< Haggai 2 >

1 a ranar ashirin da ɗaya ga watan bakwai, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
Le vingt et unième jour du septième mois, la parole de l'Éternel fut adressée, par Aggée le prophète, en ces termes:
2 “Ka yi magana da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel wanda yake gwamna a Yahuda, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma dukan raguwar mutane. Ka tambaye su ka ce,
Parle donc à Zorobabel, fils de Salathiel, gouverneur de Juda, et à Joshua, fils de Jotsadak, grand sacrificateur, et au reste du peuple, et dis-leur:
3 ‘Wane ne a cikinku ya ragu da ya ga wannan gida a darajarsa ta dā? Yaya yake a gare ku a yanzu? Bai yi kamar a bakin kome ba, ko ba haka ba?
Qui est-ce qui reste parmi vous, de ceux qui ont vu cette maison dans sa gloire première, et comment la voyez-vous maintenant? Telle qu'elle est, n'est-elle pas comme un rien à vos yeux?
4 Amma yanzu ka ƙarfafa, ya Zerubbabel,’ in ji Ubangiji. ‘Ka ƙarfafa, ya Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist. Ku ƙarfafa, dukanku mutanen ƙasar,’ in ji Ubangiji, ‘ku yi aiki. Gama ina tare da ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Or maintenant, courage, Zorobabel! dit l'Éternel; courage, Joshua, fils de Jotsadak, grand sacrificateur! et courage, vous, tout le peuple du pays! dit l'Éternel; et travaillez, car je suis avec vous, dit l'Éternel des armées,
5 ‘Wannan shi ne alkawarin da na yi da ku a lokacin da kuka fito daga Masar. Ruhuna kuwa yana tare da ku. Kada ku ji tsoro.’
Selon l'alliance que j'ai traitée avec vous quand vous sortîtes d'Égypte, et mon Esprit demeure au milieu de vous: ne craignez point!
6 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ba da jimawa ba zan sāke girgiza sammai da kuma ƙasa, teku da busasshiyar ƙasa.
Car ainsi a dit l'Éternel des armées: Encore une fois, dans peu de temps, j'ébranlerai les cieux et la terre, et la mer et le sec.
7 Zan girgiza dukan al’ummai, marmarin kowace al’umma kuma zai taso, sa’an nan zan cika gidan nan da ɗaukaka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
J'ébranlerai toutes les nations, et les trésors de toutes les nations arriveront, et je remplirai cette maison de gloire, a dit l'Éternel des armées.
8 ‘Da zinariya da azurfa duka nawa ne,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
L'argent est à moi, et l'or est à moi, dit l'Éternel des armées.
9 ‘Ɗaukakar gidan nan na yanzu za tă fi ɗaukakar gidan nan na dā,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki. ‘A wannan wuri kuma zan ba da salama,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
La gloire de cette dernière maison sera plus grande que celle de la première, a dit l'Éternel des armées; et je mettrai la paix en ce lieu, dit l'Éternel des armées.
10 A ranar ashirin da huɗu ga watan tara, a shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai cewa,
Le vingt-quatrième jour du neuvième mois, la seconde année de Darius, la parole de l'Éternel fut adressée, par Aggée, le prophète, en ces mots:
11 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku tambayi firist abin da doka ta ce.
Ainsi dit l'Éternel des armées: Propose donc aux sacrificateurs cette question sur la loi.
12 Idan mutum yana riƙe da naman da aka keɓe a rigarsa, sa’an nan kuma wannan rigar ta taɓa burodi, ko dafaffen abinci, ko ruwan inabi, ko mai, ko kowane irin abinci, wannan zai sa abin yă zama tsarkake?’” Firistoci suka amsa, suka ce, “A’a.”
Si quelqu'un porte de la chair consacrée dans le pan de son vêtement, et que de ce vêtement il touche du pain, ou un mets cuit, ou du vin, ou de l'huile, ou un aliment quelconque, cela devient-il sacré? Les sacrificateurs répondirent, et dirent: Non!
13 Sa’an nan Haggai ya ce, “In mutumin da ya ƙazantar da kansa ta wurin taɓa gawa, ya taɓa wani daga cikin waɗannan abubuwa, za su ƙazantu?” Firistoci suka amsa, suka ce, “I, zai ƙazantu.”
