< Habakkuk 1 >

1 Saƙon da annabi Habakkuk ya karɓa.
Peygamber Habakkuk'a bir görümde verilen bildiridir.
2 Har yaushe, ya Ubangiji, zan yi kukan neman taimako, amma ka ƙi ji? Ina kuka a gare ka saboda zalunci amma ba ka ce ufam ba.
Ya RAB, ne zamana dek seni yardıma çağıracağım, Beni duymuyor musun? “Zorbalık var” diye haykırıyorum sana, Ama kurtarmıyorsun!
3 Me ya sa ka bari ina ta kallon rashin gaskiya? Me ya sa kake barin abin da ba daidai ba? Hallaka da tashin hankali suna a gabana; ga rashin jituwa da faɗa ko’ina.
Bunca kötülüğü bana neden gösteriyorsun, Nasıl hoş görürsün bunca haksızlığı? Nereye baksam şiddet ve zorbalık var. Kavgaların, çekişmelerin sonu gelmiyor.
4 Saboda haka ba a bin doka, shari’a kuma ba ta aiki. Mugaye sun kewaye masu adalci don a hana gaskiya tă yi aiki.
Bu yüzden yasa işlemez oldu, Bir türlü yerini bulmuyor hak. Kötüler doğruları kıskaca almış Ve böylece adalet saptırılıyor.
5 “Ka dubi al’ummai, ka gani, ka sha mamaki. Ga shi zan yi wani abu a kwanakinka, wanda ko ma an faɗa maka ba za ka gaskata ba.
“Bakın öbür uluslara, Gördüklerinize büsbütün şaşacaksınız. Sizin gününüzde öyle işler yapacağım ki, Anlatsalar inanmayacaksınız.
6 Zan tā da Babiloniyawa, waɗannan marasa hankali da kuma marasa tausayi; masu gajeren haƙuri, waɗanda suke ratsa ko’ina a duniya don su ƙwace wuraren zaman da ba nasu ba.
Başkalarına ait toprakları ele geçirmek için Dünyanın dört yanına yürüyen o acımasız ve saldırgan ulusu, Kildaniler'i güçlendireceğim.
7 Suna da bantsoro da firgitarwa; dokoki da ƙa’idodinsu ne kawai suka sani.
Dehşetli ve korkunçturlar, Gururlu ve başlarına buyrukturlar.
8 Dawakansu sun fi damisoshi sauri, sun fi kyarketan yamma zafin rai. Mahayansu suna zuwa a guje; mahayansu daga nesa suka fito. Suna firiya kamar ungulu mai sauka da gaggawa don yă ci mushe;
Parstan çeviktir atları, Aç kurttan daha azgın. Atlıları yeri deşerek geliyor uzaklardan, Avına saldıran kartal gibi uçuyorlar,
9 duk sukan zo da nufin tā-da-na-zaune-tsaye. Ana jin tsoronsu tun ma kafin su iso suna tattara bayi kamar yashi.
Yağmalamak için geliyor hepsi. Orduları çöl rüzgarı gibi ilerliyor Ve kum gibi tutsak topluyorlar.
10 Sukan yi wa sarakuna ba’a su kuma rena masu mulki. Sukan yi wa dukan birane masu mafaka dariya; sukan tara ƙasa su hau, su cinye abokan gābansu da yaƙi.
Küçümsüyorlar kralları, Yöneticilerle alay ediyorlar. Dudak büküyorlar bütün surlu kentlere, Önlerine toprak yığıp onları ele geçiriyorlar.
11 Sa’an nan su wuce da sauri kamar iska, mutane ne masu laifi, waɗanda ƙarfinsu shi ne allahnsu.”
Rüzgar gibi geçip gidiyorlar. Bu suçlu adamların ilahları kendi güçleridir.”
12 Ya Ubangiji, ba tun fil azal kake ba? Ya Allahna, Mai Tsarkina, ba za mu mutu ba. Ya Ubangiji ka sanya su su tabbatar da hukunci; Ya Dutse, ka naɗa su don su yi hukunci.
Ya RAB, kutsal Tanrım, Öncesizlikten beri var olan sen değil misin? Sen ölmeyeceksin. Ya RAB, bizi yargılamak için Kildaniler'i mi seçtin? Ey sığınağımız, onlara mı verdin cezalandırma yetkisini?
13 Idanunka masu tsarki ne da suka fi gaban duban mugunta; ba ka amince da abin da ke ba daidai ba. To, don me ka ƙyale munafukai suna cin karensu ba babbaka? Me ya sa kake shiru sa’ad da mugaye suke haɗiye adalai da suka fi su adalci?
Kötüye bakamayacak kadar saftır gözlerin. Haksızlığı hoş göremezsin. Öyleyse nasıl hoş görürsün Bu hain adamları? Doğrular kötülere yem olurken Neden susuyorsun?
14 Ka mai da maza kamar kifin teku, kamar halittun tekun da ba su da shugaba.
İnsanları denizdeki balıklara, Yöneticiden yoksun sürüngenlere çevirdin.
15 Mugu abokin gāba yakan kama su duka da ƙugiya, yă jawo su waje da abin kamun kifinsa, yă tattara su cikin ragarsa, ta haka yakan yi murna da farin ciki.
Kildaniler onları oltayla, ağla, Serpme ağla tutar gibi tutuyor Ve sevinç çığlıkları atıyorlar.
16 Saboda haka yakan yi hadaya wa abin kamun kifinsa yă kuma ƙona turare wa ragarsa, domin ta wurin abin kamun kifinsa ne yake yin rayuwar jin daɗi yă kuma zaɓi irin abincin da yake so.
Kurban kesiyorlar ağlarına bu yüzden. Kendilerine lezzetli ve bol yiyecek sağlayan ağları için buhur yakıyorlar.
17 Zai ci gaba da juye abin kamun kifinsu ke nan, suna hallaka al’ummai ba tausayi?
Ağlarını durmadan boşaltmaya, Ulusları acımasızca öldürmeye devam edecekler mi?

< Habakkuk 1 >