< Haggai 2 >

1 a ranar ashirin da ɗaya ga watan bakwai, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
Niheo amy Kagày mpitokiy amy volam-pahafitoy, amy andro faha-roapolo-raik’ ambi’ i volañeiy, ty tsara’ Iehovà manao ty hoe:
2 “Ka yi magana da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel wanda yake gwamna a Yahuda, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma dukan raguwar mutane. Ka tambaye su ka ce,
anò ty hoe amy Zerobabele, ana’ i Sealtiele, naho am’ Iehosoa, ana’ Iehotsadake, mpisorom-bey, vaho amo sehanga’ondatio:
3 ‘Wane ne a cikinku ya ragu da ya ga wannan gida a darajarsa ta dā? Yaya yake a gare ku a yanzu? Bai yi kamar a bakin kome ba, ko ba haka ba?
Ia ty honka ama’ areo nahaisake ty anjomba toy amy enge’e taoloy? akore ty fahaoniña’ areo aze henanekeo? Hera tsy vente’e am-pihaino’ areo?
4 Amma yanzu ka ƙarfafa, ya Zerubbabel,’ in ji Ubangiji. ‘Ka ƙarfafa, ya Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist. Ku ƙarfafa, dukanku mutanen ƙasar,’ in ji Ubangiji, ‘ku yi aiki. Gama ina tare da ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Fe mihaozara henane zao ry Zerobabele, hoe t’Iehovà; le mihafatrara ry Iehosoa, ana’ Iehotsadake, mpisorom-bey, naho mihaozara ry hene ondati’ o taneo, hoe t’Iehovà vaho mifanehafa, fa himbaeko, hoe t’Iehovà’ i Màroy.
5 ‘Wannan shi ne alkawarin da na yi da ku a lokacin da kuka fito daga Masar. Ruhuna kuwa yana tare da ku. Kada ku ji tsoro.’
Kanao nampijadoñeko i tsara nifañinàko ama’ areo t’ie niavotse i Mitsraimey te mimoneñe ama’ areo ao ty Troko: le ko mirevendreveñe.
6 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ba da jimawa ba zan sāke girgiza sammai da kuma ƙasa, teku da busasshiyar ƙasa.
Fa hoe ty nafè’ Iehovà’ i Màroy: Indraik’ avao, le anianike te hozoñozoñeko i likerañey naho ty tane toy, naho i riakey vaho o tamboho maikeo;
7 Zan girgiza dukan al’ummai, marmarin kowace al’umma kuma zai taso, sa’an nan zan cika gidan nan da ɗaukaka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
le hampi­ezeñezeñeko o kilakila’ ondatio, naho homb’atoy iaby ze vara soa’ o fifeheañeo vaho hatsafeko engeñe ty anjomba toy, hoe t’Iehovà’ i Màroy.
8 ‘Da zinariya da azurfa duka nawa ne,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Ahiko o volafotio, Ahiko ka o volamènao, hoe t’Iehovà’ i Màroy.
9 ‘Ɗaukakar gidan nan na yanzu za tă fi ɗaukakar gidan nan na dā,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki. ‘A wannan wuri kuma zan ba da salama,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
Handikoatse ty enge’ i taoloy ty enge’ i anjomba manonjohiy, hoe t’Iehovà’ i Màroy; vaho hampanintsiñeko ty toetse toy, hoe ty nafè’ Iehovà’ i Màroy.
10 A ranar ashirin da huɗu ga watan tara, a shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai cewa,
Niheo amy Kagày mpitoky amy faha-roapolo-efats’ambi’ i volam-paha-sivey, amy taom-paha-roe’ i Dariavesey ty tsara’ Iehovà manao ty hoe:
11 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku tambayi firist abin da doka ta ce.
Hoe ty nafè’ Iehovà’ i Màroy: Añontaneo o mpisoroñeo ty amy Hàke, ty hoe:
12 Idan mutum yana riƙe da naman da aka keɓe a rigarsa, sa’an nan kuma wannan rigar ta taɓa burodi, ko dafaffen abinci, ko ruwan inabi, ko mai, ko kowane irin abinci, wannan zai sa abin yă zama tsarkake?’” Firistoci suka amsa, suka ce, “A’a.”
Ie minday hena navaheñe an-kitambe’e ao vaho mioza ami’ty mofo ndra ampemba ndra divay ndra menake ndra amy ze atao mahakama i kitambey, hiavake hao re? Tsie, hoe ty natoi’ o mpisoroñeo.
13 Sa’an nan Haggai ya ce, “In mutumin da ya ƙazantar da kansa ta wurin taɓa gawa, ya taɓa wani daga cikin waɗannan abubuwa, za su ƙazantu?” Firistoci suka amsa, suka ce, “I, zai ƙazantu.”
