< Ibraniyawa 1 >
1 A dā Allah ya yi wa kakanni-kakanninmu magana ta bakin annabawa a lokuta dabam-dabam da kuma a hanyoyi iri-iri,
In manifold portions and in all manners, spake Aloha with our fathers by the prophets from the first: but in these last days he hath spoken with us by his Son;
2 amma a waɗannan kwanaki a ƙarshe ya yi magana da mu ta wurin Ɗansa, wanda ya naɗa magājin dukan abubuwa, wanda kuma ta wurinsa ya halicci duniya. (aiōn )
whom he constituted the heir of every thing, and by whom he made the worlds; (aiōn )
3 Ɗan shi ne hasken ɗaukakar Allah, shi ne kuma ainihin kamanninsa, yana riƙe da dukan abubuwa ta wurin kalmarsa mai iko. Bayan ya yi tsarkakewa don zunubai, sai ya zauna a hannun daman Maɗaukaki a sama.
who himself is the resplendence of his glory, and the image of his Being, and upholdeth all (things) by the power of his word; and he, in his (own) person, hath made purification of sins, and hath sat down at the right hand of the Majesty on high.
4 Ta haka yake da fifiko a kan mala’iku kamar yadda sunan da ya gāda ya fi nasu fifiko.
And this (person) is altogether more excellent than the angels, by so much as the name he hath inherited (is) more excellent than theirs.
5 Gama ga wane daga cikin mala’ikun Allah ya taɓa cewa, “Kai Ɗana ne; yau na zama Uba a gare ka”? Ko kuwa, “Zan zama Ubansa, shi kuma zai zama Ɗana”?
For unto which one from (among) the angels at any time said Aloha, Thou art MY SON; I to-day have begotten thee? And again, I will be to him the Father, and he shall be to me the Son?
6 Haka kuma, sa’ad da Allah ya kawo ɗan farinsa a duniya ya ce, “Bari dukan mala’ikun Allah su yi masa sujada.”
But again, when bringing in the First-begotten into the world, he said, Let all the angels of Aloha worship him.
7 Da yake magana game da mala’iku kuwa ya ce, “Ya mai da mala’ikunsa iska, bayinsa kuma harsunan wuta.”
But concerning the angels, thus hath he spoken: Who hath made his angels spirit, and his ministers a flaming fire.
8 Amma game da Ɗan ya ce, “Kursiyinka, ya Allah, zai kasance har abada abadin, adalci kuma zai zama sandan mulkinka. (aiōn )
But concerning the Son he hath said, Thy throne, Aloha, (is) for ever and ever, a right sceptre (is) the sceptre of thy kingdom. (aiōn )
9 Ka ƙaunaci abin da yake daidai, ka kuma ƙi mugunta; saboda haka Allah, Allahnka, ya ɗora ka a bisan abokan zamanka, ta wurin shafan da ya yi maka da man farin ciki.”
Thou hast loved righteousness, and hast hated iniquity; therefore Aloha thy God hath anointed thee with the oil of exultation more (abundantly) than thy fellows.
10 Ya kuma ce, “Tun da farko, ya Ubangiji, ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
And again, Thou in the beginning hast laid the foundations of the earth, and the heavens are the work of thy hands.
11 Su za su hallaka, amma kai kana nan; dukansu za su tsufa kamar riga.
They pass away, but thou art enduring; and all they as vestments shall become old,
12 Za ka naɗe su kamar mayafi, kamar riga za su sauya. Amma kai ba za ka canja ba, shekarunka kuma ba za su taɓa ƙarewa ba.”
and as a garment thou shalt fold them up, they shall be changed; but thou (shalt be) as Thou Art, and thy years shall not fail
13 Ga wane daga cikin mala’iku Allah ya taɓa cewa, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka”?
But to which from (among) the angels hath he said at any time, Sit at my right hand, until I put thine adversaries a footstool beneath thy feet?
14 Ashe, dukan mala’iku ba ruhohi masu hidima ba ne da aka aika don su yi wa waɗanda za su gāji ceto hidima?
Are not all they spirits of ministration, who (are) sent forth in service on behalf of those who are hereafter to inherit salvation?