< Haggai 1 >

1 A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus, a rana ta fari ga watan shida, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai zuwa ga Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, gwamnan Yahuda, da kuma Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist.
No segundo ano de Dario o rei, no sexto mês, no primeiro dia do mês, a palavra de Javé veio por Ageu, o profeta, a Zorobabel, filho de Shealtiel, governador de Judá, e a Josué, filho de Jehozadak, o sumo sacerdote, dizendo:
2 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Waɗannan mutane sun ce, ‘Lokaci bai yi ba tukuna da za a gina gidan Ubangiji.’”
“Isto é o que diz Javé dos Exércitos: Estas pessoas dizem: “Ainda não chegou a hora, a hora da construção da casa de Yahweh”.
3 Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
Então a palavra de Javé veio por Haggai, o profeta, dizendo:
4 “Ashe, lokaci ya yi da za ku zauna a ɗakunan da kuka yi da rufin katako, amma haikalin nan yana zaman kufai?”
“É um momento para vocês mesmos morarem em suas casas em painéis, enquanto esta casa é um desperdício?
5 To, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
Agora, portanto, é isto que Javé dos Exércitos diz: “Considerem seus caminhos.
6 Kun shuka da yawa, amma kun girbe kaɗan. Kun ci, amma ba ku ƙoshi ba. Kun sha, amma ba ku kashe ƙishirwa ba. Kun sa tufafi, amma ba ku ji ɗumi ba. Kuna karɓar albashi, ya zama sai ka ce kuna zuba a hudajjen aljihu.”
Vocês semearam muito, e trazem pouco. Vocês comem, mas não têm o suficiente. Você bebe, mas não está cheio de bebida. Vocês se vestem, mas ninguém está quente; e quem ganha salário, ganha salário para colocá-los em uma bolsa com buracos”.
7 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
“Isto é o que diz Yahweh dos Exércitos: “Considere seus caminhos.
8 Ku haura zuwa kan duwatsu ku sauko da katakai don ku gina gidan, don ni ma in ji daɗinsa, in kuma sami ɗaukaka,” in ji Ubangiji.
Vá até a montanha, traga madeira e construa a casa. Terei prazer nisso e serei glorificado”, diz Yahweh.
9 “Ga shi, kukan sa rai za ku sami da yawa, amma sai ku ga kun sami kaɗan. Ɗan kaɗan ɗin ma da kukan kawo gida, nakan hura shi yă tafi. Me ya sa yake faruwa haka?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Saboda gidana da yake zaman kango, yayinda kowannenku yana faman gina gidansa.
“Você procurou muito, e eis que chegou a pouco; e quando você a trouxe para casa, eu a explodi”. Por que”, diz Yahweh dos Exércitos, “Por causa da minha casa que jaz desperdício, enquanto cada um de vocês está ocupado com sua própria casa”.
10 Shi ya sa, saboda ku sammai sun ƙi saukar da raɓa, ƙasa kuma ta ƙi ba da amfani.
Portanto, para vosso bem, os céus retêm o orvalho, e a terra retém seus frutos.
11 Na kawo fări a ƙasar, da a kan duwatsu, da a kan hatsi, da a kan dukan abin da yake tsirowa daga ƙasa, da a kan mutane, da a kan dabbobi da kuma a kan wahalar hannuwanku.”
Eu pedi uma seca na terra, nas montanhas, nos grãos, no vinho novo, no óleo, naquilo que o solo produz, nos homens, no gado, e em todo o trabalho das mãos”.
12 Sa’an nan sai Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, wanda yake babban firist, da kuma dukan raguwar jama’ar suka yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnsu da kuma saƙon annabi Haggai, domin Ubangiji Allahnsu ne ya aiko shi. Mutane kuwa suka ji tsoron Ubangiji.
Então Zerubabel, filho de Shealtiel, e Josué, filho de Jehozadak, o sumo sacerdote, com todo o restante do povo, obedeceram a Javé sua voz de Deus, e as palavras de Ageu, o profeta, como Javé seu Deus o havia enviado; e o povo temia a Javé.
13 Sai Haggai, ɗan saƙon Ubangiji, ya ba da wannan saƙo na Ubangiji ga mutane cewa, “Ina tare da ku” in ji Ubangiji.
Então Haggai, mensageiro de Javé, falou a mensagem de Javé ao povo, dizendo: “Eu estou com você”, diz Javé.
14 Saboda haka Ubangiji ya motsa zuciyar Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, wanda yake gwamna a Yahuda, da kuma zuciyar Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma zukatan dukan raguwar jama’ar. Suka zo suka fara aiki a gidan Ubangiji Maɗaukaki, Allahnsu,
Javé despertou o espírito de Zorobabel, filho de Shealtiel, governador de Judá, e o espírito de Josué, filho de Jehozadak, sumo sacerdote, e o espírito de todo o resto do povo; e eles vieram e trabalharam na casa de Javé dos Exércitos, seu Deus,
15 a ranar ashirin da huɗu ga watan shida. A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus,
no vigésimo quarto dia do mês, no sexto mês, no segundo ano de Dario, o rei.

< Haggai 1 >