Et Aggée dit: Si celui qui est souillé pour un mort touche toutes ces choses, seront-elles souillées? Les sacrificateurs répondirent, et dirent: Elles seront souillées.
14 Sai annabi Haggai ya ce, “‘Haka yake da wannan mutane da kuma wannan al’umma a gabana,’ in ji Ubangiji. ‘Duk abin da suke yi da kuma dukan abin da suke miƙawa ƙazantattu ne.
Alors Aggée reprit et dit: Tel est ce peuple, telle est cette nation devant moi, dit l'Éternel, et telle est toute l'œuvre de leurs mains; ce qu'ils offrent là est souillé.
15 “‘Yanzu kuwa sai ku yi la’akari da wannan daga wannan rana zuwa gaba, ku tuna yadda al’amura suke kafin a ɗora wani dutse bisa wani a haikalin Ubangiji.
Considérez donc attentivement ce qui s'est passé depuis ce jour et en remontant, avant qu'on eût mis pierre sur pierre au temple de l'Éternel.
16 A lokacin, idan wani ya tafi wurin tsibin da zai auna mudu ashirin, sai yă iske mudu goma kawai. Idan kuma wani ya tafi wurin matse ruwan inabi don yă ɗebo lita hamsin, sai yă tarar da lita ashirin kawai.
Alors, quand on venait à un tas de vingt mesures, il n'y en avait que dix; quand on venait à la cuve pour puiser cinquante mesures du pressoir, il n'y en avait que vingt.
17 Na mai da aikin da kuka sha wahala kuka yi ya zama banza ta wurin saukar da burtuntuna, da fumfuna, da ƙanƙara, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,’ in ji Ubangiji.
Je vous ai frappés de brûlure, de nielle et de grêle dans tout le travail de vos mains; et vous n'êtes pas revenus à moi, dit l'Éternel.
18 ‘Daga wannan rana zuwa gaba, wato, rana ta ashirin da huɗu ga watan tara, ku lura da ranar da aka kafa harsashin haikalin Ubangiji. Ku lura da kyau.
Considérez donc attentivement ce qui arrivera depuis ce jour-ci et dans la suite, depuis le vingt-quatrième jour du neuvième mois, depuis le jour où le temple de l'Éternel fut fondé; considérez-le attentivement!
19 Akwai sauran irin da ya rage a rumbu? Har yanzu, kuringar inabi da itacen ɓaure, rumman da itacen zaitun ba su ba da’ya’ya ba tukuna. “‘Amma daga wannan rana zuwa gaba zan sa muku albarka.’”
Y a-t-il encore du grain dans les greniers? Jusqu'à la vigne, au figuier, au grenadier et à l'olivier, rien n'a rapporté. Mais, dès ce jour, je bénirai.
20 Maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai sau na biyu a rana ta ashirin da huɗu ga wata cewa,
La parole de l'Éternel fut adressée, pour la seconde fois, à Aggée, le vingt-quatrième jour du mois, en ces mots:
21 “Ka faɗa wa Zerubbabel gwamnan Yahuda cewa zan girgiza sammai da ƙasa.
Parle à Zorobabel, gouverneur de Juda, et dis-lui: J'ébranlerai les cieux et la terre;
22 Zan hamɓarar da gadajen mulki in kuma ragargaza ƙarfin ƙasashen al’ummai. Zan tumɓuke kekunan yaƙi da mahayansu; dawakai da mahayansu za su mutu, kowane ta wurin takobin ɗan’uwansu.
Je renverserai le trône des royaumes, et je détruirai la force des royaumes des nations; je renverserai les chars et ceux qui les montent; les chevaux et ceux qui les montent seront abattus, l'un par l'épée de l'autre.
23 “‘A wannan rana,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘Zan ɗauke ka, bawana Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel,’ in ji Ubangiji, ‘in kuma maishe ka kamar zoben hatimi, gama na zaɓe ka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
En ce jour-là, dit l'Éternel des armées, je te prendrai, Zorobabel, fils de Salathiel, mon serviteur, dit l'Éternel, et je te tiendrai comme un cachet; car je t'ai choisi, dit l'Éternel des armées.

< Haggai 2 >