< Haggai 2 >

1 a ranar ashirin da ɗaya ga watan bakwai, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
Et le vingt-unième jour du septième mois, le Seigneur confia Sa parole aux mains d'Aggée, le prophète, disant:
2 “Ka yi magana da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel wanda yake gwamna a Yahuda, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma dukan raguwar mutane. Ka tambaye su ka ce,
Parle à Zorobabel, fils de Salathiel, de la tribu de Juda, et à Jésus, fils de Josédec, le grand prêtre, et à tout le reste du peuple, disant:
3 ‘Wane ne a cikinku ya ragu da ya ga wannan gida a darajarsa ta dā? Yaya yake a gare ku a yanzu? Bai yi kamar a bakin kome ba, ko ba haka ba?
Qui de vous a vu ce temple en sa première gloire? Et comment le voyez-vous aujourd'hui? N'est-il pas devant vous comme n'étant point?
4 Amma yanzu ka ƙarfafa, ya Zerubbabel,’ in ji Ubangiji. ‘Ka ƙarfafa, ya Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist. Ku ƙarfafa, dukanku mutanen ƙasar,’ in ji Ubangiji, ‘ku yi aiki. Gama ina tare da ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Et maintenant arme-toi de force, Zorobabel, fils de Salathiel, de la tribu de Juda; arme-toi de force, Jésus, fils de Josédec, le grand-prêtre; arme-toi de force, peuple de la terre, dit le Seigneur, et travaille; car Je suis avec vous, dit le Seigneur tout-puissant.
5 ‘Wannan shi ne alkawarin da na yi da ku a lokacin da kuka fito daga Masar. Ruhuna kuwa yana tare da ku. Kada ku ji tsoro.’
Et Mon Esprit est debout au milieu de vous; ayez confiance;
6 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ba da jimawa ba zan sāke girgiza sammai da kuma ƙasa, teku da busasshiyar ƙasa.
Car voici ce que dit le Seigneur tout-puissant: Encore une fois, J'ébranlerai le ciel et la terre, la mer et le désert;
7 Zan girgiza dukan al’ummai, marmarin kowace al’umma kuma zai taso, sa’an nan zan cika gidan nan da ɗaukaka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
et J'ébranlerai toutes les nations; et celles des nations que J'aurai élevées viendront; et je remplirai de gloire le temple, dit le Seigneur tout- puissant.
8 ‘Da zinariya da azurfa duka nawa ne,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
À Moi est l'or, à Moi l'argent, dit le Seigneur tout-puissant.
9 ‘Ɗaukakar gidan nan na yanzu za tă fi ɗaukakar gidan nan na dā,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki. ‘A wannan wuri kuma zan ba da salama,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
La gloire de ce temple sera grande; mais celle de la fin surpassera celle du commencement, dit le Seigneur Dieu tout-puissant; et à cette terre Je donnerai la paix, dit le Seigneur Dieu tout-puissant, et je donnerai la paix en ce lieu à tous ceux qui travaillent à réédifier le temple.
10 A ranar ashirin da huɗu ga watan tara, a shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai cewa,
Le vingt-troisième jour du neuvième mois de la seconde année du règne de Darius, la parole du Seigneur vint à Aggée, le prophète, disant:
11 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku tambayi firist abin da doka ta ce.
Voici ce que dit le Seigneur, Maître de toutes choses: Consulte les prêtres sur la loi; dis-leur:
12 Idan mutum yana riƙe da naman da aka keɓe a rigarsa, sa’an nan kuma wannan rigar ta taɓa burodi, ko dafaffen abinci, ko ruwan inabi, ko mai, ko kowane irin abinci, wannan zai sa abin yă zama tsarkake?’” Firistoci suka amsa, suka ce, “A’a.”
Si un homme prend dans le coin de son manteau de la chair consacrée, et si le coin de son manteau touche du pain ou de la viande cuite, du vin ou de l'huile, ou tout autre aliment, cet aliment sera-t-il sanctifié? Et les prêtres répondirent et dirent: Non.
13 Sa’an nan Haggai ya ce, “In mutumin da ya ƙazantar da kansa ta wurin taɓa gawa, ya taɓa wani daga cikin waɗannan abubuwa, za su ƙazantu?” Firistoci suka amsa, suka ce, “I, zai ƙazantu.”
Et Aggée dit: Si un homme souillé et non purifié en son âme touche l'une de ces choses, sera-t-elle souillée? Et les prêtres répondirent et dirent: Elle sera souillée.
