< Habakkuk 1 >
1 Saƙon da annabi Habakkuk ya karɓa.
Profetien, som Habakuk, Profeten, har skuet.
2 Har yaushe, ya Ubangiji, zan yi kukan neman taimako, amma ka ƙi ji? Ina kuka a gare ka saboda zalunci amma ba ka ce ufam ba.
Hvor længe, Herre! har jeg dog raabt, og du vil ikke høre! jeg raaber til dig over Vold, og du vil ikke frelse.
3 Me ya sa ka bari ina ta kallon rashin gaskiya? Me ya sa kake barin abin da ba daidai ba? Hallaka da tashin hankali suna a gabana; ga rashin jituwa da faɗa ko’ina.
Hvorfor lader du mig skue Uret og ser selv paa Jammer? Ødelæggelse og Vold er for mit Ansigt, og der kom Trætte, og Kiv rejser sig.
4 Saboda haka ba a bin doka, shari’a kuma ba ta aiki. Mugaye sun kewaye masu adalci don a hana gaskiya tă yi aiki.
Derfor er Lov magtesløs, og Ret kommer aldrig frem; thi de ugudelige omringe den retfærdige, derfor kommer Retten forvendt ud.
5 “Ka dubi al’ummai, ka gani, ka sha mamaki. Ga shi zan yi wani abu a kwanakinka, wanda ko ma an faɗa maka ba za ka gaskata ba.
Ser ud iblandt Hedningerne, og skuer; forundrer eder, og vorder forundrede; thi jeg gør en Gerning i eders Dage, I vilde ikke tro den, naar den fortaltes.
6 Zan tā da Babiloniyawa, waɗannan marasa hankali da kuma marasa tausayi; masu gajeren haƙuri, waɗanda suke ratsa ko’ina a duniya don su ƙwace wuraren zaman da ba nasu ba.
Thi se, jeg opvækker Kaldæerne, et barsk og hastigt Folk, som farer frem, saa vidt som Jorden naar, for at tage Boliger til Eje, som ikke høre det til.
7 Suna da bantsoro da firgitarwa; dokoki da ƙa’idodinsu ne kawai suka sani.
Frygteligt og forfærdeligt er det; fra det gaar dets Ret og Overhøjhed ud.
8 Dawakansu sun fi damisoshi sauri, sun fi kyarketan yamma zafin rai. Mahayansu suna zuwa a guje; mahayansu daga nesa suka fito. Suna firiya kamar ungulu mai sauka da gaggawa don yă ci mushe;
Og dets Heste ere lettere end Pardere og hidsigere end Ulve om Aftenen, og dets Ryttere brede sig ud, ja, dets Ryttere komme langt borte fra, de flyve som en Ørn, der haster efter Æde.
9 duk sukan zo da nufin tā-da-na-zaune-tsaye. Ana jin tsoronsu tun ma kafin su iso suna tattara bayi kamar yashi.
Alle til Hobe komme de til Voldsdaad, deres Ansigters Higen er fremad, og det samler Fanger som Sand.
10 Sukan yi wa sarakuna ba’a su kuma rena masu mulki. Sukan yi wa dukan birane masu mafaka dariya; sukan tara ƙasa su hau, su cinye abokan gābansu da yaƙi.
Og det spotter Konger, og Fyrster ere til Latter for det; det ler ad hver Befæstning, saa det dynger Støv op og indtager den.
11 Sa’an nan su wuce da sauri kamar iska, mutane ne masu laifi, waɗanda ƙarfinsu shi ne allahnsu.”
Da farer det frem som en Stormvind og drager videre, saa at det paadrager sig Skyld; denne dets Kraft bliver til dets Gud.
12 Ya Ubangiji, ba tun fil azal kake ba? Ya Allahna, Mai Tsarkina, ba za mu mutu ba. Ya Ubangiji ka sanya su su tabbatar da hukunci; Ya Dutse, ka naɗa su don su yi hukunci.
Er du ikke fra fordums Tid Herren, min Gud, min Hellige! vi skulle ikke dø; Herre! du har sat det til Dom; o Klippe! du har grundfæstet det til at straffe os.
13 Idanunka masu tsarki ne da suka fi gaban duban mugunta; ba ka amince da abin da ke ba daidai ba. To, don me ka ƙyale munafukai suna cin karensu ba babbaka? Me ya sa kake shiru sa’ad da mugaye suke haɗiye adalai da suka fi su adalci?
Du, som er ren af Øjne, saa at du ikke kan se paa ondt og ikke formaar at skue Jammer, hvorfor skuer du hen til de troløse, hvorfor tier du, naar den ugudelige opsluger den, som er retfærdigere end han?
14 Ka mai da maza kamar kifin teku, kamar halittun tekun da ba su da shugaba.
Du gjorde da Menneskene som Fiske i Havet, som Krybet, der ingen Herre har.
15 Mugu abokin gāba yakan kama su duka da ƙugiya, yă jawo su waje da abin kamun kifinsa, yă tattara su cikin ragarsa, ta haka yakan yi murna da farin ciki.
Han drager dem alle sammen op med Krog, samler dem i sin Vod og sanker dem i sit Garn; derover glæder og fryder han sig.
16 Saboda haka yakan yi hadaya wa abin kamun kifinsa yă kuma ƙona turare wa ragarsa, domin ta wurin abin kamun kifinsa ne yake yin rayuwar jin daɗi yă kuma zaɓi irin abincin da yake so.
Derfor ofrer han til sin Vod og bringer Røgoffer til sit Garn; thi ved dem er hans Del fed, og hans Mad er det fede.
17 Zai ci gaba da juye abin kamun kifinsu ke nan, suna hallaka al’ummai ba tausayi?
Mon han derfor skal tømme sin Vod og altid slaa Folk ihjel uden Skaansel?