< Ibraniyawa 1 >

1 A dā Allah ya yi wa kakanni-kakanninmu magana ta bakin annabawa a lokuta dabam-dabam da kuma a hanyoyi iri-iri,
God, that spak sum tyme bi prophetis in many maneres to oure fadris, at the
2 amma a waɗannan kwanaki a ƙarshe ya yi magana da mu ta wurin Ɗansa, wanda ya naɗa magājin dukan abubuwa, wanda kuma ta wurinsa ya halicci duniya. (aiōn g165)
laste in these daies he hath spoke to vs bi the sone; whom he hath ordeyned eir of alle thingis, and bi whom he made the worldis. (aiōn g165)
3 Ɗan shi ne hasken ɗaukakar Allah, shi ne kuma ainihin kamanninsa, yana riƙe da dukan abubuwa ta wurin kalmarsa mai iko. Bayan ya yi tsarkakewa don zunubai, sai ya zauna a hannun daman Maɗaukaki a sama.
Which whanne also he is the briytnesse of glorie, and figure of his substaunce, and berith alle thingis bi word of his vertu, he makith purgacioun of synnes, and syttith on the riythalf of the maieste in heuenes;
4 Ta haka yake da fifiko a kan mala’iku kamar yadda sunan da ya gāda ya fi nasu fifiko.
and so myche is maad betere than aungels, bi hou myche he hath eneritid a more dyuerse name bifor hem.
5 Gama ga wane daga cikin mala’ikun Allah ya taɓa cewa, “Kai Ɗana ne; yau na zama Uba a gare ka”? Ko kuwa, “Zan zama Ubansa, shi kuma zai zama Ɗana”?
For to whiche of the aungels seide God ony tyme, Thou art my sone, Y haue gendrid thee to dai? And eftsoone, Y schal be to hym in to a fadir, and he schal be to me in to a sone?
6 Haka kuma, sa’ad da Allah ya kawo ɗan farinsa a duniya ya ce, “Bari dukan mala’ikun Allah su yi masa sujada.”
And whanne eftsoone he bryngith in the firste bigetun sone in to the world, he seith, And alle the aungels of God worschipe hym.
7 Da yake magana game da mala’iku kuwa ya ce, “Ya mai da mala’ikunsa iska, bayinsa kuma harsunan wuta.”
But he seith to aungels, He that makith hise aungels spiritis, and hise mynystris flawme of fier.
8 Amma game da Ɗan ya ce, “Kursiyinka, ya Allah, zai kasance har abada abadin, adalci kuma zai zama sandan mulkinka. (aiōn g165)
But to the sone he seith, God, thi trone is in to the world of world; a yerde of equite is the yerde of thi rewme; (aiōn g165)
9 Ka ƙaunaci abin da yake daidai, ka kuma ƙi mugunta; saboda haka Allah, Allahnka, ya ɗora ka a bisan abokan zamanka, ta wurin shafan da ya yi maka da man farin ciki.”
thou hast louyd riytwisnesse, and hatidist wickidnesse; therfor the God, thi God, anoyntide thee with oile of ioye, more than thi felowis.
10 Ya kuma ce, “Tun da farko, ya Ubangiji, ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
And, Thou, Lord, in the bigynnyng foundidist the erthe, and heuenes ben werkis of thin hondis; thei schulen perische,
11 Su za su hallaka, amma kai kana nan; dukansu za su tsufa kamar riga.
but thou schalt perfitli dwelle; and alle schulen wexe elde as a cloth, and thou schalt chaunge hem as a cloth,
12 Za ka naɗe su kamar mayafi, kamar riga za su sauya. Amma kai ba za ka canja ba, shekarunka kuma ba za su taɓa ƙarewa ba.”
and thei schulen be chaungid. But thou art the same thi silf, and thi yeeris schulen not faile.
13 Ga wane daga cikin mala’iku Allah ya taɓa cewa, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka”?
But to whiche of the aungels seide God at ony tyme, Sitte thou on my riythalf, till Y putte thin enemyes a stool of thi feet?
14 Ashe, dukan mala’iku ba ruhohi masu hidima ba ne da aka aika don su yi wa waɗanda za su gāji ceto hidima?
Whether thei alle ben not seruynge spiritis, sente to seruen for hem that taken the eritage of heelthe?

< Ibraniyawa 1 >