Le hoe t’i Kagày: Aa ie tsapae’ ty nileoren-dolo i raha rezay, halio hao re? Haleotse re, hoe ty natoi’ o mpisoroñeo.
14 Sai annabi Haggai ya ce, “‘Haka yake da wannan mutane da kuma wannan al’umma a gabana,’ in ji Ubangiji. ‘Duk abin da suke yi da kuma dukan abin da suke miƙawa ƙazantattu ne.
Nanoiñe amy zao t’i Kagày nanao ty hoe: Izay ka ondaty retoañe, naho ty fifeheañe miatrek’ ahy, hoe t’Iehovà: hambañe ama’e ka o satam-pità’ iareo iabio; vaho maleotse o engae’ iereoo.
15 “‘Yanzu kuwa sai ku yi la’akari da wannan daga wannan rana zuwa gaba, ku tuna yadda al’amura suke kafin a ɗora wani dutse bisa wani a haikalin Ubangiji.
Ie henane zao, haraharao: taolo’ ty nampiningirañe ty vato ambone’ ty vato añ’ anjomba’ Iehovà ao,
16 A lokacin, idan wani ya tafi wurin tsibin da zai auna mudu ashirin, sai yă iske mudu goma kawai. Idan kuma wani ya tafi wurin matse ruwan inabi don yă ɗebo lita hamsin, sai yă tarar da lita ashirin kawai.
ie henane zay naho niheo-mb’am-pitoboroñañe aman-droapolo ondatio, folo avao ty nitendreke; ie nimb’am-pipiritañe mb’eo hañakara’e fitovy limampolo am-pipiritañe ao, le roa-polo avao ty tao;
17 Na mai da aikin da kuka sha wahala kuka yi ya zama banza ta wurin saukar da burtuntuna, da fumfuna, da ƙanƙara, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,’ in ji Ubangiji.
linafako ty voreke o satam-pità’ areoo, naho tromambo, vaho havandra; fe tsy nitolike, hoe t’Iehovà:
18 ‘Daga wannan rana zuwa gaba, wato, rana ta ashirin da huɗu ga watan tara, ku lura da ranar da aka kafa harsashin haikalin Ubangiji. Ku lura da kyau.
Ehe, vetsevetseo henane zao, mifototse amy andro faha-roapolo-efats’ ambi’ i volam-paha-siveiy, i andro nañoreñañe ty mananta’ i anjomba’ Iehovàiy—itsa­koreo;
19 Akwai sauran irin da ya rage a rumbu? Har yanzu, kuringar inabi da itacen ɓaure, rumman da itacen zaitun ba su ba da’ya’ya ba tukuna. “‘Amma daga wannan rana zuwa gaba zan sa muku albarka.’”
ke mbe aman-tabiry ty an-driha ao? Eka, mboe tsy namoa o vaheo, o sakoañeo, o raketao, naho o oliveo—fe henane zao, ho tahieko nahareo.
20 Maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai sau na biyu a rana ta ashirin da huɗu ga wata cewa,
Niheo amy Kagày fañindroe’e amy andro faha-roapolo-efats’ambi’ i volañeiy ty tsara’ Iehovà nanao ty hoe:
21 “Ka faɗa wa Zerubbabel gwamnan Yahuda cewa zan girgiza sammai da ƙasa.
Saontsio amy Zerobabele, mpanjaka’ Iehodà ty hoe: hampiezeñezeñeko o likerañeo naho ty tane toy;
22 Zan hamɓarar da gadajen mulki in kuma ragargaza ƙarfin ƙasashen al’ummai. Zan tumɓuke kekunan yaƙi da mahayansu; dawakai da mahayansu za su mutu, kowane ta wurin takobin ɗan’uwansu.
havalitsin­goreko ty fiambesa’ o fifeheañeo naho harotsa­ko ty haozaram-pifeleha’ o kilakila’ ndatio vaho hahohoko o sareteo rekets’ o mijoñe ama’eo; sindre hikorovoke o soavalao rekets’ o mpiningitseo, songa am-pibaran-dongo’e.
23 “‘A wannan rana,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘Zan ɗauke ka, bawana Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel,’ in ji Ubangiji, ‘in kuma maishe ka kamar zoben hatimi, gama na zaɓe ka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
Ie amy andro zay, hoe t’Iehovà’ i Màroy, ho rambeseko irehe ry Zerobabele, mpitoroko, toe ana’ i Sealtiele, hoe t’Iehovà, hanoeko bangem-pitomboke; toe ihe ty jinoboko, hoe t’Iehovà’ i Màroy.

< Haggai 2 >