< Haggai 2 >
1 a ranar ashirin da ɗaya ga watan bakwai, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
Iden syvende Maaned, paa den een og tyvende Dag i Maaneden, kom Herrens Ord ved Profeten Haggaj, saaledes:
2 “Ka yi magana da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel wanda yake gwamna a Yahuda, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma dukan raguwar mutane. Ka tambaye su ka ce,
Sig dog til Serubabel, Sealthiels Søn, Judas Landshøvding, og til Ypperstepræsten Josua, Jozadaks Søn, og til det overblevne Folk saalunde:
3 ‘Wane ne a cikinku ya ragu da ya ga wannan gida a darajarsa ta dā? Yaya yake a gare ku a yanzu? Bai yi kamar a bakin kome ba, ko ba haka ba?
Hvo iblandt eder er tilbage, som har set dette Hus i dets første Herlighed? og hvorledes se I det nu? er det ikke imod hint som intet for eders Øjne?
4 Amma yanzu ka ƙarfafa, ya Zerubbabel,’ in ji Ubangiji. ‘Ka ƙarfafa, ya Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist. Ku ƙarfafa, dukanku mutanen ƙasar,’ in ji Ubangiji, ‘ku yi aiki. Gama ina tare da ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Dog nu, vær frimodig, Serubabel! siger Herren, og vær frimodig, Josua, Jozadaks Søn, du Ypperstepræst! og vær frimodig, alt Folk i Landet! siger Herren, og arbejder; thi jeg er med eder, siger den Herre Zebaoth.
5 ‘Wannan shi ne alkawarin da na yi da ku a lokacin da kuka fito daga Masar. Ruhuna kuwa yana tare da ku. Kada ku ji tsoro.’
Ordet i min Pagt med eder, der I droge ud af Ægypten, og min Aand vedbliver at være midt iblandt eder; frygter ikke!
6 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ba da jimawa ba zan sāke girgiza sammai da kuma ƙasa, teku da busasshiyar ƙasa.
Thi saa siger den Herre Zebaoth: Endnu en Gang, om en liden Stund, vil jeg ryste Himlene og Jorden og Havet og det tørre Land.
7 Zan girgiza dukan al’ummai, marmarin kowace al’umma kuma zai taso, sa’an nan zan cika gidan nan da ɗaukaka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Og jeg vil ryste alle Folkene, og alle Folkenes Kostbarheder skulle komme; og jeg vil fylde dette Hus med Herlighed, siger den Herre Zebaoth.
8 ‘Da zinariya da azurfa duka nawa ne,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Mig hører Sølvet til, mig hører Guldet til, siger den Herre Zebaoth.
9 ‘Ɗaukakar gidan nan na yanzu za tă fi ɗaukakar gidan nan na dā,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki. ‘A wannan wuri kuma zan ba da salama,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
Dette Hus's sidste Herlighed skal blive større end den første, siger den Herre Zebaoth; og jeg vil give Fred paa dette Sted, siger den Herre Zebaoth.
10 A ranar ashirin da huɗu ga watan tara, a shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai cewa,
Paa den fire og tyvende Dag i den niende Maaned, i Darius's andet Aar, kom Herrens Ord ved Profeten Haggaj, saaledes:
11 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku tambayi firist abin da doka ta ce.
Saa siger den Herre Zebaoth: Spørg dog Præsterne om Loven, og sig:
12 Idan mutum yana riƙe da naman da aka keɓe a rigarsa, sa’an nan kuma wannan rigar ta taɓa burodi, ko dafaffen abinci, ko ruwan inabi, ko mai, ko kowane irin abinci, wannan zai sa abin yă zama tsarkake?’” Firistoci suka amsa, suka ce, “A’a.”
Se, naar nogen bærer helligt Kød i sin Kjortelflig og rører med sin Flig ved Brød eller ved noget kogt eller ved Vin eller ved Olie eller ved Mad, i hvad Slags det end er, mon det helliges derved? Og Præsterne svarede og sagde: Nej.
13 Sa’an nan Haggai ya ce, “In mutumin da ya ƙazantar da kansa ta wurin taɓa gawa, ya taɓa wani daga cikin waɗannan abubuwa, za su ƙazantu?” Firistoci suka amsa, suka ce, “I, zai ƙazantu.”
