< Haggai 2 >

1 a ranar ashirin da ɗaya ga watan bakwai, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
Au septième mois, au vingt-unième jour du mois, la parole du Seigneur fut adressée par l’entremise d’Aggée, le prophète, disant:
2 “Ka yi magana da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel wanda yake gwamna a Yahuda, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma dukan raguwar mutane. Ka tambaye su ka ce,
Parle à Zorobabel, fils de Salathiel, chef de Juda, et à Jésus, fils de Josédec, le grand-prêtre, et à ceux qui sont restés du peuple, en disant:
3 ‘Wane ne a cikinku ya ragu da ya ga wannan gida a darajarsa ta dā? Yaya yake a gare ku a yanzu? Bai yi kamar a bakin kome ba, ko ba haka ba?
Qui est celui parmi vous qui, étant resté, a vu cette maison dans sa première gloire? et comment la voyez-vous maintenant? Est-ce qu’elle n’est pas à vos yeux comme si elle n’existait pas?
4 Amma yanzu ka ƙarfafa, ya Zerubbabel,’ in ji Ubangiji. ‘Ka ƙarfafa, ya Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist. Ku ƙarfafa, dukanku mutanen ƙasar,’ in ji Ubangiji, ‘ku yi aiki. Gama ina tare da ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Mais maintenant, Zorobabel, prends courage, dit le Seigneur; prends courage, Jésus, fils de Josédec, grand-prêtre; prends courage aussi, peuple entier de la terre, dit le Seigneur des armées; et observez (parce que, moi, je suis avec vous, dit le Seigneur des armées)
5 ‘Wannan shi ne alkawarin da na yi da ku a lokacin da kuka fito daga Masar. Ruhuna kuwa yana tare da ku. Kada ku ji tsoro.’
L’alliance que j’ai faite avec vous, lorsque vous êtes sortis de la terre d’Egypte: et mon esprit sera au milieu de vous; ne craignez point.
6 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ba da jimawa ba zan sāke girgiza sammai da kuma ƙasa, teku da busasshiyar ƙasa.
Parce que voici ce que dit le Seigneur des armées: Encore un peu de temps, et j’ébranlerai le ciel, et la terre, et la mer, et la partie aride.
7 Zan girgiza dukan al’ummai, marmarin kowace al’umma kuma zai taso, sa’an nan zan cika gidan nan da ɗaukaka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Et j’ébranlerai toutes les nations: ET VIENDRÀ LE DÉSIRÉ de toutes les nations; et je remplirai cette maison de gloire, dit le Seigneur des armées.
8 ‘Da zinariya da azurfa duka nawa ne,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
À moi est l’argent, et à moi est l’or, dit le Seigneur des armées.
9 ‘Ɗaukakar gidan nan na yanzu za tă fi ɗaukakar gidan nan na dā,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki. ‘A wannan wuri kuma zan ba da salama,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
La gloire de cette dernière maison sera plus grande que celle de la première, dit le Seigneur des armées; et en ce lieu je donnerai la paix, dit le Seigneur des armées.
10 A ranar ashirin da huɗu ga watan tara, a shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai cewa,
Au vingt-quatrième jour du neuvième mois, en la seconde année du roi Darius, la parole du Seigneur fut adressée à Aggée, le prophète, disant:
11 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku tambayi firist abin da doka ta ce.
Voici ce que dit le Seigneur des armées: Interroge les prêtres sur la loi, en disant:
12 Idan mutum yana riƙe da naman da aka keɓe a rigarsa, sa’an nan kuma wannan rigar ta taɓa burodi, ko dafaffen abinci, ko ruwan inabi, ko mai, ko kowane irin abinci, wannan zai sa abin yă zama tsarkake?’” Firistoci suka amsa, suka ce, “A’a.”
Si un homme porte de la chair sanctifiée dans un coin de son vêtement, et que ce coin de son vêtement touche du pain ou de la viande, ou du vin, ou de l’huile, ou tout autre aliment, ce qu’il aura touché sera-t-il sanctifié? Or, répondant, les prêtres dirent: Non.
13 Sa’an nan Haggai ya ce, “In mutumin da ya ƙazantar da kansa ta wurin taɓa gawa, ya taɓa wani daga cikin waɗannan abubuwa, za su ƙazantu?” Firistoci suka amsa, suka ce, “I, zai ƙazantu.”
