< Ibraniyawa 1 >

1 A dā Allah ya yi wa kakanni-kakanninmu magana ta bakin annabawa a lokuta dabam-dabam da kuma a hanyoyi iri-iri,
God, who at several times and in divers manners spoke in time past unto the fathers by the prophets,
2 amma a waɗannan kwanaki a ƙarshe ya yi magana da mu ta wurin Ɗansa, wanda ya naɗa magājin dukan abubuwa, wanda kuma ta wurinsa ya halicci duniya. (aiōn g165)
Has in these last days spoken unto us by his Son, whom he has appointed heir of all things, by whom also he made the worlds; (aiōn g165)
3 Ɗan shi ne hasken ɗaukakar Allah, shi ne kuma ainihin kamanninsa, yana riƙe da dukan abubuwa ta wurin kalmarsa mai iko. Bayan ya yi tsarkakewa don zunubai, sai ya zauna a hannun daman Maɗaukaki a sama.
Who being the brightness of his glory, and the express image of his person, and upholding all things by the word (rhema) of his power, when he had by himself purged our sins, sat down on the right hand of the Majesty on high:
4 Ta haka yake da fifiko a kan mala’iku kamar yadda sunan da ya gāda ya fi nasu fifiko.
Being made so much better than the angels, as he has by inheritance obtained a more excellent name than they.
5 Gama ga wane daga cikin mala’ikun Allah ya taɓa cewa, “Kai Ɗana ne; yau na zama Uba a gare ka”? Ko kuwa, “Zan zama Ubansa, shi kuma zai zama Ɗana”?
For unto which of the angels said he at any time, You are my Son, this day have I begotten you? And again, I will be to him a Father, and he shall be to me a Son?
6 Haka kuma, sa’ad da Allah ya kawo ɗan farinsa a duniya ya ce, “Bari dukan mala’ikun Allah su yi masa sujada.”
And again, when he brings in the First-Born into the world, he says, And let all the angels of God worship him.
7 Da yake magana game da mala’iku kuwa ya ce, “Ya mai da mala’ikunsa iska, bayinsa kuma harsunan wuta.”
And of the angels he says, Who makes his angels spirits, (pneuma) and his ministers a flame of fire.
8 Amma game da Ɗan ya ce, “Kursiyinka, ya Allah, zai kasance har abada abadin, adalci kuma zai zama sandan mulkinka. (aiōn g165)
But unto the Son he says, Your throne, O God, is for ever and ever: a sceptre of righteousness is the sceptre of your kingdom. (aiōn g165)
9 Ka ƙaunaci abin da yake daidai, ka kuma ƙi mugunta; saboda haka Allah, Allahnka, ya ɗora ka a bisan abokan zamanka, ta wurin shafan da ya yi maka da man farin ciki.”
You have loved righteousness, and hated iniquity; therefore God, even your God, has anointed you with the oil of gladness above your fellows.
10 Ya kuma ce, “Tun da farko, ya Ubangiji, ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
And, You, Lord, in the beginning have laid the foundation of the earth; and the heavens are the works of your hands:
11 Su za su hallaka, amma kai kana nan; dukansu za su tsufa kamar riga.
They shall perish; but you remain; and they all shall wax old as does a garment;
12 Za ka naɗe su kamar mayafi, kamar riga za su sauya. Amma kai ba za ka canja ba, shekarunka kuma ba za su taɓa ƙarewa ba.”
And as a vesture shall you fold them up, and they shall be changed: but you are the same, and your years shall not fail.
13 Ga wane daga cikin mala’iku Allah ya taɓa cewa, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka”?
But to which of the angels said he at any time, Sit on my right hand, until I make your enemies your footstool?
14 Ashe, dukan mala’iku ba ruhohi masu hidima ba ne da aka aika don su yi wa waɗanda za su gāji ceto hidima?
Are they not all ministering spirits, (pneuma) sent forth to minister for them who shall be heirs of salvation?

< Ibraniyawa 1 >