< Haggai 1 >

1 A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus, a rana ta fari ga watan shida, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai zuwa ga Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, gwamnan Yahuda, da kuma Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist.
Kuningas Daarejaveksen toisena vuotena, kuudennessa kuussa, kuukauden ensimmäisenä päivänä, tuli tämä Herran sana profeetta Haggain kautta Juudan käskynhaltijalle Serubbaabelille, Sealtielin pojalle, ja ylimmäiselle papille Joosualle, Joosadakin pojalle:
2 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Waɗannan mutane sun ce, ‘Lokaci bai yi ba tukuna da za a gina gidan Ubangiji.’”
"Näin sanoo Herra Sebaot: Tämä kansa sanoo: Aika ei ole tullut rakentaa Herran huonetta".
3 Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
Mutta profeetta Haggain kautta tuli tämä Herran sana:
4 “Ashe, lokaci ya yi da za ku zauna a ɗakunan da kuka yi da rufin katako, amma haikalin nan yana zaman kufai?”
"Onko sitten aika teidän asua panelilla kaunistetuissa huoneissanne, kun tämä huone on rauniona?
5 To, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
Ja nyt sanoo Herra Sebaot näin: Ottakaa vaari teistänne.
6 Kun shuka da yawa, amma kun girbe kaɗan. Kun ci, amma ba ku ƙoshi ba. Kun sha, amma ba ku kashe ƙishirwa ba. Kun sa tufafi, amma ba ku ji ɗumi ba. Kuna karɓar albashi, ya zama sai ka ce kuna zuba a hudajjen aljihu.”
Te kylvätte paljon, mutta saatte vähän. Te syötte, mutta ette tule ravituiksi. Te juotte, mutta jano ei sammu. Te vaatetatte itsenne, mutta ei tule lämmin. Ja palkkatyöläinen panee työpalkan reikäiseen kukkaroon.
7 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
Näin sanoo Herra Sebaot: Ottakaa vaari teistänne.
8 Ku haura zuwa kan duwatsu ku sauko da katakai don ku gina gidan, don ni ma in ji daɗinsa, in kuma sami ɗaukaka,” in ji Ubangiji.
Nouskaa vuorille, tuokaa puita ja rakentakaa temppeli, niin minä siihen mielistyn ja näytän kunniani, sanoo Herra.
9 “Ga shi, kukan sa rai za ku sami da yawa, amma sai ku ga kun sami kaɗan. Ɗan kaɗan ɗin ma da kukan kawo gida, nakan hura shi yă tafi. Me ya sa yake faruwa haka?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Saboda gidana da yake zaman kango, yayinda kowannenku yana faman gina gidansa.
Te odotatte paljoa, mutta se menee vähiin. Te tuotte kotiin, mutta minä puhallan sen pois. Minkätähden? sanoo Herra Sebaot. Minun huoneeni tähden, kun se on rauniona ja te juoksette kukin oman huoneenne hyväksi.
10 Shi ya sa, saboda ku sammai sun ƙi saukar da raɓa, ƙasa kuma ta ƙi ba da amfani.
Sentähden teiltä taivas pidättää kasteen ja maa pidättää satonsa.
11 Na kawo fări a ƙasar, da a kan duwatsu, da a kan hatsi, da a kan dukan abin da yake tsirowa daga ƙasa, da a kan mutane, da a kan dabbobi da kuma a kan wahalar hannuwanku.”
Ja minä olen kutsunut kuivuuden maahan ja vuorille, viljalle, viinille ja öljylle, ja mitä vain maa tuottaa, ja ihmisille ja eläimille ja kaikelle kätten vaivannäölle."
12 Sa’an nan sai Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, wanda yake babban firist, da kuma dukan raguwar jama’ar suka yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnsu da kuma saƙon annabi Haggai, domin Ubangiji Allahnsu ne ya aiko shi. Mutane kuwa suka ji tsoron Ubangiji.
Niin Serubbaabel, Sealtielin poika, ja ylimmäinen pappi Joosua, Joosadakin poika, ja kansan koko jäännös kuuli Herran, Jumalansa ääntä ja profeetta Haggain sanoja, jota varten Herra, heidän Jumalansa, oli hänet lähettänytkin, ja kansa pelkäsi Herraa.
13 Sai Haggai, ɗan saƙon Ubangiji, ya ba da wannan saƙo na Ubangiji ga mutane cewa, “Ina tare da ku” in ji Ubangiji.
Haggai, Herran sanansaattaja, sanoi, saattaen Herran sanan, kansalle näin: "Minä olen teidän kanssanne, sanoo Herra".
14 Saboda haka Ubangiji ya motsa zuciyar Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, wanda yake gwamna a Yahuda, da kuma zuciyar Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma zukatan dukan raguwar jama’ar. Suka zo suka fara aiki a gidan Ubangiji Maɗaukaki, Allahnsu,
Ja Herra herätti Juudan käskynhaltijan Serubbaabelin, Sealtielin pojan, hengen ja ylimmäisen papin Joosuan, Joosadakin pojan, hengen ja kansan koko jäännöksen hengen, ja he tulivat ja ryhtyivät rakentamaan Herran Sebaotin, heidän Jumalansa, temppeliä
15 a ranar ashirin da huɗu ga watan shida. A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus,
kahdentenakymmenentenä neljäntenä päivänä kuudennessa kuussa, kuningas Daarejaveksen toisena vuotena.

< Haggai 1 >