< Haggai 2 >

1 a ranar ashirin da ɗaya ga watan bakwai, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
Paa den een og tyvende Dag i den syvende Maaned kom HERRENS Ord ved Profeten Haggaj saaledes:
2 “Ka yi magana da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel wanda yake gwamna a Yahuda, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma dukan raguwar mutane. Ka tambaye su ka ce,
Sig til Judas Statholder Zerubbabel, Sjaltiels Søn, til Ypperstepræsten Josua, Jozadaks Søn, og til Resten af Folket saaledes:
3 ‘Wane ne a cikinku ya ragu da ya ga wannan gida a darajarsa ta dā? Yaya yake a gare ku a yanzu? Bai yi kamar a bakin kome ba, ko ba haka ba?
Er der nogen tilbage iblandt eder af dem, der har set dette Hus i dets fordums Herlighed? Hvorledes tykkes det eder da nu? Er det ikke som intet i eders Øjne?
4 Amma yanzu ka ƙarfafa, ya Zerubbabel,’ in ji Ubangiji. ‘Ka ƙarfafa, ya Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist. Ku ƙarfafa, dukanku mutanen ƙasar,’ in ji Ubangiji, ‘ku yi aiki. Gama ina tare da ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Dog vær kun trøstig, Zerubbabel, lyder det fra HERREN, vær kun trøstig, du Ypperstepræst Josua, Jozadaks Søn, vær kun trøstigt, alt Folket i Landet, lyder det fra HERREN. Arbejd kun, thi jeg er med eder, lyder det fra Hærskarers HERRE,
5 ‘Wannan shi ne alkawarin da na yi da ku a lokacin da kuka fito daga Masar. Ruhuna kuwa yana tare da ku. Kada ku ji tsoro.’
og min Aand bliver iblandt eder med den Pagt, jeg sluttede med eder, da I drog bort fra Ægypten; frygt ikke!
6 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ba da jimawa ba zan sāke girgiza sammai da kuma ƙasa, teku da busasshiyar ƙasa.
Thi saa siger Hærskarers HERRE: Endnu en Gang om en liden Stund vil jeg ryste Himmel og Jord, Hav og tørt Land,
7 Zan girgiza dukan al’ummai, marmarin kowace al’umma kuma zai taso, sa’an nan zan cika gidan nan da ɗaukaka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
og jeg vil ryste alle Folkene, og da skal alle Folkenes Skatte komme hid, og jeg fylder dette Hus med Herlighed, siger Hærskarers HERRE.
8 ‘Da zinariya da azurfa duka nawa ne,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Mit er Sølvet, og mit er Guldet, lyder det fra Hærskarers HERRE.
9 ‘Ɗaukakar gidan nan na yanzu za tă fi ɗaukakar gidan nan na dā,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki. ‘A wannan wuri kuma zan ba da salama,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
Dette Hus's kommende Herlighed bliver større end den tidligere, siger Hærskarers HERRE, og paa dette Sted vil jeg give Fred, lyder det fra Hærskarers HERRE.
10 A ranar ashirin da huɗu ga watan tara, a shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai cewa,
Paa den fire og tyvende Dag i den niende Maaned i Darius's andet Regeringsaar kom HERRENS Ord ved Profeten Haggaj saaledes:
11 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku tambayi firist abin da doka ta ce.
Saa siger Hærskarers HERRE: Bed Præsterne om Svar paa følgende Spørgsmaal:
12 Idan mutum yana riƙe da naman da aka keɓe a rigarsa, sa’an nan kuma wannan rigar ta taɓa burodi, ko dafaffen abinci, ko ruwan inabi, ko mai, ko kowane irin abinci, wannan zai sa abin yă zama tsarkake?’” Firistoci suka amsa, suka ce, “A’a.”
»Dersom en Mand bærer helligt Kød i sin Kappeflig og med Fligen rører ved Brød eller noget, som er kogt, eller ved Vin eller Olie eller nogen Slags Mad, bliver disse Ting saa hellige?« Præsterne svarede nej.
13 Sa’an nan Haggai ya ce, “In mutumin da ya ƙazantar da kansa ta wurin taɓa gawa, ya taɓa wani daga cikin waɗannan abubuwa, za su ƙazantu?” Firistoci suka amsa, suka ce, “I, zai ƙazantu.”
