< Haggai 2 >

1 a ranar ashirin da ɗaya ga watan bakwai, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
Le septième mois, le vingt-et-unième jour du mois, la parole de Dieu arriva par l’organe du prophète Haggaï en ces termes:
2 “Ka yi magana da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel wanda yake gwamna a Yahuda, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma dukan raguwar mutane. Ka tambaye su ka ce,
"Adresse donc à Zorobabel, fils de Chaltiël, gouverneur de Judée, à Josué, fils de Joçadak, le grand-prêtre, et au reste du peuple les paroles que voici:
3 ‘Wane ne a cikinku ya ragu da ya ga wannan gida a darajarsa ta dā? Yaya yake a gare ku a yanzu? Bai yi kamar a bakin kome ba, ko ba haka ba?
"Est-II encore parmi vous quelqu’un qui ait vu ce temple dans sa splendeur primitive? Et comment le considérez-vous à présent? N’Est-il pas vrai qu’il est comme rien à vos yeux?
4 Amma yanzu ka ƙarfafa, ya Zerubbabel,’ in ji Ubangiji. ‘Ka ƙarfafa, ya Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist. Ku ƙarfafa, dukanku mutanen ƙasar,’ in ji Ubangiji, ‘ku yi aiki. Gama ina tare da ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Toutefois, prends courage, Zorobabel, dit le Seigneur, prends courage, Josué, fils de Joçadak, toi le grand-prêtre, prenez courage, vous les gens de ce pays, dit l’Eternel, et agissez en conséquence, car je suis avec vous, dit l’Eternel-Cebaot.
5 ‘Wannan shi ne alkawarin da na yi da ku a lokacin da kuka fito daga Masar. Ruhuna kuwa yana tare da ku. Kada ku ji tsoro.’
Aux termes de l’alliance que j’ai contractée avec vous lors de votre sortie de l’Egypte, mon esprit réside au milieu de vous: ne craignez rien!"
6 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ba da jimawa ba zan sāke girgiza sammai da kuma ƙasa, teku da busasshiyar ƙasa.
"Oui, ainsi parle l’Eternel-Cebaot, encore un court délai, et je mettrai en mouvement le ciel et la terre, la mer et le continent;
7 Zan girgiza dukan al’ummai, marmarin kowace al’umma kuma zai taso, sa’an nan zan cika gidan nan da ɗaukaka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
je mettrai en mouvement tous les peuples, pour qu’affluent ici les biens les plus précieux de tous ces peuples, et ainsi je remplirai cette maison de splendeur, dit l’Eternel-Cebaot.
8 ‘Da zinariya da azurfa duka nawa ne,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
A moi appartient l’argent, à moi l’or, dit l’Eternel-Cebaot.
9 ‘Ɗaukakar gidan nan na yanzu za tă fi ɗaukakar gidan nan na dā,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki. ‘A wannan wuri kuma zan ba da salama,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
Plus grande sera la splendeur de ce second temple que celle du premier, dit l’Eternel-Cebaot, et en ce lieu je ferai régner la paix, dit l’Eternel-Cebaot."
10 A ranar ashirin da huɗu ga watan tara, a shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai cewa,
Le vingt-quatrième jour du neuvième mois, dans la deuxième année de Darius, la parole de Dieu arriva par l’organe du prophète Haggaï en ces termes:
11 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku tambayi firist abin da doka ta ce.
"Ainsi parle l’Eternel-Cebaot: Interroge donc les prêtres sur le point de doctrine que voici:
12 Idan mutum yana riƙe da naman da aka keɓe a rigarsa, sa’an nan kuma wannan rigar ta taɓa burodi, ko dafaffen abinci, ko ruwan inabi, ko mai, ko kowane irin abinci, wannan zai sa abin yă zama tsarkake?’” Firistoci suka amsa, suka ce, “A’a.”
S’Il arrive que quelqu’un transporte de la chair consacrée dans le pan de son habit, et qu’il mette ce pan de vêtement en contact avec du pain, un légume, du vin, de l’huile ou tout autre comestible, ceux-ci contracteront-ils la sainteté?" Les prêtres répondirent en disant: "Non!"
13 Sa’an nan Haggai ya ce, “In mutumin da ya ƙazantar da kansa ta wurin taɓa gawa, ya taɓa wani daga cikin waɗannan abubuwa, za su ƙazantu?” Firistoci suka amsa, suka ce, “I, zai ƙazantu.”
