< Habakkuk 1 >

1 Saƙon da annabi Habakkuk ya karɓa.
Malheur accablant qu’a vu Habacuc, le prophète.
2 Har yaushe, ya Ubangiji, zan yi kukan neman taimako, amma ka ƙi ji? Ina kuka a gare ka saboda zalunci amma ba ka ce ufam ba.
Jusques à quand, Seigneur, crierai-je et vous ne m’exaucerez pas, jusques à quand élèverai-je ma voix avec force vers vous, souffrant violence, et vous ne me sauverez pas?
3 Me ya sa ka bari ina ta kallon rashin gaskiya? Me ya sa kake barin abin da ba daidai ba? Hallaka da tashin hankali suna a gabana; ga rashin jituwa da faɗa ko’ina.
Pourquoi m’avez-vous montré l’iniquité et la peine, pourquoi avez-vous fait voir la rapine et l’injustice devant moi? Il y a eu jugement, mais l’opposition a été plus puissante.
4 Saboda haka ba a bin doka, shari’a kuma ba ta aiki. Mugaye sun kewaye masu adalci don a hana gaskiya tă yi aiki.
À cause de cela, la loi a été déchirée, et le jugement n’est pas parvenu à l’exécution, parce que l’impie prévaut contre le juste; c’est pourquoi il sort de là une décision injuste.
5 “Ka dubi al’ummai, ka gani, ka sha mamaki. Ga shi zan yi wani abu a kwanakinka, wanda ko ma an faɗa maka ba za ka gaskata ba.
Jetez les yeux sur les nations, et voyez; admirez et soyez frappés de stupeur: parce qu’il s’est fait en vos jours une œuvre que personne ne croira lorsqu’elle sera racontée.
6 Zan tā da Babiloniyawa, waɗannan marasa hankali da kuma marasa tausayi; masu gajeren haƙuri, waɗanda suke ratsa ko’ina a duniya don su ƙwace wuraren zaman da ba nasu ba.
Car voici que moi je susciterai les Chaldéens, nation cruelle et prompte, qui parcourt l’étendue de la terre, afin de s’emparer des tabernacles qui ne sont pas à elle.
7 Suna da bantsoro da firgitarwa; dokoki da ƙa’idodinsu ne kawai suka sani.
Elle est horrible et formidable; c’est d’elle-même que le jugement et la charge sortiront.
8 Dawakansu sun fi damisoshi sauri, sun fi kyarketan yamma zafin rai. Mahayansu suna zuwa a guje; mahayansu daga nesa suka fito. Suna firiya kamar ungulu mai sauka da gaggawa don yă ci mushe;
Ses chevaux sont plus légers que les léopards, et plus vîtes que les loups du soir; et ses cavaliers se répandront; car ses cavaliers viendront de loin, ils voleront comme un aigle se hâtant pour manger.
9 duk sukan zo da nufin tā-da-na-zaune-tsaye. Ana jin tsoronsu tun ma kafin su iso suna tattara bayi kamar yashi.
Tous viendront au butin; leur face est comme un vent brûlant; et ils assembleront les captifs, comme le sable.
10 Sukan yi wa sarakuna ba’a su kuma rena masu mulki. Sukan yi wa dukan birane masu mafaka dariya; sukan tara ƙasa su hau, su cinye abokan gābansu da yaƙi.
Et lui-même triomphera des rois, et les princes seront pour lui un sujet de dérision; lui-même se moquera de toute fortification, et il formera un terrassement, et il la prendra.
11 Sa’an nan su wuce da sauri kamar iska, mutane ne masu laifi, waɗanda ƙarfinsu shi ne allahnsu.”
Alors son esprit sera changé; il passera et tombera; voilà quelle est sa puissance qu’il tient de son Dieu.
12 Ya Ubangiji, ba tun fil azal kake ba? Ya Allahna, Mai Tsarkina, ba za mu mutu ba. Ya Ubangiji ka sanya su su tabbatar da hukunci; Ya Dutse, ka naɗa su don su yi hukunci.
Est-ce que vous, vous n’êtes pas dès le commencement, Seigneur mon Dieu, mon Saint, pour que nous ne mourions pas? Seigneur, vous l’avez établi pour accomplir votre jugement et vous l’avez rendu fort, afin de le châtier.
13 Idanunka masu tsarki ne da suka fi gaban duban mugunta; ba ka amince da abin da ke ba daidai ba. To, don me ka ƙyale munafukai suna cin karensu ba babbaka? Me ya sa kake shiru sa’ad da mugaye suke haɗiye adalai da suka fi su adalci?
Vos yeux sont purs, afin de ne point voir le mal; vous ne pourrez regarder l’iniquité: pourquoi regardez-vous ceux qui font des iniquités et gardez-vous le silence, l’impie dévorant celui qui est plus juste que lui?
14 Ka mai da maza kamar kifin teku, kamar halittun tekun da ba su da shugaba.
Et vous traitez des hommes comme les poissons de la mer, et comme un reptile qui n’a pas de prince.
15 Mugu abokin gāba yakan kama su duka da ƙugiya, yă jawo su waje da abin kamun kifinsa, yă tattara su cikin ragarsa, ta haka yakan yi murna da farin ciki.
Il a tout enlevé avec un hameçon, il l’a entraîné dans sa seine, et rassemblé dans son rets. Sur cela il se réjouira, et il exultera.
16 Saboda haka yakan yi hadaya wa abin kamun kifinsa yă kuma ƙona turare wa ragarsa, domin ta wurin abin kamun kifinsa ne yake yin rayuwar jin daɗi yă kuma zaɓi irin abincin da yake so.
À cause de cela, il immolera des victimes à sa seine, et il sacrifiera à son rets, parce que par eux son partage s’est accru, et sa nourriture a été acquise.
17 Zai ci gaba da juye abin kamun kifinsu ke nan, suna hallaka al’ummai ba tausayi?
À cause de cela, donc il tend sa seine, et jamais il ne s’abstiendra de tuer des nations.

< Habakkuk 1 >