< Haggai 1 >
1 A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus, a rana ta fari ga watan shida, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai zuwa ga Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, gwamnan Yahuda, da kuma Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist.
In the second year of Darius the king, in the sixth month, on the first day of the month, a word of YHWH has been by the hand of Haggai the prophet, to Zerubbabel son of Shealtiel, governor of Judah, and to Joshua son of Josedech, the high priest, saying,
2 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Waɗannan mutane sun ce, ‘Lokaci bai yi ba tukuna da za a gina gidan Ubangiji.’”
“Thus spoke YHWH of Hosts, saying, This people—they have said, The time has not come, The time the house of YHWH [is] to be built.”
3 Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
And there is a word of YHWH by the hand of Haggai the prophet, saying,
4 “Ashe, lokaci ya yi da za ku zauna a ɗakunan da kuka yi da rufin katako, amma haikalin nan yana zaman kufai?”
“Is it time for you to dwell in your covered houses, And this house to lie waste?”
5 To, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
And now, thus said YHWH of Hosts: “Set your heart to your ways.
6 Kun shuka da yawa, amma kun girbe kaɗan. Kun ci, amma ba ku ƙoshi ba. Kun sha, amma ba ku kashe ƙishirwa ba. Kun sa tufafi, amma ba ku ji ɗumi ba. Kuna karɓar albashi, ya zama sai ka ce kuna zuba a hudajjen aljihu.”
You have sown much, and brought in little, To eat, and not to satiety, To drink, and not to drunkenness, To clothe, and none has heat, And he who is hiring himself out, Is hiring himself for a bag pierced through.”
7 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
Thus said YHWH of Hosts: “Set your heart to your ways.
8 Ku haura zuwa kan duwatsu ku sauko da katakai don ku gina gidan, don ni ma in ji daɗinsa, in kuma sami ɗaukaka,” in ji Ubangiji.
Go up the mountain, and you have brought in wood, And build the house, and I am pleased with it. And I am honored,” said YHWH.
9 “Ga shi, kukan sa rai za ku sami da yawa, amma sai ku ga kun sami kaɗan. Ɗan kaɗan ɗin ma da kukan kawo gida, nakan hura shi yă tafi. Me ya sa yake faruwa haka?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Saboda gidana da yake zaman kango, yayinda kowannenku yana faman gina gidansa.
“Looking for much, and behold, little, And you brought [it] home, and I blew on it—why?” A declaration of YHWH of Hosts, “Because of My house that is desolate, And you are running—each to his house,
10 Shi ya sa, saboda ku sammai sun ƙi saukar da raɓa, ƙasa kuma ta ƙi ba da amfani.
Therefore, over you the heavens have refrained from dew, And the land has refrained its increase.
11 Na kawo fări a ƙasar, da a kan duwatsu, da a kan hatsi, da a kan dukan abin da yake tsirowa daga ƙasa, da a kan mutane, da a kan dabbobi da kuma a kan wahalar hannuwanku.”
And I proclaim drought on the land, And on the mountains, and on the grain, And on the new wine, and on the oil, And on what the ground brings forth, And on man, and on beast, And on all labor of the hands.”
12 Sa’an nan sai Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, wanda yake babban firist, da kuma dukan raguwar jama’ar suka yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnsu da kuma saƙon annabi Haggai, domin Ubangiji Allahnsu ne ya aiko shi. Mutane kuwa suka ji tsoron Ubangiji.
And Zerubbabel son of Shealtiel, and Joshua son of Josedech, the high priest, and all the remnant of the people, listen to the voice of their God YHWH, and to the words of Haggai the prophet, as their God YHWH had sent him, and the people are afraid of the face of YHWH.
13 Sai Haggai, ɗan saƙon Ubangiji, ya ba da wannan saƙo na Ubangiji ga mutane cewa, “Ina tare da ku” in ji Ubangiji.
And Haggai, messenger of YHWH, in messages of YHWH, speaks to the people, saying, “I [am] with you, a declaration of YHWH.”
14 Saboda haka Ubangiji ya motsa zuciyar Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, wanda yake gwamna a Yahuda, da kuma zuciyar Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma zukatan dukan raguwar jama’ar. Suka zo suka fara aiki a gidan Ubangiji Maɗaukaki, Allahnsu,
And YHWH stirs up the spirit of Zerubbabel son of Shealtiel, governor of Judah, and the spirit of Joshua son of Josedech, the high priest, and the spirit of all the remnant of the people, and they come in, and work in the house of YHWH of Hosts their God,
15 a ranar ashirin da huɗu ga watan shida. A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus,
in the twenty-fourth day of the sixth month, in the second year of Darius the king.