< Haggai 2 >

1 a ranar ashirin da ɗaya ga watan bakwai, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
In the seventh month, on the twenty-first of the month, came the word of Yahweh, by the hand of Haggai the prophet, saying:
2 “Ka yi magana da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel wanda yake gwamna a Yahuda, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma dukan raguwar mutane. Ka tambaye su ka ce,
Speak, I pray thee, unto Zerubbabel son of Shealtiel, pasha of Judah, and unto Jehoshua son of Jehozadak, the high priest, —and unto the remnant of the people, saying: —
3 ‘Wane ne a cikinku ya ragu da ya ga wannan gida a darajarsa ta dā? Yaya yake a gare ku a yanzu? Bai yi kamar a bakin kome ba, ko ba haka ba?
Who is there among you that is left, that saw this house, in its former glory? And how do ye see it now? Is it not, in comparison with that, as nothing, in your eyes?
4 Amma yanzu ka ƙarfafa, ya Zerubbabel,’ in ji Ubangiji. ‘Ka ƙarfafa, ya Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist. Ku ƙarfafa, dukanku mutanen ƙasar,’ in ji Ubangiji, ‘ku yi aiki. Gama ina tare da ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Now, therefore—Be strong, O Zerubbabel, urgeth Yahweh, and be strong, O Jehoshua son of Jehozadak the high priest, and be strong, all ye people of the land, urgeth Yahweh, and work; For, I, am with you, Declareth Yahweh of hosts.
5 ‘Wannan shi ne alkawarin da na yi da ku a lokacin da kuka fito daga Masar. Ruhuna kuwa yana tare da ku. Kada ku ji tsoro.’
The very thing that I solemnized with you, when ye came forth out of the land of Egypt, That, my spirit abiding in your midst, ye should not fear.
6 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ba da jimawa ba zan sāke girgiza sammai da kuma ƙasa, teku da busasshiyar ƙasa.
For, thus, saith Yahweh of hosts, Yet once, a little, it is, —and I am shaking the heavens and the earth, and the sea and the dry land;
7 Zan girgiza dukan al’ummai, marmarin kowace al’umma kuma zai taso, sa’an nan zan cika gidan nan da ɗaukaka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
And I will shake all the nations, and the delight of all the nations, shall come in, —and I will fill this house with glory, saith Yahweh of hosts.
8 ‘Da zinariya da azurfa duka nawa ne,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Mine is the silver and Mine the gold, Declareth Yahweh of hosts:
9 ‘Ɗaukakar gidan nan na yanzu za tă fi ɗaukakar gidan nan na dā,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki. ‘A wannan wuri kuma zan ba da salama,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
Greater shall be the last glory of this house than the first, saith Yahweh of hosts, —and, in this place, will I give prosperity, Declareth Yahweh of hosts.
10 A ranar ashirin da huɗu ga watan tara, a shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai cewa,
On the twenty-fourth of the ninth month, in the second year of Darius, came the word of Yahweh unto Haggai the prophet, saying:
11 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku tambayi firist abin da doka ta ce.
Thus, saith Yahweh of hosts, —I pray you, ask the priests a direction, saying:
12 Idan mutum yana riƙe da naman da aka keɓe a rigarsa, sa’an nan kuma wannan rigar ta taɓa burodi, ko dafaffen abinci, ko ruwan inabi, ko mai, ko kowane irin abinci, wannan zai sa abin yă zama tsarkake?’” Firistoci suka amsa, suka ce, “A’a.”
If a man carry holy flesh in the skirt of his garment, and then toucheth with his skirt bread or a cooked dish or wine or oil or any food, shall it be holy? And the priests answered and said, No.
13 Sa’an nan Haggai ya ce, “In mutumin da ya ƙazantar da kansa ta wurin taɓa gawa, ya taɓa wani daga cikin waɗannan abubuwa, za su ƙazantu?” Firistoci suka amsa, suka ce, “I, zai ƙazantu.”
