< Haggai 1 >

1 A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus, a rana ta fari ga watan shida, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai zuwa ga Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, gwamnan Yahuda, da kuma Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist.
Dans la deuxième année du roi Darius, le sixième mois, le premier jour du mois, la parole de l’Eternel fut adressée par l’organe du prophète Haggaï à Zorobabel, fils de Chaltiël, gouverneur de Judée, et à Josué, fils de Joçadak, le grand-prêtre, en ces termes:
2 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Waɗannan mutane sun ce, ‘Lokaci bai yi ba tukuna da za a gina gidan Ubangiji.’”
"Ainsi parle l’Eternel-Cebaot, à savoir: Ce peuple dit: Le temps n’est pas venu encore de rebâtir le temple du Seigneur!"
3 Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
La parole de l’Eternel arriva par l’organe du prophète Haggaï en ces termes:
4 “Ashe, lokaci ya yi da za ku zauna a ɗakunan da kuka yi da rufin katako, amma haikalin nan yana zaman kufai?”
"Le temps est-il donc venu pour vous d’habiter vos maisons lambrissées, alors que ce temple est en ruines!
5 To, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
Or, maintenant, ainsi parle l’Eternel-Cebaot: Appliquez votre attention à votre manière d’agir!
6 Kun shuka da yawa, amma kun girbe kaɗan. Kun ci, amma ba ku ƙoshi ba. Kun sha, amma ba ku kashe ƙishirwa ba. Kun sa tufafi, amma ba ku ji ɗumi ba. Kuna karɓar albashi, ya zama sai ka ce kuna zuba a hudajjen aljihu.”
Vous avez semé beaucoup pour récolter peu, vous mangez sans être rassasiés, vous buvez sans avoir tout votre saoûl, vous mettez des vêtements, mais ils ne vous donnent pas de chaleur, et celui qui se loue pour un salaire gagne le salaire pour une bourse trouée."
7 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
Ainsi parle l’Eternel-Cebaot: "Appliquez votre attention à votre manière d’agir!
8 Ku haura zuwa kan duwatsu ku sauko da katakai don ku gina gidan, don ni ma in ji daɗinsa, in kuma sami ɗaukaka,” in ji Ubangiji.
Montez sur la montagne, rapportez-en du bois et bâtissez le temple: j’y prendrai plaisir et je m’en trouverai honoré, dit le Seigneur.
9 “Ga shi, kukan sa rai za ku sami da yawa, amma sai ku ga kun sami kaɗan. Ɗan kaɗan ɗin ma da kukan kawo gida, nakan hura shi yă tafi. Me ya sa yake faruwa haka?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Saboda gidana da yake zaman kango, yayinda kowannenku yana faman gina gidansa.
Vous comptiez sur une moisson abondante, et elle s’est réduite à peu de chose; quand vous l’avez rentrée dans votre maison, j’ai soufflé dessus. Pourquoi cela? dit l’Eternel-Cebaot. C’Est à cause de ma maison qui est en ruines, tandis que vous courez tous dans votre maison à vous.
10 Shi ya sa, saboda ku sammai sun ƙi saukar da raɓa, ƙasa kuma ta ƙi ba da amfani.
C’Est pourquoi les cieux ont retenu leur rosée à vos dépens, et la terre a refusé ses produits.
11 Na kawo fări a ƙasar, da a kan duwatsu, da a kan hatsi, da a kan dukan abin da yake tsirowa daga ƙasa, da a kan mutane, da a kan dabbobi da kuma a kan wahalar hannuwanku.”
J’Ai appelé la sécheresse sur les champs et sur les montagnes, sur le froment, le moût et l’huile, sur tout ce que fait pousser le sol; de même sur les hommes et les bêtes, sur tous les produits du travail de vos mains."
12 Sa’an nan sai Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, wanda yake babban firist, da kuma dukan raguwar jama’ar suka yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnsu da kuma saƙon annabi Haggai, domin Ubangiji Allahnsu ne ya aiko shi. Mutane kuwa suka ji tsoron Ubangiji.
Zorobabel, fils de Chaltiël, Josué, fils de Joçadak, le grand-prêtre, et tout le reste du peuple écoutèrent la voix de l’Eternel, leur Dieu, et les paroles du prophète Haggaï, dont l’avait chargé l’Eternel, leur Dieu, et le peuple témoigna sa vénération au Seigneur.
13 Sai Haggai, ɗan saƙon Ubangiji, ya ba da wannan saƙo na Ubangiji ga mutane cewa, “Ina tare da ku” in ji Ubangiji.
Or, Haggaï, envoyé de l’Eternel, en vertu de sa mission divine, parla au peuple en ces termes: "Je serai avec vous" dit l’Eternel.
14 Saboda haka Ubangiji ya motsa zuciyar Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, wanda yake gwamna a Yahuda, da kuma zuciyar Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma zukatan dukan raguwar jama’ar. Suka zo suka fara aiki a gidan Ubangiji Maɗaukaki, Allahnsu,
Et l’Eternel excita le zèle de Zorobabel, fils de Chaltiël, gouverneur de Judée, le zèle de Josué, fils de Joçadak, le grand-prêtre, et le zèle de tout le reste du peuple. Ils vinrent et se mirent à l’œuvre dans la maison de l’Eternel-Cebaot, leur Dieu.
15 a ranar ashirin da huɗu ga watan shida. A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus,
C’Était le vingt-quatrième jour du sixième mois, dans la deuxième année du roi Darius.

< Haggai 1 >