Da sagde Haggaj: Dersom nogen, der er uren ved Lig, rører ved een af alle disse Ting, mon den bliver uren? Og Præsterne svarede og sagde: Den bliver uren.
14 Sai annabi Haggai ya ce, “‘Haka yake da wannan mutane da kuma wannan al’umma a gabana,’ in ji Ubangiji. ‘Duk abin da suke yi da kuma dukan abin da suke miƙawa ƙazantattu ne.
Da svarede Haggaj og sagde: Saaledes er dette Folk, og saaledes er dette Folkefærd for mit Ansigt, siger Herren, og saaledes er al deres Hænders Gerning; og hvad de ofre der, det er urent.
15 “‘Yanzu kuwa sai ku yi la’akari da wannan daga wannan rana zuwa gaba, ku tuna yadda al’amura suke kafin a ɗora wani dutse bisa wani a haikalin Ubangiji.
Og nu, giver Agt paa Tiden fra denne Dag og tilbage, førend der blev lagt Sten paa Sten til Herrens Tempel:
16 A lokacin, idan wani ya tafi wurin tsibin da zai auna mudu ashirin, sai yă iske mudu goma kawai. Idan kuma wani ya tafi wurin matse ruwan inabi don yă ɗebo lita hamsin, sai yă tarar da lita ashirin kawai.
Førend dette skete, kom da nogen til en Kornhob, der skulde give tyve Maal, saa blev der ti; kom man til Persen for at øse halvtredsindstyve Spande, saa blev der tyve.
17 Na mai da aikin da kuka sha wahala kuka yi ya zama banza ta wurin saukar da burtuntuna, da fumfuna, da ƙanƙara, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,’ in ji Ubangiji.
Med Brand og Rust i Kornet og med Hagel slog jeg eder, ja, al eders Hænders Gerning; men I vendte ikke om til mig, siger Herren.
18 ‘Daga wannan rana zuwa gaba, wato, rana ta ashirin da huɗu ga watan tara, ku lura da ranar da aka kafa harsashin haikalin Ubangiji. Ku lura da kyau.
Giver dog Agt paa Tiden fra denne Dag og tilbage, fra den fire og tyvende Dag i den niende Maaned, ja, endog fra den Dag, da Grundvolden til Herrens Tempel blev lagt, giver Agt!
19 Akwai sauran irin da ya rage a rumbu? Har yanzu, kuringar inabi da itacen ɓaure, rumman da itacen zaitun ba su ba da’ya’ya ba tukuna. “‘Amma daga wannan rana zuwa gaba zan sa muku albarka.’”
Mon der endnu er Korn i Laden? ja, selv Vintræet og Figentræet og Granatæbletræet og Olietræet har intet baaret; men fra denne Dag af vil jeg velsigne.
20 Maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai sau na biyu a rana ta ashirin da huɗu ga wata cewa,
Og Herrens Ord kom anden Gang til Haggaj, paa den fire og tyvende Dag i Maaneden, saaledes:
21 “Ka faɗa wa Zerubbabel gwamnan Yahuda cewa zan girgiza sammai da ƙasa.
Sig til Serubabel, Judas Landshøvding: Jeg vil ryste Himmelen og Jorden,
22 Zan hamɓarar da gadajen mulki in kuma ragargaza ƙarfin ƙasashen al’ummai. Zan tumɓuke kekunan yaƙi da mahayansu; dawakai da mahayansu za su mutu, kowane ta wurin takobin ɗan’uwansu.
og jeg vil omkaste Rigernes Troner og ødelægge Hedningernes Rigers Styrke; og jeg vil omkaste Vogne og dem, som fare paa dem, og Heste, og de, som ride paa dem, skulle styrte, den ene ved den andens Sværd.
23 “‘A wannan rana,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘Zan ɗauke ka, bawana Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel,’ in ji Ubangiji, ‘in kuma maishe ka kamar zoben hatimi, gama na zaɓe ka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
Paa den Dag, siger den Herre Zebaoth, vil jeg tage dig, Serubabel, Sealthiels Søn, min Tjener, siger Herren, og agte dig som Signetringen; thi dig har jeg udvalgt, siger den Herre Zebaoth.