Aggée dit: Si un homme souillé par l’attouchement d’un cadavre touche quelqu’une de toutes ces choses, sera-t-elle souillée? Et les prêtres répondirent et dirent: Elle sera souillée.
14 Sai annabi Haggai ya ce, “‘Haka yake da wannan mutane da kuma wannan al’umma a gabana,’ in ji Ubangiji. ‘Duk abin da suke yi da kuma dukan abin da suke miƙawa ƙazantattu ne.
Et Aggée reprit et dit: Ainsi est ce peuple, ainsi est cette nation devant ma face, dit le Seigneur, et ainsi est-il de toute œuvre de leurs mains, et tout ce qu’ils m’ont offert en ce lieu sera souillé.
15 “‘Yanzu kuwa sai ku yi la’akari da wannan daga wannan rana zuwa gaba, ku tuna yadda al’amura suke kafin a ɗora wani dutse bisa wani a haikalin Ubangiji.
Et maintenant appliquez vos cœurs à ce qui s’est passé depuis ce jour et au-delà, avant qu’une pierre eût été posée sur une pierre au temple du Seigneur.
16 A lokacin, idan wani ya tafi wurin tsibin da zai auna mudu ashirin, sai yă iske mudu goma kawai. Idan kuma wani ya tafi wurin matse ruwan inabi don yă ɗebo lita hamsin, sai yă tarar da lita ashirin kawai.
Lorsque vous vous approchiez d’un tas de vingt boisseaux de grains, ils se réduisaient à dix; et lorsque vous entriez au pressoir pour faire cinquante cruches de vin, il s’en faisait vingt.
17 Na mai da aikin da kuka sha wahala kuka yi ya zama banza ta wurin saukar da burtuntuna, da fumfuna, da ƙanƙara, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,’ in ji Ubangiji.
Je vous ai frappés d’un vent brûlant; et j’ai frappé de la nielle et de la grêle tous les travaux de vos mains; et il n’y a eu personne parmi vous qui revînt à moi, dit le Seigneur.
18 ‘Daga wannan rana zuwa gaba, wato, rana ta ashirin da huɗu ga watan tara, ku lura da ranar da aka kafa harsashin haikalin Ubangiji. Ku lura da kyau.
Appliquez vos cœurs à ce qui se fera depuis ce jour et à l’avenir, depuis le vingt-quatrième jour du neuvième mois; depuis le jour que les fondements du temple du Seigneur ont été jetés, appliquez votre cœur.
19 Akwai sauran irin da ya rage a rumbu? Har yanzu, kuringar inabi da itacen ɓaure, rumman da itacen zaitun ba su ba da’ya’ya ba tukuna. “‘Amma daga wannan rana zuwa gaba zan sa muku albarka.’”
Est-ce que les grains n’ont déjà pas germé? et la vigne, et le figuier et le grenadier et l’olivier n’ont-ils pas fleuri? Depuis ce jour je bénirai.
20 Maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai sau na biyu a rana ta ashirin da huɗu ga wata cewa,
Et la parole du Seigneur fut adressée une seconde fois à Aggée le vingt-quatrième jour du mois, disant:
21 “Ka faɗa wa Zerubbabel gwamnan Yahuda cewa zan girgiza sammai da ƙasa.
Parle à Zorobabel, chef de Juda, en disant: Moi j’ébranlerai à la fois le ciel et la terre.
22 Zan hamɓarar da gadajen mulki in kuma ragargaza ƙarfin ƙasashen al’ummai. Zan tumɓuke kekunan yaƙi da mahayansu; dawakai da mahayansu za su mutu, kowane ta wurin takobin ɗan’uwansu.
Et je renverserai le trône des royaumes, et je briserai la force du règne des nations; et je renverserai le quadrige, et celui qui le monte; les chevaux tomberont ainsi que leurs cavaliers; un homme tombera sous le glaive -de son frère.
23 “‘A wannan rana,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘Zan ɗauke ka, bawana Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel,’ in ji Ubangiji, ‘in kuma maishe ka kamar zoben hatimi, gama na zaɓe ka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
En ce jour-là, dit le Seigneur des armées, je te prendrai, Zorobabel, fils de Salathiel, mon serviteur, dit le Seigneur, et je te poserai comme un sceau, parce que je t’ai choisi, dit le Seigneur des armées.

< Haggai 2 >