< Haggai 1 >

1 A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus, a rana ta fari ga watan shida, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai zuwa ga Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, gwamnan Yahuda, da kuma Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist.
En la seconde année du roi Darius, au sixième mois, au premier jour du mois, la parole du Seigneur fut adressée, par l’entremise d’Aggée, le prophète, à Zorobabel, chef de Juda, fils de Salathiel, et à Jésus, le grand-prêtre, fils de Josédec, disant:
2 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Waɗannan mutane sun ce, ‘Lokaci bai yi ba tukuna da za a gina gidan Ubangiji.’”
Voici ce que dit le Seigneur des armées: Ce peuple dit: Il n’est pas encore venu, le temps de bâtir la maison du Seigneur.
3 Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
Et la parole du Seigneur fut adressée par l’entremise d’Aggée, le prophète, disant:
4 “Ashe, lokaci ya yi da za ku zauna a ɗakunan da kuka yi da rufin katako, amma haikalin nan yana zaman kufai?”
Est-ce qu’il est temps pour vous d’habiter dans des maisons lambrissées, quand cette maison est déserte?
5 To, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
Et maintenant, voici ce que dit le Seigneur des armées: Appliquez vos cœurs à vos voies.
6 Kun shuka da yawa, amma kun girbe kaɗan. Kun ci, amma ba ku ƙoshi ba. Kun sha, amma ba ku kashe ƙishirwa ba. Kun sa tufafi, amma ba ku ji ɗumi ba. Kuna karɓar albashi, ya zama sai ka ce kuna zuba a hudajjen aljihu.”
Vous avez semé beaucoup, et vous avez peu recueilli; vous avez mangé, et vous n’avez pas été rassasiés; vous avez bu, et vous n’avez pas été désaltérés; vous vous êtes couverts, et vous ne vous êtes pas réchauffés; et celui qui a accumulé des profits les a mis dans un sac percé.
7 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
Voici ce que dit le Seigneur des armées: Appliquez vos cœurs à vos voies.
8 Ku haura zuwa kan duwatsu ku sauko da katakai don ku gina gidan, don ni ma in ji daɗinsa, in kuma sami ɗaukaka,” in ji Ubangiji.
Montez sur la montagne, portez des bois, et bâtissez la maison, et elle me sera agréable, et je serai glorifié, dit le Seigneur.
9 “Ga shi, kukan sa rai za ku sami da yawa, amma sai ku ga kun sami kaɗan. Ɗan kaɗan ɗin ma da kukan kawo gida, nakan hura shi yă tafi. Me ya sa yake faruwa haka?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Saboda gidana da yake zaman kango, yayinda kowannenku yana faman gina gidansa.
Vous avez espéré plus, et il arrive moins; ce peu, vous l’ avez apporté dans votre maison, et j’ai soufflé dessus; pour quel motif, dit le Seigneur des armées? parce que ma maison est déserte, et que chacun de vous se hâte pour la sienne.
10 Shi ya sa, saboda ku sammai sun ƙi saukar da raɓa, ƙasa kuma ta ƙi ba da amfani.
C’est pour cela qu’au-dessus de vous il a été défendu aux cieux de donner de la rosée, et qu’à la terre il a été défendu de donner ses productions.
11 Na kawo fări a ƙasar, da a kan duwatsu, da a kan hatsi, da a kan dukan abin da yake tsirowa daga ƙasa, da a kan mutane, da a kan dabbobi da kuma a kan wahalar hannuwanku.”
Et j’ai appelé la sécheresse sur la terre, et sur les montagnes, et sur le blé, et sur le vin, et sur l’huile, et sur tout ce que produit la terre, et sur les hommes, et sur les bêtes, et sur tous les travaux de vos mains.
12 Sa’an nan sai Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, wanda yake babban firist, da kuma dukan raguwar jama’ar suka yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnsu da kuma saƙon annabi Haggai, domin Ubangiji Allahnsu ne ya aiko shi. Mutane kuwa suka ji tsoron Ubangiji.
Et Zorobabel, fils de Salathiel, et Jésus, fus de Josédec, le grand-prêtre, et tous ceux qui étaient restés du peuple, entendirent la voix du Seigneur leur Dieu, et les paroles d’Aggée, le prophète, qu’envoya vers eux le Seigneur leur Dieu; et le peuple fut saisi de crainte devant la face du Seigneur.
13 Sai Haggai, ɗan saƙon Ubangiji, ya ba da wannan saƙo na Ubangiji ga mutane cewa, “Ina tare da ku” in ji Ubangiji.
Et Aggée, envoyé du Seigneur dans les messages du Seigneur, parla, disant au peuple: Moi, je suis avec vous, dit le Seigneur.
14 Saboda haka Ubangiji ya motsa zuciyar Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, wanda yake gwamna a Yahuda, da kuma zuciyar Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma zukatan dukan raguwar jama’ar. Suka zo suka fara aiki a gidan Ubangiji Maɗaukaki, Allahnsu,
Et le Seigneur suscita l’esprit de Zorobabel, fils de Salathiel, chef de Juda, et l’esprit de Jésus, fils de Josédec, le grand prêtre, et l’esprit de tous ceux qui étaient restés du peuple, et ils entrèrent dans le temple, et ils travaillaient dans la maison du Seigneur des armées leur Dieu.
15 a ranar ashirin da huɗu ga watan shida. A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus,
Au vingt-quatrième jour, au sixième mois, en la seconde année du roi Darius;

< Haggai 1 >