Haggaj spurgte da: »Hvis en, som er blevet uren ved Lig, rører ved nogen af disse Ting, bliver den saa uren?« Præsterne svarede ja.
14 Sai annabi Haggai ya ce, “‘Haka yake da wannan mutane da kuma wannan al’umma a gabana,’ in ji Ubangiji. ‘Duk abin da suke yi da kuma dukan abin da suke miƙawa ƙazantattu ne.
Saa tog Haggaj til Orde og sagde: Saaledes er det i mine Øjne med disse Mennesker, saaledes med dette Folk, lyder det fra HERREN, og saaledes med alt deres Hænders Værk og med, hvad de ofrer der: det er urent.
15 “‘Yanzu kuwa sai ku yi la’akari da wannan daga wannan rana zuwa gaba, ku tuna yadda al’amura suke kafin a ɗora wani dutse bisa wani a haikalin Ubangiji.
Men læg nu Mærke til, hvorledes det gaar fra i Dag! Før Sten lagdes paa Sten i HERRENS Hus,
16 A lokacin, idan wani ya tafi wurin tsibin da zai auna mudu ashirin, sai yă iske mudu goma kawai. Idan kuma wani ya tafi wurin matse ruwan inabi don yă ɗebo lita hamsin, sai yă tarar da lita ashirin kawai.
hvorledes gik det eder da? Naar man kom til en Dynge Korn paa tyve Maal, var der ti; og kom man til en Vinperse for at øse halvtredsindstyve Maal af Kummen, var der tyve.
17 Na mai da aikin da kuka sha wahala kuka yi ya zama banza ta wurin saukar da burtuntuna, da fumfuna, da ƙanƙara, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,’ in ji Ubangiji.
Jeg slog eder med Kornbrand, Rust og Hagl ved alt eders Arbejde, men I omvendte eder ikke til mig, lyder det fra HERREN.
18 ‘Daga wannan rana zuwa gaba, wato, rana ta ashirin da huɗu ga watan tara, ku lura da ranar da aka kafa harsashin haikalin Ubangiji. Ku lura da kyau.
Læg Mærke til, hvorledes det gaar fra i Dag, fra den fire og tyvende Dag i den niende Maaned, fra den Dag Grunden lagdes til HERRENS Hus, læg Mærke dertil!
19 Akwai sauran irin da ya rage a rumbu? Har yanzu, kuringar inabi da itacen ɓaure, rumman da itacen zaitun ba su ba da’ya’ya ba tukuna. “‘Amma daga wannan rana zuwa gaba zan sa muku albarka.’”
Er Sæden endnu i Laderne, staar Vinstokken, Figentræet, Granatæbletræet og Oliventræet endnu uden Frugt? Fra i Dag velsigner jeg.
20 Maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai sau na biyu a rana ta ashirin da huɗu ga wata cewa,
Og HERRENS Ord kom for anden Gang til Haggaj paa den fire og tyvende Dag i Maaneden saaledes:
21 “Ka faɗa wa Zerubbabel gwamnan Yahuda cewa zan girgiza sammai da ƙasa.
Sig til Judas Statholder Zerubbabel: Jeg ryster Himmelen og Jorden
22 Zan hamɓarar da gadajen mulki in kuma ragargaza ƙarfin ƙasashen al’ummai. Zan tumɓuke kekunan yaƙi da mahayansu; dawakai da mahayansu za su mutu, kowane ta wurin takobin ɗan’uwansu.
og omstyrter Kongernes Troner, tilintetgør Hedningerigernes Styrke og vælter Stridsvognene med deres Førere, og Heste og Ryttere skal styrte, og den ene skal falde for den andens Sværd.
23 “‘A wannan rana,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘Zan ɗauke ka, bawana Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel,’ in ji Ubangiji, ‘in kuma maishe ka kamar zoben hatimi, gama na zaɓe ka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
Paa hin Dag, lyder det fra Hærskarers HERRE, tager jeg dig, min Tjener Zerubbabel, Sjealtiels Søn, lyder det fra HERREN, og gør dig til en Seglring; thi dig har jeg udvalgt, lyder det fra Hærskarers HERRE.

< Haggai 2 >