14 Sai annabi Haggai ya ce, “‘Haka yake da wannan mutane da kuma wannan al’umma a gabana,’ in ji Ubangiji. ‘Duk abin da suke yi da kuma dukan abin da suke miƙawa ƙazantattu ne.
Et Aggée reprit, et dit: Tel est ce peuple; telle est cette nation devant Moi, dit le Seigneur; telles sont toutes les œuvres de leurs mains; tel est celui qui approchera de ce lieu souillé à cause des présents qu'il a reçus le matin; et ils souffriront à l'aspect de leurs travaux; et ils ont haï celui qui les a réprimandés devant les portes de la ville.
15 “‘Yanzu kuwa sai ku yi la’akari da wannan daga wannan rana zuwa gaba, ku tuna yadda al’amura suke kafin a ɗora wani dutse bisa wani a haikalin Ubangiji.
Et maintenant, en vos cœurs, remontez dans le passé à partir de ce jour, avant qu'on eût posé pierre sur pierre dans le temple du Seigneur; ce qui vous arrivait
16 A lokacin, idan wani ya tafi wurin tsibin da zai auna mudu ashirin, sai yă iske mudu goma kawai. Idan kuma wani ya tafi wurin matse ruwan inabi don yă ɗebo lita hamsin, sai yă tarar da lita ashirin kawai.
lorsque vous jetiez dans le coffre à orge vingt mesures de grain, et qu'elles se réduisaient à dix; lorsque vous alliez à la cuve, sous le pressoir, pour y puiser vingt-cinq mesures, et qu'il n'y en avait plus que vingt.
17 Na mai da aikin da kuka sha wahala kuka yi ya zama banza ta wurin saukar da burtuntuna, da fumfuna, da ƙanƙara, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,’ in ji Ubangiji.
Je vous ai frappés par la stérilité; J'ai frappé les œuvres de vos mains par les ravages du vent et par la grêle; et vous ne vous êtes point convertis à Moi, dit le Seigneur.
18 ‘Daga wannan rana zuwa gaba, wato, rana ta ashirin da huɗu ga watan tara, ku lura da ranar da aka kafa harsashin haikalin Ubangiji. Ku lura da kyau.
Pensez donc en vos cœurs, à partir de ce jour et au delà, à partir du vingt-troisième jour du neuvième mois, et du jour où le temple du Seigneur a été fondé; considérez en vos cœurs
19 Akwai sauran irin da ya rage a rumbu? Har yanzu, kuringar inabi da itacen ɓaure, rumman da itacen zaitun ba su ba da’ya’ya ba tukuna. “‘Amma daga wannan rana zuwa gaba zan sa muku albarka.’”
si l'on voit pareille chose dans les granges; vigne, figuier, grenadier ou olivier, rien n'a encore porté des fruits; mais à partir de ce jour Je vous bénirai.
20 Maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai sau na biyu a rana ta ashirin da huɗu ga wata cewa,
Et la parole du Seigneur vint une seconde fois à Aggée, le prophète, le vingt-quatrième jour du moi, disant:
21 “Ka faɗa wa Zerubbabel gwamnan Yahuda cewa zan girgiza sammai da ƙasa.
Parle à Zorobabel, fils de Salathiel, de la tribu de Juda; dis-lui J'ébranlerai le ciel et la terre, la mer et le désert,
22 Zan hamɓarar da gadajen mulki in kuma ragargaza ƙarfin ƙasashen al’ummai. Zan tumɓuke kekunan yaƙi da mahayansu; dawakai da mahayansu za su mutu, kowane ta wurin takobin ɗan’uwansu.
et Je renverserai le trône des rois, et Je détruirai la puissance des rois des nations, et je ferai tomber leurs chars et leurs écuyers; et les chevaux et leurs cavaliers seront abattus; et le frère frappera du glaive son frère.
23 “‘A wannan rana,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘Zan ɗauke ka, bawana Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel,’ in ji Ubangiji, ‘in kuma maishe ka kamar zoben hatimi, gama na zaɓe ka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
Or, en ce jour-là, dit le Seigneur, maître de toutes choses, je protégerai Zorobabel, fils de Salathiel, Mon serviteur, dit le Seigneur Dieu; et tu seras pour Moi comme un sceau d'alliance, parce que je t'ai choisi, dit le Seigneur tout-puissant.

< Haggai 2 >