Haggaï reprit: "Si une personne devenue impure par le contact d’un mort touche ces objets, seront-ils impurs?" Les prêtres répondirent en disant: "Ils seront impurs."
14 Sai annabi Haggai ya ce, “‘Haka yake da wannan mutane da kuma wannan al’umma a gabana,’ in ji Ubangiji. ‘Duk abin da suke yi da kuma dukan abin da suke miƙawa ƙazantattu ne.
Alors Haggaï prit la parole et dit: "Il en est ainsi de ce peuple: voilà comme il paraît à mes yeux, ce peuple, dit l’Eternel, lui et toutes les œuvres de ses mains. Ce qu’ils me présentent là comme offrande est impur!
15 “‘Yanzu kuwa sai ku yi la’akari da wannan daga wannan rana zuwa gaba, ku tuna yadda al’amura suke kafin a ɗora wani dutse bisa wani a haikalin Ubangiji.
Or ça, observez attentivement ce qui va se passer dans la suite, à partir de ce jour; car jusqu’aujourd’hui on n’avait pas posé pierre sur pierre au sanctuaire de l’Eternel.
16 A lokacin, idan wani ya tafi wurin tsibin da zai auna mudu ashirin, sai yă iske mudu goma kawai. Idan kuma wani ya tafi wurin matse ruwan inabi don yă ɗebo lita hamsin, sai yă tarar da lita ashirin kawai.
Jadis, on se rendait auprès d’un monceau de vingt gerbes, et il n’y en avait que dix; on se rendait auprès d’une cuve de vin dans l’attente d’y puiser cinquante mesures et elles se réduisaient à vingt.
17 Na mai da aikin da kuka sha wahala kuka yi ya zama banza ta wurin saukar da burtuntuna, da fumfuna, da ƙanƙara, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,’ in ji Ubangiji.
Je vous avais éprouvés par la rouille, la nielle et la grêle, s’attaquant à toute l’ouvre de vos mains, mais cela ne vous a pas ramenés à moi, dit l’Eternel.
18 ‘Daga wannan rana zuwa gaba, wato, rana ta ashirin da huɗu ga watan tara, ku lura da ranar da aka kafa harsashin haikalin Ubangiji. Ku lura da kyau.
Observez donc avec soin ce qui va se passer, à dater de ce jour et ultérieurement, à dater de ce jour qui est le vingt-quatrième du neuvième mois, jour où ont été jetés les fondements du sanctuaire de l’Eternel. Oui, prenez-le bien à cœur!
19 Akwai sauran irin da ya rage a rumbu? Har yanzu, kuringar inabi da itacen ɓaure, rumman da itacen zaitun ba su ba da’ya’ya ba tukuna. “‘Amma daga wannan rana zuwa gaba zan sa muku albarka.’”
Avez-vous encore des grains dans le grenier? N’Est-ce pas que ni vigne, ni figuier, ni grenadier, ni olivier n’ont rien donné? Mais à partir de ce jour je vous comblerai de mes bénédictions."
20 Maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai sau na biyu a rana ta ashirin da huɗu ga wata cewa,
La parole de l’Eternel s’adressa une seconde fois à Haggaï, le vingt-quatrième jour du mois, en ces termes:
21 “Ka faɗa wa Zerubbabel gwamnan Yahuda cewa zan girgiza sammai da ƙasa.
"Dis à Zorobabel, gouverneur de Judée, ce qui suit: Je vais faire trembler le ciel et la terre.
22 Zan hamɓarar da gadajen mulki in kuma ragargaza ƙarfin ƙasashen al’ummai. Zan tumɓuke kekunan yaƙi da mahayansu; dawakai da mahayansu za su mutu, kowane ta wurin takobin ɗan’uwansu.
Je mettrai sens dessus dessous le trône des royaumes, je détruirai la puissance des empires des nations; je renverserai les chars de guerre et ceux qui y siègent, les coursiers et leurs cavaliers tomberont à terre, frappés les uns par le glaive des autres.
23 “‘A wannan rana,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘Zan ɗauke ka, bawana Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel,’ in ji Ubangiji, ‘in kuma maishe ka kamar zoben hatimi, gama na zaɓe ka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
En ce jour, dit l’Eternel-Cebaot, je te prendrai, ô Zorobabel, fils de Chaltiël, toi mon serviteur, dit l’Eternel, et je te considérerai comma un anneau sigillaire, car c’est toi que j’ai élu, dit l’Eternel-Cebaot."

< Haggai 2 >