< Haggai 1 >

1 A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus, a rana ta fari ga watan shida, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai zuwa ga Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, gwamnan Yahuda, da kuma Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist.
Ķēniņa Dārija otrā gadā, sestā mēnesi, pirmā mēneša dienā, Tā Kunga vārds notika caur pravieti Hagaju uz Zerubabeli Šealtiēļa dēlu, Jūda valdnieku, un uz Jozua, Jocadaka dēlu, augsto priesteri, un sacīja:
2 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Waɗannan mutane sun ce, ‘Lokaci bai yi ba tukuna da za a gina gidan Ubangiji.’”
Tā runā Tas Kungs Cebaot un saka: šie ļaudis runā: laiks vēl nav nācis, uzcelt Tā Kunga namu.
3 Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
Un Tā Kunga vārds notika caur pravieti Hagaju sacīdams:
4 “Ashe, lokaci ya yi da za ku zauna a ɗakunan da kuka yi da rufin katako, amma haikalin nan yana zaman kufai?”
Vai tad jums ir laiks, dzīvot glītos namos un šim namam būs stāvēt postā?
5 To, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
Nu tad tā saka Tas Kungs Cebaot: ņemat vērā savus ceļus.
6 Kun shuka da yawa, amma kun girbe kaɗan. Kun ci, amma ba ku ƙoshi ba. Kun sha, amma ba ku kashe ƙishirwa ba. Kun sa tufafi, amma ba ku ji ɗumi ba. Kuna karɓar albashi, ya zama sai ka ce kuna zuba a hudajjen aljihu.”
Jūs sējat daudz un pļaujat maz, jūs ēdat, bet nepaēdat, jūs dzerat bet nepadzerat, jūs ģērbjaties, bet jums nepaliek silti, un algādzis pelna algu cauram makam.
7 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
Tā saka Tas Kungs Cebaot: liekat vērā savus ceļus.
8 Ku haura zuwa kan duwatsu ku sauko da katakai don ku gina gidan, don ni ma in ji daɗinsa, in kuma sami ɗaukaka,” in ji Ubangiji.
Ejat augšā kalnos un vediet kokus un uztaisiet šo namu; pie tā Man būs labs prāts, un Es tapšu pagodināts, saka Tas Kungs.
9 “Ga shi, kukan sa rai za ku sami da yawa, amma sai ku ga kun sami kaɗan. Ɗan kaɗan ɗin ma da kukan kawo gida, nakan hura shi yă tafi. Me ya sa yake faruwa haka?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Saboda gidana da yake zaman kango, yayinda kowannenku yana faman gina gidansa.
Jūs gan gaidāt uz daudz, bet redzi, jūs dabūjat maz, un jebšu jūs to esat mājās pārnesuši, taču Es to izputināju. Kāpēc tā? saka Tas Kungs Cebaot. Mana nama labad, kas stāv postā, kamēr ikviens skrien sava nama labad.
10 Shi ya sa, saboda ku sammai sun ƙi saukar da raɓa, ƙasa kuma ta ƙi ba da amfani.
Tādēļ debess jums aiztur rasu, un zeme aiztur savus augļus.
11 Na kawo fări a ƙasar, da a kan duwatsu, da a kan hatsi, da a kan dukan abin da yake tsirowa daga ƙasa, da a kan mutane, da a kan dabbobi da kuma a kan wahalar hannuwanku.”
Un sausumu Es saucu(sūtu) pār zemi un pār kalniem un pār labību un pār vīnu un pār eļļu un pār visu, kas izaug no zemes, un pār cilvēkiem un pār lopiem un pār ikvienu rokas darbu.
12 Sa’an nan sai Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, wanda yake babban firist, da kuma dukan raguwar jama’ar suka yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnsu da kuma saƙon annabi Haggai, domin Ubangiji Allahnsu ne ya aiko shi. Mutane kuwa suka ji tsoron Ubangiji.
Tad Zerubabels, Šealtiēļa dēls, un Jozuas, Jocadaka dēls, augstais priesteris, un visi atlikušie ļaudis klausīja Tā Kunga, sava Dieva, balsij un pravieša Hagaja vārdiem it(tieši) kā Tas Kungs, viņu Dievs, to bija sūtījis, un tie ļaudis bijās no Tā Kunga.
13 Sai Haggai, ɗan saƙon Ubangiji, ya ba da wannan saƙo na Ubangiji ga mutane cewa, “Ina tare da ku” in ji Ubangiji.
Tad sacīja Hagaja, Tā Kunga vēstnesis, kam Tā Kunga vēsts bija uz tiem ļaudīm: Es esmu ar jums, saka Tas Kungs.
14 Saboda haka Ubangiji ya motsa zuciyar Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, wanda yake gwamna a Yahuda, da kuma zuciyar Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma zukatan dukan raguwar jama’ar. Suka zo suka fara aiki a gidan Ubangiji Maɗaukaki, Allahnsu,
Un Tas Kungs pamodināja Zerubabela, Šealtiēļa dēla, Jūdas ķēniņa garu un Jozuas, Jocadaka dēla, augstā priestera garu un visu atlikušo ļaužu garu, ka tie gāja un darīja darbu pie Tā Kunga Cebaot, sava Dieva, nama,
15 a ranar ashirin da huɗu ga watan shida. A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus,
Sestā mēneša divdesmit ceturtā dienā ķēniņa Dārija otrā gadā.

< Haggai 1 >