< Haggai 1 >
1 A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus, a rana ta fari ga watan shida, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai zuwa ga Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, gwamnan Yahuda, da kuma Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist.
Uti andra årena Konungs Darios, uti sjette månadenom, på första dagen i månadenom, skedde Herrans ord, genom den Propheten Haggai, till Serubbabel, Sealthiels son, Juda Första, och till Jehosua, Jozadaks son, den öfversta Presten, och sade:
2 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Waɗannan mutane sun ce, ‘Lokaci bai yi ba tukuna da za a gina gidan Ubangiji.’”
Så säger Herren Zebaoth: Detta folket säger: Tiden är ännu icke kommen, att man Herrans hus bygga skall.
3 Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
Och Herrans ord skedde genom den Propheten Haggai sägandes:
4 “Ashe, lokaci ya yi da za ku zauna a ɗakunan da kuka yi da rufin katako, amma haikalin nan yana zaman kufai?”
Månn då edar tid vara kommen, att I bo skolen uti hvälfdom husom, och detta huset måste öde stå?
5 To, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
Nu, så säger Herren Zebaoth: Ser, huru det går eder.
6 Kun shuka da yawa, amma kun girbe kaɗan. Kun ci, amma ba ku ƙoshi ba. Kun sha, amma ba ku kashe ƙishirwa ba. Kun sa tufafi, amma ba ku ji ɗumi ba. Kuna karɓar albashi, ya zama sai ka ce kuna zuba a hudajjen aljihu.”
I sån mycket, och fören litet in; I äten, och varden dock icke mätte; I dricken, och varden dock intet otörstige; I kläden eder, och kunnen dock intet värma eder; och den der penningar förtjenar, han lägger dem uti hålogan pung.
7 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
Så säger Herren Zebaoth: Ser, huru det går eder.
8 Ku haura zuwa kan duwatsu ku sauko da katakai don ku gina gidan, don ni ma in ji daɗinsa, in kuma sami ɗaukaka,” in ji Ubangiji.
Går upp på berget, och hemter trä, och bygger huset; det skall vara mig tacknämligt och jag skall bevisa mina äro, säger Herren.
9 “Ga shi, kukan sa rai za ku sami da yawa, amma sai ku ga kun sami kaɗan. Ɗan kaɗan ɗin ma da kukan kawo gida, nakan hura shi yă tafi. Me ya sa yake faruwa haka?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Saboda gidana da yake zaman kango, yayinda kowannenku yana faman gina gidansa.
Ty I vänten väl efter mycket, och si, det varder litet; och om I än fören det hem, så blås jag dock det bort. Hvi så? säger Herren Zebaoth. Derföre, att mitt hus så öde står, och hvar och en hastar med sino huse;
10 Shi ya sa, saboda ku sammai sun ƙi saukar da raɓa, ƙasa kuma ta ƙi ba da amfani.
Derföre hafver himmelen förhållit daggena öfver eder, och jorden sina frukt.
11 Na kawo fări a ƙasar, da a kan duwatsu, da a kan hatsi, da a kan dukan abin da yake tsirowa daga ƙasa, da a kan mutane, da a kan dabbobi da kuma a kan wahalar hannuwanku.”
Och jag hafver kallat torko, både öfver land och berg, öfver korn, vin, oljo, och öfver allt det utaf jordene kommer; och öfver folk och fä, och öfver allt händers arbete.
12 Sa’an nan sai Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, wanda yake babban firist, da kuma dukan raguwar jama’ar suka yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnsu da kuma saƙon annabi Haggai, domin Ubangiji Allahnsu ne ya aiko shi. Mutane kuwa suka ji tsoron Ubangiji.
Då hörde Serubbabel, Sealthiels son, och Jehosua, Jozadaks son, den öfverste Presten, och alle öfverblefne af folket, sådana Herrans, deras Guds, röst, och Prophetens Haggai ord; såsom Herren, deras Gud, honom sändt hade; och folket fruktade sig för Herranom.
13 Sai Haggai, ɗan saƙon Ubangiji, ya ba da wannan saƙo na Ubangiji ga mutane cewa, “Ina tare da ku” in ji Ubangiji.
Då sade Haggai, Herrans Ängel, som Herrans bådskap hade till folket: Jag är med eder, säger Herren.
14 Saboda haka Ubangiji ya motsa zuciyar Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, wanda yake gwamna a Yahuda, da kuma zuciyar Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma zukatan dukan raguwar jama’ar. Suka zo suka fara aiki a gidan Ubangiji Maɗaukaki, Allahnsu,
Och Herren uppväckte Serubbabels anda, Sealthiels sons, Juda Förstas, och Jehosua anda, Jozadaks sons, dens öfversta Prestens, och allt igenlefda folkens anda; så att de kommo, och arbetade uppå Herrans Zebaoths, deras Guds, hus.
15 a ranar ashirin da huɗu ga watan shida. A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus,
På fjerde och tjugonde dagen i sjette månadenom, uti andro årena Konungs Darios;