< Haggai 1 >

1 A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus, a rana ta fari ga watan shida, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai zuwa ga Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, gwamnan Yahuda, da kuma Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist.
I kong Darius' annet år, i den sjette måned, på den første dag i måneden, kom Herrens ord ved profeten Haggai til Serubabel, Sealtiels sønn, stattholder over Juda, og til Josva, Jehosadaks sønn, ypperstepresten, og det lød så:
2 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Waɗannan mutane sun ce, ‘Lokaci bai yi ba tukuna da za a gina gidan Ubangiji.’”
Så sier Herren, hærskarenes Gud: Dette folk sier: Det er ennu ikke tid til å komme, tid til å bygge Herrens hus.
3 Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
Så kom da Herrens ord ved profeten Haggai:
4 “Ashe, lokaci ya yi da za ku zauna a ɗakunan da kuka yi da rufin katako, amma haikalin nan yana zaman kufai?”
Er det tid for eder til å bo i eders bordklædde hus, mens dette hus ligger øde?
5 To, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
Og nu sier Herren, hærskarenes Gud, så: Legg merke til hvorledes det går eder!
6 Kun shuka da yawa, amma kun girbe kaɗan. Kun ci, amma ba ku ƙoshi ba. Kun sha, amma ba ku kashe ƙishirwa ba. Kun sa tufafi, amma ba ku ji ɗumi ba. Kuna karɓar albashi, ya zama sai ka ce kuna zuba a hudajjen aljihu.”
I sår meget, men høster lite i hus; I eter, men blir ikke mette; I drikker, men blir ikke utørste; I klær eder, men ingen blir varm, og den som tjener for lønn, får sin lønn i en hullet pung.
7 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
Så sier Herren, hærskarenes Gud: Legg merke til hvorledes det går eder!
8 Ku haura zuwa kan duwatsu ku sauko da katakai don ku gina gidan, don ni ma in ji daɗinsa, in kuma sami ɗaukaka,” in ji Ubangiji.
Gå op i fjellene og hent tømmer og bygg huset! Så vil jeg ha velbehag i det og herliggjøre mig, sier Herren.
9 “Ga shi, kukan sa rai za ku sami da yawa, amma sai ku ga kun sami kaɗan. Ɗan kaɗan ɗin ma da kukan kawo gida, nakan hura shi yă tafi. Me ya sa yake faruwa haka?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Saboda gidana da yake zaman kango, yayinda kowannenku yana faman gina gidansa.
I venter meget, og se, det blir til lite, og når I bærer det i hus, så blåser jeg det bort. Hvorfor? sier Herren, hærskarenes Gud. Fordi mitt hus ligger øde, mens I har det travelt hver med sitt hus.
10 Shi ya sa, saboda ku sammai sun ƙi saukar da raɓa, ƙasa kuma ta ƙi ba da amfani.
Derfor har himmelen lukket sig over eder, så den ikke gir dugg, og jorden har holdt sin grøde tilbake.
11 Na kawo fări a ƙasar, da a kan duwatsu, da a kan hatsi, da a kan dukan abin da yake tsirowa daga ƙasa, da a kan mutane, da a kan dabbobi da kuma a kan wahalar hannuwanku.”
Og jeg har kalt tørke hit over landet og fjellene, over kornet og mosten og oljen og alt det som jorden bærer, og over folk og fe og over alt eders henders arbeid.
12 Sa’an nan sai Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, wanda yake babban firist, da kuma dukan raguwar jama’ar suka yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnsu da kuma saƙon annabi Haggai, domin Ubangiji Allahnsu ne ya aiko shi. Mutane kuwa suka ji tsoron Ubangiji.
Og Serubabel, Sealtiels sønn, og Josva, Jehosadaks sønn, ypperstepresten, og alle som var igjen av folket, hørte på Herrens, sin Guds røst og på profeten Haggais ord, fordi Herren deres Gud hadde sendt ham, og folket fryktet for Herren.
13 Sai Haggai, ɗan saƙon Ubangiji, ya ba da wannan saƙo na Ubangiji ga mutane cewa, “Ina tare da ku” in ji Ubangiji.
Da sa Haggai, Herrens sendebud, i Herrens ærend til folket: Jeg er med eder, sier Herren.
14 Saboda haka Ubangiji ya motsa zuciyar Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, wanda yake gwamna a Yahuda, da kuma zuciyar Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma zukatan dukan raguwar jama’ar. Suka zo suka fara aiki a gidan Ubangiji Maɗaukaki, Allahnsu,
Og Herren vakte slik iver hos Serubabel, Sealtiels sønn, stattholderen over Juda, og hos Josva, Jehosadaks sønn, ypperstepresten, og hos hele det folk som var blitt igjen, at de kom og arbeidet på Herrens, sin Guds, hærskarenes Guds hus;
15 a ranar ashirin da huɗu ga watan shida. A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus,
det var på den fire og tyvende dag i måneden, i den sjette måned i kong Darius' annet år.

< Haggai 1 >