Then said Haggai, If one who is defiled for a dead person touch any of these, shall it be defiled? And the priests answered and said, It shall be defiled.
14 Sai annabi Haggai ya ce, “‘Haka yake da wannan mutane da kuma wannan al’umma a gabana,’ in ji Ubangiji. ‘Duk abin da suke yi da kuma dukan abin da suke miƙawa ƙazantattu ne.
Then answered Haggai and said, So, is this people and, so, is this nation before me, Declareth Yahweh, and, so, is every work of their hands, —therefore, whatsoever they offer there, is, defiled.
15 “‘Yanzu kuwa sai ku yi la’akari da wannan daga wannan rana zuwa gaba, ku tuna yadda al’amura suke kafin a ɗora wani dutse bisa wani a haikalin Ubangiji.
Now, therefore, I pray you apply your heart, from this day and upwards, —So long as there had not been laid one stone upon another in the temple of Yahweh,
16 A lokacin, idan wani ya tafi wurin tsibin da zai auna mudu ashirin, sai yă iske mudu goma kawai. Idan kuma wani ya tafi wurin matse ruwan inabi don yă ɗebo lita hamsin, sai yă tarar da lita ashirin kawai.
So long were things thus, that, on coming unto a heap of twenty, then was it found to be ten, —on coming unto the vat to draw off fifty measures, then were there found to be twenty.
17 Na mai da aikin da kuka sha wahala kuka yi ya zama banza ta wurin saukar da burtuntuna, da fumfuna, da ƙanƙara, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,’ in ji Ubangiji.
I smote you with blight and with mildew and with hail, in all the work of your hands, —Yet ye did not return unto me, Declareth Yahweh.
18 ‘Daga wannan rana zuwa gaba, wato, rana ta ashirin da huɗu ga watan tara, ku lura da ranar da aka kafa harsashin haikalin Ubangiji. Ku lura da kyau.
Apply your heart, I pray you, from this day and upwards, —from the twenty-fourth day of the ninth month, even from the day when was founded the temple of Yahweh, apply your heart:
19 Akwai sauran irin da ya rage a rumbu? Har yanzu, kuringar inabi da itacen ɓaure, rumman da itacen zaitun ba su ba da’ya’ya ba tukuna. “‘Amma daga wannan rana zuwa gaba zan sa muku albarka.’”
Is the seed yet in the store-house? Howbeit, though at present neither, the vine nor the fig-tree nor the pomegranate nor the olive tree, hath brought forth, from this very day, will I bless you.
20 Maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai sau na biyu a rana ta ashirin da huɗu ga wata cewa,
Then came the word of Yahweh, the second time unto Haggai, on the twenty-fourth of the month, saying:
21 “Ka faɗa wa Zerubbabel gwamnan Yahuda cewa zan girgiza sammai da ƙasa.
Speak thou unto Zerubbabel, pasha of Judah, saying, —I am shaking, the heavens and the earth;
22 Zan hamɓarar da gadajen mulki in kuma ragargaza ƙarfin ƙasashen al’ummai. Zan tumɓuke kekunan yaƙi da mahayansu; dawakai da mahayansu za su mutu, kowane ta wurin takobin ɗan’uwansu.
And I will overturn the throne of kingdoms, and will destroy the strength of the kingdoms of the nations, —and I will overturn the chariots and them who ride therein, and horses and their riders, shall come down, every man by the sword of his brother.
23 “‘A wannan rana,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘Zan ɗauke ka, bawana Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel,’ in ji Ubangiji, ‘in kuma maishe ka kamar zoben hatimi, gama na zaɓe ka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
On that day, declareth Yahweh of hosts, will I take thee, O Zerubbabel son of Shealtiel—my servant, declareth Yahweh, and will set thee as a signet-ring; For, thee, have I chosen, Declareth Yahweh of hosts.

< Haggai 2 >