< Haggai 1 >
1 A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus, a rana ta fari ga watan shida, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai zuwa ga Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, gwamnan Yahuda, da kuma Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist.
En la sixième année du règne de Darius, le sixième mois, le premier jour du mois, la parole du Seigneur vint à Aggée, le prophète, disant: Parle à Zorobabel, fils de Salathiel, de la tribu de Juda, et à Jésus, fils de Josédec, le grand prêtre, et dis:
2 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Waɗannan mutane sun ce, ‘Lokaci bai yi ba tukuna da za a gina gidan Ubangiji.’”
Voici ce que dit le Seigneur Tout-Puissant. Ils disent que le temps n'est pas venu de réédifier la maison du Seigneur.
3 Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
Or la parole du Seigneur est venue à Aggée, le prophète, disant:
4 “Ashe, lokaci ya yi da za ku zauna a ɗakunan da kuka yi da rufin katako, amma haikalin nan yana zaman kufai?”
Le temps est-il venu pour vous de demeurer en vos maisons lambrissées en voûte, quand Notre temple est désert?
5 To, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
Et maintenant, voici ce que dit le Seigneur tout-puissant. Dirigez vos cœurs en vos voies.
6 Kun shuka da yawa, amma kun girbe kaɗan. Kun ci, amma ba ku ƙoshi ba. Kun sha, amma ba ku kashe ƙishirwa ba. Kun sa tufafi, amma ba ku ji ɗumi ba. Kuna karɓar albashi, ya zama sai ka ce kuna zuba a hudajjen aljihu.”
Vous avez semé beaucoup, et peu recueilli; vous avez mangé, mais pas à satiété; vous avez bu, mais point jusqu'à l'ivresse; vous vous êtes vêtus, et vous n'avez pas été réchauffés; et celui qui a thésaurisé ses salaires, les a déposés dans un sac troué.
7 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
Or voici ce que dit le Seigneur tout-puissant. Dirigez vos cœurs en vos voies;
8 Ku haura zuwa kan duwatsu ku sauko da katakai don ku gina gidan, don ni ma in ji daɗinsa, in kuma sami ɗaukaka,” in ji Ubangiji.
montez sur la montagne; abattez des arbres, et réédifiez le temple; et Je M'y complairai, et Je serai glorifié, dit le Seigneur.
9 “Ga shi, kukan sa rai za ku sami da yawa, amma sai ku ga kun sami kaɗan. Ɗan kaɗan ɗin ma da kukan kawo gida, nakan hura shi yă tafi. Me ya sa yake faruwa haka?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Saboda gidana da yake zaman kango, yayinda kowannenku yana faman gina gidansa.
Vous avez convoité beaucoup, et peu vous est venu; et ce peu vous l'avez emporté en vos maisons, et d'un souffle Je l'en ai fait sortir; c'est pourquoi voici ce que dit le Seigneur tout-puissant: En punition de ce que Ma demeure est déserte, et que chacun de vous court à sa demeure,
10 Shi ya sa, saboda ku sammai sun ƙi saukar da raɓa, ƙasa kuma ta ƙi ba da amfani.
le ciel vous refusera sa rosée, et la terre vous retirera ses fruits.
11 Na kawo fări a ƙasar, da a kan duwatsu, da a kan hatsi, da a kan dukan abin da yake tsirowa daga ƙasa, da a kan mutane, da a kan dabbobi da kuma a kan wahalar hannuwanku.”
Et Je ferai passer un glaive sur la terre et sur les montagnes, sur le blé et sur le vin, sur l'huile et sur les fruits de la terre, sur les hommes, leur bétail et tous les travaux de leurs mains.
12 Sa’an nan sai Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, wanda yake babban firist, da kuma dukan raguwar jama’ar suka yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnsu da kuma saƙon annabi Haggai, domin Ubangiji Allahnsu ne ya aiko shi. Mutane kuwa suka ji tsoron Ubangiji.
Et Zorobabel, fils de Salathiel, de la tribu de Juda, et Jésus, fils de Josédec, le grand prêtre, et tout le reste du peuple entendirent la voix du Seigneur leur Dieu, et les paroles d'Aggée, le prophète, telles que par lui le Seigneur, leur Dieu, les leur avait envoyées. Et le peuple révéra la face du Seigneur.
13 Sai Haggai, ɗan saƙon Ubangiji, ya ba da wannan saƙo na Ubangiji ga mutane cewa, “Ina tare da ku” in ji Ubangiji.
Et Aggée, le messager du Seigneur, rapporta au peuple le message du Seigneur, disant: Je suis avec vous, dit le Seigneur.
14 Saboda haka Ubangiji ya motsa zuciyar Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, wanda yake gwamna a Yahuda, da kuma zuciyar Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma zukatan dukan raguwar jama’ar. Suka zo suka fara aiki a gidan Ubangiji Maɗaukaki, Allahnsu,
Et le Seigneur suscita l'esprit de Zorobabel, fils de Salathiel, de la tribu de Juda, et l'esprit de Jésus, fils de Josédec, le grand prêtre, et l'esprit du reste du peuple; et ils entrèrent dans le temple du Seigneur, leur Dieu tout-puissant, et ils y firent des travaux.
15 a ranar ashirin da huɗu ga watan shida. A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus,
Le vingt-quatrième jour du sixième mois, la seconde année du règne de Darius;