< Ibraniyawa 1 >

1 A dā Allah ya yi wa kakanni-kakanninmu magana ta bakin annabawa a lokuta dabam-dabam da kuma a hanyoyi iri-iri,
God, who in the past spoke to our forefathers through the prophets at various times and in many ways,
2 amma a waɗannan kwanaki a ƙarshe ya yi magana da mu ta wurin Ɗansa, wanda ya naɗa magājin dukan abubuwa, wanda kuma ta wurinsa ya halicci duniya. (aiōn g165)
has in these last days spoken to us through his Son. God appointed the Son heir of everything, and made the universe through him. (aiōn g165)
3 Ɗan shi ne hasken ɗaukakar Allah, shi ne kuma ainihin kamanninsa, yana riƙe da dukan abubuwa ta wurin kalmarsa mai iko. Bayan ya yi tsarkakewa don zunubai, sai ya zauna a hannun daman Maɗaukaki a sama.
The Son is the radiant glory of God, and the visible expression of his true character. He sustains everything by his powerful command. When he had provided cleansing for sin he sat down at the right hand of the Majesty in heaven.
4 Ta haka yake da fifiko a kan mala’iku kamar yadda sunan da ya gāda ya fi nasu fifiko.
He was placed much higher than the angels since he received a greater name than them.
5 Gama ga wane daga cikin mala’ikun Allah ya taɓa cewa, “Kai Ɗana ne; yau na zama Uba a gare ka”? Ko kuwa, “Zan zama Ubansa, shi kuma zai zama Ɗana”?
God never said to any angel, “You are my Son; today I have become your Father,” or “I will be a Father to him, and he will be a Son to me.”
6 Haka kuma, sa’ad da Allah ya kawo ɗan farinsa a duniya ya ce, “Bari dukan mala’ikun Allah su yi masa sujada.”
Also, when he brought his firstborn Son into the world, he said, “Let all God's angels worship him.”
7 Da yake magana game da mala’iku kuwa ya ce, “Ya mai da mala’ikunsa iska, bayinsa kuma harsunan wuta.”
Regarding the angels, he says, “He makes his angels winds, and his servants flames of fire,”
8 Amma game da Ɗan ya ce, “Kursiyinka, ya Allah, zai kasance har abada abadin, adalci kuma zai zama sandan mulkinka. (aiōn g165)
but about the Son he says, “Your throne, God, lasts forever and ever, and justice is the ruling scepter of your kingdom. (aiōn g165)
9 Ka ƙaunaci abin da yake daidai, ka kuma ƙi mugunta; saboda haka Allah, Allahnka, ya ɗora ka a bisan abokan zamanka, ta wurin shafan da ya yi maka da man farin ciki.”
You love what is right, and hate what is lawless. That is why God, your God, has placed you above everyone else by anointing you with the oil of joy.”
10 Ya kuma ce, “Tun da farko, ya Ubangiji, ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
“You, Lord, laid the foundations of the earth in the beginning. The heavens are the product of your hands.
11 Su za su hallaka, amma kai kana nan; dukansu za su tsufa kamar riga.
They will come to an end, but you will continue. They will wear out like clothes do,
12 Za ka naɗe su kamar mayafi, kamar riga za su sauya. Amma kai ba za ka canja ba, shekarunka kuma ba za su taɓa ƙarewa ba.”
and you will roll them up like a cloak. Like clothes, they will be changed, but you never change, and your life never ends.”
13 Ga wane daga cikin mala’iku Allah ya taɓa cewa, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka”?
But he never said to any angel, “Sit at my right hand until I place your enemies in subjection under your feet.”
14 Ashe, dukan mala’iku ba ruhohi masu hidima ba ne da aka aika don su yi wa waɗanda za su gāji ceto hidima?
What are the angels? They are beings that serve, sent out to help those who will receive salvation.

< Ibraniyawa 1 >