Amma game da Ɗan ya ce, “Kursiyinka, ya Allah, zai kasance har abada abadin, adalci kuma zai zama sandan mulkinka. (aiōn g165)
Mais il dit du Fils, « Ton trône, ô Dieu, est pour les siècles des siècles. Le sceptre de la droiture est le sceptre de votre Royaume. (aiōn g165)
9 Ka ƙaunaci abin da yake daidai, ka kuma ƙi mugunta; saboda haka Allah, Allahnka, ya ɗora ka a bisan abokan zamanka, ta wurin shafan da ya yi maka da man farin ciki.”
Tu as aimé la justice et haï l'iniquité; C'est pourquoi Dieu, ton Dieu, t'a oint d'une huile de jubilation au-dessus de tes semblables. »
10 Ya kuma ce, “Tun da farko, ya Ubangiji, ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
Et, « Toi, Seigneur, au commencement, tu as posé les fondements de la terre. Les cieux sont l'œuvre de tes mains.
11 Su za su hallaka, amma kai kana nan; dukansu za su tsufa kamar riga.
Ils vont périr, mais toi tu continues. Ils vieilliront tous comme un vêtement.
12 Za ka naɗe su kamar mayafi, kamar riga za su sauya. Amma kai ba za ka canja ba, shekarunka kuma ba za su taɓa ƙarewa ba.”
Tu les enrouleras comme un manteau, et ils seront changés; mais tu es le même. Vos années ne manqueront pas. »
13 Ga wane daga cikin mala’iku Allah ya taɓa cewa, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka”?
Mais lequel des anges a-t-il dit à un moment donné, « Assieds-toi à ma droite, jusqu'à ce que je fasse de tes ennemis le marchepied de tes pieds? »
14 Ashe, dukan mala’iku ba ruhohi masu hidima ba ne da aka aika don su yi wa waɗanda za su gāji ceto hidima?
Ne sont-ils pas tous des esprits serviteurs, envoyés pour servir ceux qui doivent hériter du salut?

< Ibraniyawa 1 >